< 2 Sarakuna 18 >
1 A shekara ta uku ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila, Hezekiya ɗan Ahaz sarkin Yahuda ya fara mulki.
Kwasekusithi ngomnyaka wesithathu kaHosheya indodana kaEla, inkosi yakoIsrayeli, uHezekhiya indodana kaAhazi inkosi yakoJuda waba yinkosi.
2 Yana da shekara ashirin da biyar da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Abiya’yar Zakariya.
Wayeleminyaka engamatshumi amabili lanhlanu lapho esiba yinkosi; wabusa iminyaka engamatshumi amabili lesificamunwemunye eJerusalema. Lebizo likanina lalinguAbhi indodakazi kaZekhariya.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda kakansa Dawuda ya yi.
Wasesenza okulungileyo emehlweni eNkosi njengakho konke uDavida uyise akwenzayo.
4 Ya kawar da masujadan kan tudu, ya farfasa keɓaɓɓun duwatsu, ya sassare ginshiƙan Ashera. Ya fashe macijin tagullan da Musa ya yi, gama har zuwa lokacin nan Isra’ilawa suna ƙona turare gare shi. (An ba shi suna Nehushtan.)
Yena wasusa indawo eziphakemeyo, wabhidliza insika eziyizithombe, wagamula izixuku, wachoboza inyoka yethusi uMozisi ayeyenzile, ngoba kuze kube yilezonsuku abantwana bakoIsrayeli babeyitshisela impepha; wayibiza ngokuthi nguNehushitani.
5 Hezekiya ya dogara ga Ubangiji, Allah na Isra’ila. Ba a yi wani kamar sa ba cikin dukan sarakunan Yahuda; ko kafin shi, ko kuma bayansa.
Wathembela eNkosini, uNkulunkulu kaIsrayeli; okwathi emva kwakhe kakubanga khona onjengaye emakhosini wonke akoJuda, loba ayengaphambi kwakhe.
6 Ya manne wa Ubangiji, bai fasa binsa ba; ya yi biyayya da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa.
Ngoba wanamathela eNkosini, kaphambukanga ekuyilandeleni, kodwa wagcina imilayo yayo iNkosi eyayilaya uMozisi.
7 Ubangiji kuma ya kasance tare da shi, ya yi nasara a duk abin da ya sa hannu. Ya yi tawaye ga sarkin Assuriya, ya ƙi yă bauta masa.
LeNkosi yaba laye; loba ngaphi lapho aphumela khona waphumelela. Wavukela inkosi yeAsiriya, kayisebenzelanga.
8 Daga hasumiya zuwa birni mai katanga, ya ci Filistiyawa da yaƙi, har zuwa Gaza da kewaye.
Yena watshaya amaFilisti waze wafika eGaza lemingcele yayo, kusukela emphotshongweni wabalindi kuze kube semzini obiyelweyo.
9 A shekara ta huɗu ta Hezekiya, wato, shekara ta bakwai ke nan ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila; Shalmaneser Sarkin Assuriya ya tasam ma Samariya da yaƙi; ya kewaye ta.
Kwasekusithi ngomnyaka wesine wenkosi uHezekhiya, owawungumnyaka wesikhombisa kaHosheya indodana kaEla, inkosi yakoIsrayeli, uShalimaneseri inkosi yeAsiriya wenyuka wamelana leSamariya, wayivimbezela.
10 A ƙarshen shekara ta uku, Assuriyawa suka ci Samariya da yaƙi. An ci Samariya da yaƙi a shekara ta shida ta mulki Hezekiya, wanda ya zo daidai da shekara ta tara ta mulkin Hosheya sarkin Isra’ila.
Basebeyithumba ekupheleni kweminyaka emithathu. Ngomnyaka wesithupha kaHezekhiya, owawungumnyaka wesificamunwemunye kaHosheya inkosi yakoIsrayeli, iSamariya yathunjwa.
11 Sarkin Assuriya ya kwashe Isra’ila zuwa Assuriya ya zaunar da su a Hala, da Gozan a kogin Habor da kuma garuruwan Medes.
Inkosi yeAsiriya yathumbela uIsrayeli eAsiriya, yababeka eHala leHabori umfula weGozani, lemizini yamaMede.
12 Wannan ya faru ne domin ba su yi biyayya ga Ubangiji Allahnsu ba, amma suka karya alkawarinsu; da dukan abin da Musa bawan Ubangiji ya umarta. Ba su saurari umarnin ba, balle su kiyaye su.
Ngoba bengalilalelanga ilizwi leNkosi uNkulunkulu wabo, kodwa baseqa isivumelwano sayo, konke uMozisi inceku yeNkosi eyayikulayile; kabalalelanga, kabenzanga.
13 A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin sarkin Hezekiya, sai sarki Sennakerib sarkin Assuriya ya kai farmaki wa biranen Yahuda masu katanga ya kuma kama su.
Langomnyaka wetshumi lane wenkosi uHezekhiya, uSenakheribi inkosi yeAsiriya wenyuka wamelana layo yonke imizi yakoJuda ebiyelweyo, wayithumba.
14 Sai Hezekiya sarkin Yahuda ya aika saƙo ga sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka janye daga gare ni, zan kuma biya ka duk abin da ake bukata daga gare ni.” Sarkin Assuriya ya karɓi talenti ɗari uku na azurfa, da talenti talatin na zinariya daga hannun Hezekiya sarkin Yahuda.
UHezekhiya inkosi yakoJuda wasethumela enkosini yeAsiriya eLakishi esithi: Ngonile; buyela usuke kimi; okubeka phezu kwami ngizakuthwala. Inkosi yeAsiriya yasibeka phezu kukaHezekhiya inkosi yakoJuda amathalenta esiliva angamakhulu amathathu, lamathalenta angamatshumi amathathu egolide.
15 Ya zama kuwa cewa, Hezekiya ya bayar da dukan azurfan da suke a haikalin Ubangiji da kuma a ma’ajin fadan sarki.
UHezekhiya wasemnika sonke isiliva esatholakala endlini kaJehova lenothweni yendlu yenkosi.
16 A wannan lokaci ne Hezekiya sarkin Yahuda ya ɓaɓɓalle zinariyan da aka dalaye ƙofofi da madogaran ƙofofin haikalin Ubangiji, ya ba sarkin Assuriya.
Ngalesosikhathi uHezekhiya waquma igolide ezivalweni zethempeli leNkosi, lemigubazini uHezekhiya inkosi yakoJuda ayekunamathisele, walinika inkosi yeAsiriya.
17 Sai sarkin Assuriya ya aika da babban shugaban sojojinsa, da shugaban dattawansa, da wakilinsa daga birnin Lakish tare da ƙungiyar sojoji masu yawa zuwa Urushalima domin su yaƙi Sarki Hezekiya. Da suka haura sai suka tsaya a wurin lambatun da yake kawo ruwa daga Tafkin Tudu, kusa da hanyar Filin Mai Wanki.
Inkosi yeAsiriya yasithuma uTharithani loRabi-Sarisi loRabi-Shake besuka eLakishi besiya enkosini uHezekhiya belebutho elinzima eJerusalema. Benyuka-ke bafika eJerusalema. Sebenyuke bafika bema emgelweni wechibi eliphezulu, elisemgwaqweni omkhulu wensimu yomwatshi.
18 Suka kira sarki, sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka je wurinsu.
Sebebize inkosi, kwaphumela kibo uEliyakhimi indodana kaHilikhiya owayengumphathi wendlu, loShebina umbhali, loJowa indodana kaAsafi umabhalane.
19 Jagoran dogarawan sarkin Assuriya ya ce musu, “Ku ce wa Hezekiya, “‘Ga abin da babban sarkin Assuriya ya ce, da wa kake taƙama?
URabi-Shake wasesithi kibo: Khulumani khathesi kuHezekhiya: Itsho njalo inkosi enkulu, inkosi yeAsiriya ithi: Yisibindi bani lesi, othembela kuso?
20 Ka ce kana da dabara da ƙarfin soji, amma bagu kawai kake yi. Da wa ka dogara har da za ka yi mini tawaye?
Uthi, kodwa yilizwi lendebe nje: Kulecebo lamandla empi. Usuthembe bani ukuthi ungivukele?
21 Na sani kana dogara da Masar, wadda take kamar karar masara, wadda in ka jingina a kai, za tă karye tă soki hannunka. Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga dukan wanda ya dogara da shi.
Khangela-ke, wena uthembele odondolweni lomhlanga owephukileyo, oluyiGibhithe, uba umuntu eseyama phezu kwalo, luzangena esandleni sakhe lusihlabe. Unjalo uFaro inkosi yeGibhithe kubo bonke abathembela kuye.
22 Sai ya ci gaba da cewa, in kuma ka ce mini “Muna dogara ga Ubangiji Allahnmu ne,” ba masujadansa da bagadansa ne Hezekiya ya ciccire, yana ce wa Urushalima da Yahuda, “Dole ku yi sujada a gaban wannan bagade a Urushalima”?
Kodwa uba lisithi kimi: ENkosini uNkulunkulu wethu siyathemba; angithi yiyo elezindawo zayo eziphakemeyo lamalathi ayo uHezekhiya awasusileyo, wathi kuJuda leJerusalema: Phambi kwalelilathi lizakhonza eJerusalema?
23 “‘Yanzu, ka zo ku shirya da shugabana, sarkin Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sami mahayansu!
Ngakho-ke, akunike isibambiso enkosini yami, inkosi yeAsiriya, njalo ngizakunika amabhiza azinkulungwane ezimbili, uba wena ulakho ukunika abagadi bawo.
24 Yaya za ka yi tsayayya da mafi ƙanƙantan hafsan shugabana, ko da kana dogara da Masar don kekunan yaƙi da mahaya dawakai?
Pho, uzabuyisela emuva njani ubuso benduna eyodwa yabancinyane nje benceku zenkosi yami; wena-ke uthembele eGibhithe ngezinqola labagadi bamabhiza?
25 Ban da haka ma, kana gani cewa na zo in hallaka wannan wuri ne ba tare da na ji daga Ubangiji ba? Ubangiji da kansa ne ya ce da ni in kawo wa wannan ƙasa hari in hallaka ta.’”
Kambe ngenyukile yini ukumelana lalindawo ngingelaJehova ukuyichitha? UJehova uthe kimi: Yenyuka umelane lalelilizwe, ulichithe.
26 Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce wa jagoran dakarun, “Muna roƙonka ka yi wa bayinka magana da harshen Arameyik da yake muna ji. Kada ka yi mana magana da Yahudanci domin kada mutanen da suke bisa katanga su ji!”
UEliyakhimi indodana kaHilikhiya loShebina loJowa basebesithi kuRabi-Shake: Akukhulume lenceku zakho ngesiSiriya, ngoba siyasizwa; ungakhulumi lathi ngesiJuda endlebeni zabantu abasemdulini.
27 Amma shugaban sojojin ya ce, “Ai, ba gare ku da sarkinku kaɗai ne shugabana ya aike ni ba. Amma har ga mutanen da suke zaune a kan katangar birnin, waɗanda za su ci kashinsu, su sha fitsarinsu!”
Kodwa uRabi-Shake wathi kubo: Inkosi yami ingithumile yini enkosini yakho lakuwe ukukhuluma lamazwi? Kakusebantwini yini abahlezi phezu komduli ukuze badle ubulongwe babo, banathe umchamo wabo kanye lani?
28 Sai shugaban sojojin ya yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji muryar babban sarki, sarkin Assuriya!
URabi-Shake wasesima wamemeza ngelizwi elikhulu ngesiJuda, wakhuluma esithi: Zwanini ilizwi lenkosi enkulu, inkosi yeAsiriya.
29 Ga abin da sarki ya faɗa; kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku. Ba zai iya cetonku daga hannuna ba.
Itsho njalo inkosi: UHezekhiya kangalikhohlisi, ngoba kayikuba lakho ukulikhulula esandleni sayo.
30 Kada ku yarda Hezekiya yă rinjaye ku cewa ku dogara ga Allah, sa’ad da ya ce da ku, ‘Ba shakka Ubangiji zai cece mu; yana ce da ku birnin nan ba zai faɗa a hannun sarkin Assuriya ba.’
Njalo uHezekhiya angalenzi lithembele eNkosini esithi: INkosi izasikhulula lokusikhulula, lalumuzi kawuyikunikelwa esandleni senkosi yeAsiriya.
31 “Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya ce, ku shirya zaman lafiya da ni, ku fito zuwa wurina. Kowane ɗayanku kuwa zai ci’ya’yan inabinsa da’ya’yan ɓaurensa, yă kuma sha ruwa daga randarsa,
Lingamlaleli uHezekhiya, ngoba itsho njalo inkosi yeAsiriya: Yenzani isivumelwano sokuthula lami, liphume lize kimi; dlanini-ke, ngulowo lalowo okwevini lakhe langulowo lalowo okomkhiwa wakhe, linathe, ngulowo lalowo amanzi omthombo wakhe;
32 har lokacin da zan zo in kwashe ku, in kai ku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasa mai yalwar hatsi, da ruwan inabi, da abinci, da gonakin inabi, da itatuwan zaitun, da zuma, don ku rayu, kada ku mutu! “Kada ku saurari Hezekiya, don karya yake muku, sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’
ngize ngifike ngilithathe ngilise elizweni elifanana lelizwe lakini, ilizwe lamabele lewayini elitsha, ilizwe lesinkwa lezivini, ilizwe lamafutha emihlwathi loluju, ukuze liphile lingafi. Lingamlaleli uHezekhiya ngoba eliyenga esithi: INkosi izasikhulula.
33 Akwai allahn wata al’ummar da ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
Onkulunkulu bezizwe sebake bawakhulula yini ngulowo lalowo ilizwe lakhe esandleni senkosi yeAsiriya?
34 Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim, da na Hena, da na Iffa? Sun cece Samariya daga hannuna?
Bangaphi onkulunkulu beHamathi leArpadi? Bangaphi onkulunkulu beSefavayimi, beHena, leIva? Kambe bayikhulule yini iSamariya esandleni sami?
35 Wanne a cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa da gare ni? Shugaban sojojin ya kuma ci gaba da cewa, ta yaya Ubangiji zai ceci Urushalima daga hannuna?”
Ngobani kubo bonke onkulunkulu balawomazwe abakhulule ilizwe labo esandleni sami, ukuthi iNkosi ikhulule iJerusalema esandleni sami?
36 Amma mutane suka yi shiru ba su amsa masa ba, domin sarki ya umarta cewa, “Kada ku amsa masa.”
Kodwa abantu bathula, kabaze bamphendula lalizwi, ngoba umlayo wenkosi wawuyikuthi: Lingamphenduli.
37 Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf, marubuci, suka je wurin Hezekiya da tufafinsu a kece, suka faɗa masa abin da shugaban sojojin ya faɗa.
UEliyakhimi indodana kaHilikhiya owayengumphathi wendlu, loShebina umbhali, loJowa indodana kaAsafi umabhalane, basebesiza kuHezekhiya izigqoko zidatshuliwe, bamtshela amazwi kaRabi-Shake.