< 2 Sarakuna 18 >
1 A shekara ta uku ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila, Hezekiya ɗan Ahaz sarkin Yahuda ya fara mulki.
And it comes to pass, in the third year of Hoshea son of Elah, king of Israel, Hezekiah son of Ahaz, king of Judah, has reigned;
2 Yana da shekara ashirin da biyar da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Abiya’yar Zakariya.
he was a son of twenty-five years in his reigning, and he has reigned twenty-nine years in Jerusalem, and the name of his mother [is] Abi daughter of Zechariah.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda kakansa Dawuda ya yi.
And he does that which [is] right in the eyes of YHWH, according to all that his father David did,
4 Ya kawar da masujadan kan tudu, ya farfasa keɓaɓɓun duwatsu, ya sassare ginshiƙan Ashera. Ya fashe macijin tagullan da Musa ya yi, gama har zuwa lokacin nan Isra’ilawa suna ƙona turare gare shi. (An ba shi suna Nehushtan.)
he has turned aside the high places, and broken in pieces the standing-pillars, and cut down the Asherah, and beaten down the bronze serpent that Moses made, for up to these days the sons of Israel were making incense to it, and he calls it “a piece of bronze.”
5 Hezekiya ya dogara ga Ubangiji, Allah na Isra’ila. Ba a yi wani kamar sa ba cikin dukan sarakunan Yahuda; ko kafin shi, ko kuma bayansa.
In YHWH, God of Israel, he has trusted, and after him there has not been like him among all the kings of Judah, nor [among any] who were before him;
6 Ya manne wa Ubangiji, bai fasa binsa ba; ya yi biyayya da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa.
and he cleaves to YHWH, he has not turned aside from after Him, and keeps His commands that YHWH commanded Moses.
7 Ubangiji kuma ya kasance tare da shi, ya yi nasara a duk abin da ya sa hannu. Ya yi tawaye ga sarkin Assuriya, ya ƙi yă bauta masa.
And YHWH has been with him; in every place where he goes out he acts wisely, and he rebels against the king of Asshur, and has not served him;
8 Daga hasumiya zuwa birni mai katanga, ya ci Filistiyawa da yaƙi, har zuwa Gaza da kewaye.
he has struck the Philistines, even to Gaza and its borders, from a tower of watchers to the fortified city.
9 A shekara ta huɗu ta Hezekiya, wato, shekara ta bakwai ke nan ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila; Shalmaneser Sarkin Assuriya ya tasam ma Samariya da yaƙi; ya kewaye ta.
And it comes to pass, in the fourth year of King Hezekiah—it [is] the seventh year of Hoshea son of Elah, king of Israel—Shalmaneser king of Asshur has come up against Samaria and lays siege to it,
10 A ƙarshen shekara ta uku, Assuriyawa suka ci Samariya da yaƙi. An ci Samariya da yaƙi a shekara ta shida ta mulki Hezekiya, wanda ya zo daidai da shekara ta tara ta mulkin Hosheya sarkin Isra’ila.
and they capture it at the end of three years; in the sixth year of Hezekiah—it [is] the ninth year of Hoshea king of Israel—Samaria has been captured,
11 Sarkin Assuriya ya kwashe Isra’ila zuwa Assuriya ya zaunar da su a Hala, da Gozan a kogin Habor da kuma garuruwan Medes.
and the king of Asshur removes Israel to Asshur, and placed them in Halah, and in Habor [by] the river Gozan, and [in] cities of the Medes,
12 Wannan ya faru ne domin ba su yi biyayya ga Ubangiji Allahnsu ba, amma suka karya alkawarinsu; da dukan abin da Musa bawan Ubangiji ya umarta. Ba su saurari umarnin ba, balle su kiyaye su.
because that they have not listened to the voice of their God YHWH, and transgress His covenant—all that He commanded Moses, servant of YHWH—indeed, they have not listened nor done [it].
13 A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin sarkin Hezekiya, sai sarki Sennakerib sarkin Assuriya ya kai farmaki wa biranen Yahuda masu katanga ya kuma kama su.
And in the fourteenth year of King Hezekiah, Sennacherib king of Asshur has come up against all the fortified cities of Judah, and seizes them,
14 Sai Hezekiya sarkin Yahuda ya aika saƙo ga sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka janye daga gare ni, zan kuma biya ka duk abin da ake bukata daga gare ni.” Sarkin Assuriya ya karɓi talenti ɗari uku na azurfa, da talenti talatin na zinariya daga hannun Hezekiya sarkin Yahuda.
and Hezekiah king of Judah sends to the king of Asshur at Lachish, saying, “I have sinned, turn back from off me; that which you put on me I bear”; and the king of Asshur lays on Hezekiah king of Judah three hundred talents of silver and thirty talents of gold,
15 Ya zama kuwa cewa, Hezekiya ya bayar da dukan azurfan da suke a haikalin Ubangiji da kuma a ma’ajin fadan sarki.
and Hezekiah gives all the silver that is found in the house of YHWH and in the treasures of the house of the king;
16 A wannan lokaci ne Hezekiya sarkin Yahuda ya ɓaɓɓalle zinariyan da aka dalaye ƙofofi da madogaran ƙofofin haikalin Ubangiji, ya ba sarkin Assuriya.
at that time Hezekiah has cut off the doors of the temple of YHWH, and the pillars that Hezekiah king of Judah had overlaid, and gives them to the king of Asshur.
17 Sai sarkin Assuriya ya aika da babban shugaban sojojinsa, da shugaban dattawansa, da wakilinsa daga birnin Lakish tare da ƙungiyar sojoji masu yawa zuwa Urushalima domin su yaƙi Sarki Hezekiya. Da suka haura sai suka tsaya a wurin lambatun da yake kawo ruwa daga Tafkin Tudu, kusa da hanyar Filin Mai Wanki.
And the king of Asshur sends Tartan, and the chief of the eunuchs, and the chief of the butlers, from Lachish, to King Hezekiah, with a heavy force, to Jerusalem, and they go up and come to Jerusalem, and they go up, and come in and stand by the conduit of the upper pool that [is] in the highway of the fuller’s field.
18 Suka kira sarki, sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka je wurinsu.
And they call to the king, and Eliakim son of Hilkiah, who [is] over the house, and Shebna the scribe, and Joah son of Asaph, the remembrancer, go out to them.
19 Jagoran dogarawan sarkin Assuriya ya ce musu, “Ku ce wa Hezekiya, “‘Ga abin da babban sarkin Assuriya ya ce, da wa kake taƙama?
And the chief of the butlers says to them, “Now say to Hezekiah, Thus said the great king, the king of Asshur: What [is] this confidence in which you have confided?
20 Ka ce kana da dabara da ƙarfin soji, amma bagu kawai kake yi. Da wa ka dogara har da za ka yi mini tawaye?
You have said: Only a word of the lips! Counsel and might [are] for battle; now, on whom have you trusted that you have rebelled against me?
21 Na sani kana dogara da Masar, wadda take kamar karar masara, wadda in ka jingina a kai, za tă karye tă soki hannunka. Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga dukan wanda ya dogara da shi.
Now behold, you have trusted for yourself on the staff of this broken reed, on Egypt; which a man leans on, and it has gone into his hand and pierced it! So [is] Pharaoh king of Egypt to all those trusting on him.
22 Sai ya ci gaba da cewa, in kuma ka ce mini “Muna dogara ga Ubangiji Allahnmu ne,” ba masujadansa da bagadansa ne Hezekiya ya ciccire, yana ce wa Urushalima da Yahuda, “Dole ku yi sujada a gaban wannan bagade a Urushalima”?
And when you say to me, We have trusted in our God YHWH, is it not He whose high places and whose altars Hezekiah has turned aside, and says to Judah and to Jerusalem, You bow yourselves before this altar in Jerusalem?
23 “‘Yanzu, ka zo ku shirya da shugabana, sarkin Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sami mahayansu!
And now, please give a pledge for yourself to my lord the king of Asshur, and I give two thousand horses to you, if you are able to give riders for yourself on them.
24 Yaya za ka yi tsayayya da mafi ƙanƙantan hafsan shugabana, ko da kana dogara da Masar don kekunan yaƙi da mahaya dawakai?
And how do you turn back the face of one captain of the least of the servants of my lord, that you trust for yourself on Egypt for chariot and for horsemen?
25 Ban da haka ma, kana gani cewa na zo in hallaka wannan wuri ne ba tare da na ji daga Ubangiji ba? Ubangiji da kansa ne ya ce da ni in kawo wa wannan ƙasa hari in hallaka ta.’”
Have I now come up without YHWH against this place to destroy it? YHWH said to me, Go up against this land, and you have destroyed it.”
26 Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce wa jagoran dakarun, “Muna roƙonka ka yi wa bayinka magana da harshen Arameyik da yake muna ji. Kada ka yi mana magana da Yahudanci domin kada mutanen da suke bisa katanga su ji!”
And Eliakim son of Hilkiah says—and Shebna and Joah—to the chief of the butlers, “Please speak to your servants [in] Aramaic, for we are understanding, but do not speak with us [in] Jewish, in the ears of the people who [are] on the wall.”
27 Amma shugaban sojojin ya ce, “Ai, ba gare ku da sarkinku kaɗai ne shugabana ya aike ni ba. Amma har ga mutanen da suke zaune a kan katangar birnin, waɗanda za su ci kashinsu, su sha fitsarinsu!”
And the chief of the butlers says to them, “For your lord, and to you, has my lord sent me to speak these words? Is it not for the men—those sitting on the wall—to eat their own dung and to drink their own water, with you?”
28 Sai shugaban sojojin ya yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji muryar babban sarki, sarkin Assuriya!
And the chief of the butlers stands and calls with a great voice [in] Jewish, and speaks and says, “Hear a word of the great king, the king of Asshur—
29 Ga abin da sarki ya faɗa; kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku. Ba zai iya cetonku daga hannuna ba.
thus said the king: Do not let Hezekiah lift you up, for he is not able to deliver you out of his hand;
30 Kada ku yarda Hezekiya yă rinjaye ku cewa ku dogara ga Allah, sa’ad da ya ce da ku, ‘Ba shakka Ubangiji zai cece mu; yana ce da ku birnin nan ba zai faɗa a hannun sarkin Assuriya ba.’
and do not let Hezekiah make you trust in YHWH, saying, YHWH certainly delivers us, and this city is not given into the hand of the king of Asshur.
31 “Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya ce, ku shirya zaman lafiya da ni, ku fito zuwa wurina. Kowane ɗayanku kuwa zai ci’ya’yan inabinsa da’ya’yan ɓaurensa, yă kuma sha ruwa daga randarsa,
Do not listen to Hezekiah, for thus said the king of Asshur: Make a blessing with me, and come out to me, and each eat of his vine, and each [eat] of his fig tree, and each drink the waters of his own well,
32 har lokacin da zan zo in kwashe ku, in kai ku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasa mai yalwar hatsi, da ruwan inabi, da abinci, da gonakin inabi, da itatuwan zaitun, da zuma, don ku rayu, kada ku mutu! “Kada ku saurari Hezekiya, don karya yake muku, sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’
until my coming in, and I have taken you to a land like your own land, a land of grain and new wine, a land of bread and vineyards, a land of olive oil, and honey; and live, and do not die; and do not listen to Hezekiah when he persuades you, saying, YHWH delivers us.
33 Akwai allahn wata al’ummar da ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
Have each of the gods of the nations ever delivered his land out of the hand of the king of Asshur?
34 Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim, da na Hena, da na Iffa? Sun cece Samariya daga hannuna?
Where [are] the gods of Hamath and Arpad? Where [are] the gods of Sepharvaim, Hena, and Ivvah, that they have delivered Samaria out of my hand?
35 Wanne a cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa da gare ni? Shugaban sojojin ya kuma ci gaba da cewa, ta yaya Ubangiji zai ceci Urushalima daga hannuna?”
Who [are they] among all the gods of the lands that have delivered their land out of my hand, that YHWH delivers Jerusalem out of my hand?”
36 Amma mutane suka yi shiru ba su amsa masa ba, domin sarki ya umarta cewa, “Kada ku amsa masa.”
And the people have kept silent, and have not answered him a word, for the command of the king is, saying, “Do not answer him.”
37 Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf, marubuci, suka je wurin Hezekiya da tufafinsu a kece, suka faɗa masa abin da shugaban sojojin ya faɗa.
And Eliakim son of Hilkiah, who [is] over the house, comes in, and Shebna the scribe, and Joah son of Asaph, the remembrancer, to Hezekiah, with torn garments, and they declare to him the words of the chief of the butlers.