< 2 Sarakuna 19 >

1 Da sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakketa tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya shiga haikalin Ubangiji.
Et il arriva que dès que le Roi Ezéchias eut entendu ces choses, il déchira ses vêtements, et se couvrit d'un sac, et entra dans la maison de l'Eternel.
2 Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna marubuci da shugabannin firistoci, dukansu sanye da tufafin makoki, zuwa wurin annabi Ishaya ɗan Amoz.
Puis il envoya Eliakim, Maître d'hôtel, et Sebna le Secrétaire, et les anciens d'entre les Sacrificateurs, couverts de sacs, vers Esaïe le Prophète fils d'Amots.
3 Suka ce masa, “Hezekiya ya ce, yau ranar wahala ce, da ta cin mutunci, da ta shan kunya, ga shi,’ya’ya suna gab da a haife su, amma ba ƙarfin da za a yi yunƙuri a haife su.
Et ils lui dirent: Ainsi a dit Ezéchias: Ce jour est un jour d'angoisse, et de répréhension, et de blasphème; car les enfants sont venus jusqu'à l'ouverture de la matrice, mais il n'y a point de force pour enfanter.
4 Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka ya ji dukan maganganun sarkin yaƙi, wanda maigidansa, sarkin Assuriya, ya aiko don yă rena Allah mai rai. Bari Ubangiji Allahnka yă tsawata masa saboda maganar da ya ji. Saboda haka ka yi addu’a domin raguwar da har yanzu suke a raye.”
Peut-être que l'Eternel ton Dieu aura entendu toutes les paroles de Rab-saké, que le Roi des Assyriens son Maître a envoyé pour blasphémer le Dieu vivant, et pour l'outrager par les paroles que l'Eternel ton Dieu a entendues; fais donc une prière pour le reste qui se trouve encore.
5 Da fadawan sarki Hezekiya suka isa wurin Ishaya,
Les serviteurs donc du Roi Ezéchias vinrent vers Esaïe.
6 Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku, in ji Ubangiji, ‘Kada abin da ka ji yă firgita ka, wato, waɗannan kalmomin da karen nan na sarkin Assuriya ya yi saɓo da su.
Et Esaïe leur dit, vous direz ainsi à votre Maître: Ainsi a dit l'Eternel: Ne crains point pour les paroles que tu as entendues, par lesquelles les serviteurs du Roi des Assyriens m'ont blasphémé.
7 Saurara! Zan sa masa wani ruhun da zai sa yă ji wata jita-jitar da za tă sa yă koma ƙasarsa. A can zan sa a kashe shi da takobi a ƙasarsa.’”
Voici, je m'en vais mettre en lui un tel esprit, qu'ayant entendu un certain bruit, il retournera en son pays, et je le ferai tomber par l'épée dans son pays.
8 Da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye, ya kuma iske sarkin yana yaƙi da Libna.
Or quand Rab-saké s'en fut retourné, il alla trouver le Roi des Assyriens qui battait Libna; car il avait appris qu'il était parti de Lakis.
9 To, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana zuwa masa da yaƙi. Saboda haka ya sāke aika manzanni zuwa wurin Hezekiya cewa,
Le [Roi] donc [des Assyriens] eut des nouvelles touchant Tirhaca Roi d'Ethiopie: Voilà, [lui disait-on], il est sorti pour te combattre. C'est pourquoi il s'en retourna, mais il envoya des messagers à Ezéchias, en leur disant:
10 “Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda, kada ka bar allahn da kake dogara gare shi yă ruɗe ka cewa, ‘Urushalima ba za tă fāɗi a hannun sarkin Assuriya ba.’
Vous parlerez ainsi à Ezéchias Roi de Juda, et lui direz: Que ton Dieu, en qui tu te confies, ne t'abuse point en te disant: Jérusalem ne sera point livrée entre les mains du Roi des Assyriens.
11 Ba shakka ka riga ka ji abin da sarkin Assuriya ya yi da dukan ƙasashe, yana hallaka su gaba ɗaya. Kai kuwa kana ji za a cece ka?
Voilà, tu as entendu ce que les Rois des Assyriens ont fait à tous les pays en les détruisant entièrement; et tu échapperais?
12 Allolin al’umman da kakannina suka hallaka, sun cece su ne, allolin Gozan, da na Haran, da na Rezef, da kuma na mutane Eden da suke a Tel Assar?
Les dieux des nations que mes ancêtres ont détruites, [savoir] de Gozan, de Caran, de Retseph, et des enfants d'Héden, qui sont en Thélasar, les ont-ils délivrées?
13 Ina sarkin Hamat, da sarkin Arfad, da sarkin birnin Sefarfayim, ko na Hena da kuma na Iffa?”
Où est le Roi de Hamath, le Roi d'Arpad, et le Roi de la ville de Sépharvajim, Hanath, et Hiwah?
14 Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga manzannin ya karanta. Sa’an nan ya tashi ya tafi haikalin Ubangiji ya shimfiɗa wasiƙar a gaban Ubangiji.
Et quand Ezéchias eut reçu les Lettres de la main des messagers, et les eut lues, il monta dans la maison de l'Eternel, et Ezéchias les déploya devant l'Eternel.
15 Hezekiya kuwa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda yake zaune tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah bisa dukan mulkokin duniya. Kai ka yi sama da duniya.
Puis Ezéchias fit sa prière devant l'Eternel, et dit: Ô Eternel Dieu d'Israël! qui es assis entre les Chérubins, toi seul es le Dieu de tous les Royaumes de la terre; tu as fait les cieux et la terre.
16 Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka ji; ka buɗe idanunka ya Ubangiji ka gani; ka saurari kalmomin da Sennakerib ya aiko don yă yi wa Allah mai rai ba’a.
Ô Eternel! incline ton oreille, et écoute; ouvre tes yeux, et regarde; et écoute les paroles de Sanchérib, [et] de celui qu'il a envoyé pour blasphémer le Dieu vivant.
17 “Da gaske ne, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriya sun hallakar da waɗannan al’ummai da ƙasashensu.
Il est vrai, ô Eternel! que les Rois des Assyriens ont détruit ces nations-là, et leurs pays;
18 Sun jefar da allolinsu cikin wuta, suka hallaka su, gama ba alloli ba ne, katakai ne da kuma duwatsu, ayyukan hannuwan mutane.
Et qu'ils ont jeté qu feu leurs dieux, car ce n'étaient point des dieux, mais des ouvrages de main d'homme, du bois, et de la pierre, c'est pourquoi ils les ont détruits.
19 To, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, don dukan mulkokin duniya su san cewa kai kaɗai, ya Ubangiji ne Allah.”
Maintenant donc, ô Eternel notre Dieu! je te prie, délivre-nous de la main de Sanchérib, afin que tous les Royaumes de la terre sachent que c'est toi, ô Eternel! qui es le seul Dieu.
20 Sai Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo zuwa wurin Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, na ji addu’arka game da Sennakerib sarkin Assuriya.
Alors Esaïe fils d'Amots, envoya vers Ezéchias, pour lui dire: Ainsi a dit l'Eternel le Dieu d'Israël: Je t'ai exaucé dans ce que tu m'as demandé touchant Sanchérib Roi des Assyriens.
21 Ga abin da Ubangiji yana cewa game da shi, “‘Budurwar Sihiyona ta rena ka tana kuma yin maka ba’a. Diyar Urushalima ta kaɗa kanta yayinda kake gudu.
[C'est] ici la parole que l'Eternel a prononcée contre lui. La vierge fille de Sion t'a méprisé, et s'est moquée de toi; la fille de Jérusalem a hoché la tête après toi.
22 Wane ne ka zaga, ka kuma yi masa saɓo? Wa kake gāba da shi har ka ɗaga muryarka, har ka tā da idanunka da fahariya? Kana gāba da Mai Tsarki na Isra’ila!
Qui as-tu outragé et blasphémé? contre qui as-tu élevé la voix, et levé les yeux en haut? c'est contre le Saint d'Israël.
23 Ta wurin manzanninka ka tara wa Ubangiji zagi. Ka kuma ce, “Da yawa kekunan yaƙina na haye kan ƙwanƙolin duwatsu, wurin mafi tsawo na Lebanon. Na sassare itacen al’ul nasa mafi tsawo mafi daraja na itacen fir nasa. Na ratsa har can tsakiyar kurmi, mafi kyau na kurminsa.
Tu as outragé le Seigneur par le moyen de tes messagers, et tu as dit: Avec la multitude de mes chariots je suis monté tout au haut des montagnes aux côtés du Liban; je couperai les plus hauts cèdres, et les plus beaux sapins qui y soient, et j'entrerai dans les logis qui sont à ses bouts, et dans la forêt de son Carmel.
24 Na tona rijiyoyi a ƙasashen waje na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.”
J'ai creusé des sources après avoir bu les eaux étrangères; et j'ai tari avec la plante de mes pieds tous les ruisseaux des forteresses.
25 “‘Ba ka taɓa ji ba? Tun da daɗewa na ƙaddara haka. Tuntuni kuwa na shirya shi; yanzu kuma na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu katanga tarin duwatsu.
N'as-tu pas appris qu'il y a déjà longtemps que j'ai fait cette ville, et qu'anciennement je l'ai ainsi formée? et l'aurais-je maintenant amenée au point d'être réduite en désolation, [et] les villes munies, en monceaux de ruines?
26 Ƙarfin mutanensu ya tsiyaye, suka razana aka kuma kunyata su. Suna kama da tsirai a gona, kamar sabon toho kamar ciyawa mai tohuwa bisa rufin ɗaki wanda ya bushe saboda zafi, kafin yă yi girma.
Il est vrai que leurs habitants étant sans force ont été épouvantés, et confus, et qu'ils sont devenus [comme] l'herbe des champs, [comme] l'herbe verte, [et] le foin des toits, et [comme] la moisson qui a été touchée de la brûlure, avant qu elle soit crue en épi.
27 “‘Amma na san wurin zamanka da fitarka da shigarka da yadda kake fushi da ni.
Mais je sais ta demeure, ta sortie et ton entrée, [et] comment tu es forcené contre moi.
28 Domin kana fushi da ni reninka ya iso kunnuwata, zan sa ƙugiyata a hancinka da linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma a ta hanyar da ka zo.’
Or parce que tu es forcené contre moi, et que ton insolence est montée à mes oreilles, je mettrai ma boucle en tes narines, et mon mors dans tes mâchoires, et je te ferai retourner par le chemin par lequel tu es venu.
29 “Wannan zai zama alama a gare ka, ya Hezekiya, “Bana, za ku ci amfanin gonar da ya tsira da kansa, baɗi kuma amfanin gonar da ya tsiro daga na bara. Amma a shekara ta uku, za ku yi shuki, ku kuma girbe, ku dasa gonakin inabi, ku kuma ci’ya’yansa.
Et ceci te sera pour signe, [ô Ezéchias!] c'est qu'on mangera cette année ce qui viendra de soi-même aux champs; et la seconde année, ce qui croîtra encore sans semer; mais la troisième année, vous sèmerez, et vous moissonnerez; vous planterez des vignes, et vous en mangerez le fruit.
30 Sau ɗaya kuma ragowar masarautar Yahuda za tă yi saiwoyi a ƙasa ta kuma ba da’ya’ya a bisa.
Et ce qui est réchappé et demeuré de reste dans la maison de Juda, étendra sa racine par dessous, et elle produira son fruit par dessus.
31 Gama daga Urushalima za a sami ragowa, daga Dutsen Sihiyona kuma za a sami waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki za tă cika wannan.
Car de Jérusalem sortira quelque reste, et de la montagne de Sion quelques réchappés; la jalousie de l'Eternel des armées fera cela.
32 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga birnin nan ba ko yă harba kibiya a nan. Ba zai kusace ta da garkuwa ko yă yi mata zoben yaƙi ba.
C'est pourquoi ainsi a dit l'Eternel touchant le Roi des Assyriens: Il n'entrera point dans cette ville, il n'y jettera même aucune flèche, et il ne se présentera point contr'elle avec le bouclier, et il ne dressera point de terrasse contr'elle.
33 Ta hanyar da ya zo ne zai koma; ba zai shiga birnin nan ba, in ji Ubangiji.
Il s'en retournera par le chemin par lequel il est venu, et n'entrera point dans cette ville, dit l'Eternel.
34 Zan kāre birnin nan in cece ta, saboda kaina da kuma bawana Dawuda.”
Car je garantirai cette ville, afin de la délivrer, pour l'amour de moi, et pour l'amour de David mon serviteur.
35 A daren nan mala’ikan Ubangiji ya fita ya kashe dakaru dubu ɗari da tamanin da biyu a sansanin Assuriyawa. Da mutane suka farka da safe, sai ga gawawwaki ko’ina.
Il arriva donc cette nuit-là qu'un Ange de l'Eternel sortit, et tua cent quatre-vingt et cinq mille hommes au camp des Assyriens; et quand on se fut levé de bon matin, voilà, c'étaient tous corps morts.
36 Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya tā da sansanin ya kuma janye. Ya koma Ninebe ya zauna a can.
Et Sanchérib Roi des Assyriens partit de là, et s'en alla, et s'en retourna, et se tint à Ninive.
37 Wata rana yayinda yake sujada a haikalin Nisrok, allahnsa, sai’ya’yansa maza, Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka gudu zuwa ƙasar Ararat. Sai Esar-Haddon ɗansa ya gāje shi.
Et il arriva, comme il était prosterné dans la maison de Nisroc son Dieu, qu'Adrammélec et Saréetser ses fils le tuèrent avec l'épée, puis ils se sauvèrent au pays d'Ararat; et Esarhaddon son fils régna en sa place.

< 2 Sarakuna 19 >