< 2 Sarakuna 18 >
1 A shekara ta uku ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila, Hezekiya ɗan Ahaz sarkin Yahuda ya fara mulki.
Israel manghai Elah capa, Hosea kah a kum thum dongah Judah manghai Ahaz capa Hezekiah khaw manghai van.
2 Yana da shekara ashirin da biyar da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Abiya’yar Zakariya.
Anih te kum kul kum nga a lo ca vaengah manghai tih Jerusalem ah kum kul kum ko manghai. A manu ming tah Zekhariah canu Abi ni.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda kakansa Dawuda ya yi.
A cungkuem dongah a napa David kah a saii bangla BOEIPA mikhmuh ah a thuem ni a. saii.
4 Ya kawar da masujadan kan tudu, ya farfasa keɓaɓɓun duwatsu, ya sassare ginshiƙan Ashera. Ya fashe macijin tagullan da Musa ya yi, gama har zuwa lokacin nan Isra’ilawa suna ƙona turare gare shi. (An ba shi suna Nehushtan.)
Anih tah hmuensang te a khoe tih kaam te khaw a phaek. Asherah te a top tih Moses loh a saii rhohum rhul te a phop. Te tue ah aka om Israel ca rhoek loh a taengah hmueih a phum uh dongah te te Nehushtan la a khue.
5 Hezekiya ya dogara ga Ubangiji, Allah na Isra’ila. Ba a yi wani kamar sa ba cikin dukan sarakunan Yahuda; ko kafin shi, ko kuma bayansa.
Israel Pathen BOEIPA dongah pangtung tih anih hnukah Judah manghai boeih khuiah khaw anih bang a om moenih. Anih hmai ah khaw a om moenih.
6 Ya manne wa Ubangiji, bai fasa binsa ba; ya yi biyayya da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa.
BOEIPA taengah balak tih a hnuk lamloh nong pawh. BOEIPA loh Moses taengah a uen vanbangla a olpaek te a tuem.
7 Ubangiji kuma ya kasance tare da shi, ya yi nasara a duk abin da ya sa hannu. Ya yi tawaye ga sarkin Assuriya, ya ƙi yă bauta masa.
BOEIPA te a taengah a om pah vanbangla a cungkuem ah a thoeng pah tih a cangbam. Te dongah Assyria manghai te a tloelh tih anih taengah thotat pawh.
8 Daga hasumiya zuwa birni mai katanga, ya ci Filistiyawa da yaƙi, har zuwa Gaza da kewaye.
Anih loh Philisti te Gaza neh a khorhi hil, rhalrhing kah rhaltoengim lamloh hmuencak khopuei hil a ngawn.
9 A shekara ta huɗu ta Hezekiya, wato, shekara ta bakwai ke nan ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila; Shalmaneser Sarkin Assuriya ya tasam ma Samariya da yaƙi; ya kewaye ta.
Manghai Hezekiah kah a kum li dong neh Israel manghai Elah capa Hosea kah a kum rhih dongah tah Assyria manghai Shalmaneser loh Samaria a paan tih a dum.
10 A ƙarshen shekara ta uku, Assuriyawa suka ci Samariya da yaƙi. An ci Samariya da yaƙi a shekara ta shida ta mulki Hezekiya, wanda ya zo daidai da shekara ta tara ta mulkin Hosheya sarkin Isra’ila.
Tedae kum thum a thok vaengah khopuei te a loh. Te dongah Hezekiah kah a kum rhuk neh Israel manghai Hosea kah a kum ko dongah Samaria te a loh.
11 Sarkin Assuriya ya kwashe Isra’ila zuwa Assuriya ya zaunar da su a Hala, da Gozan a kogin Habor da kuma garuruwan Medes.
Assyria manghai loh Israel te Assyria la a poelyoe tih amih te Halah neh Habor kah Gozan tuiva, Madai khopuei la a mawt.
12 Wannan ya faru ne domin ba su yi biyayya ga Ubangiji Allahnsu ba, amma suka karya alkawarinsu; da dukan abin da Musa bawan Ubangiji ya umarta. Ba su saurari umarnin ba, balle su kiyaye su.
A Pathen BOEIPA ol te ngai uh pawt tih a paipi te a poe uh. A cungkuem te BOEIPA kah sal Moses loh a uen coeng dae ngai uh pawt tih vai uh pawh.
13 A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin sarkin Hezekiya, sai sarki Sennakerib sarkin Assuriya ya kai farmaki wa biranen Yahuda masu katanga ya kuma kama su.
Manghai Hezekiah kah kum hlai li dongah tah Assyria manghai Sennacherib loh Judah kah vong cak khopuei boeih te a paan tih a loh pah.
14 Sai Hezekiya sarkin Yahuda ya aika saƙo ga sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka janye daga gare ni, zan kuma biya ka duk abin da ake bukata daga gare ni.” Sarkin Assuriya ya karɓi talenti ɗari uku na azurfa, da talenti talatin na zinariya daga hannun Hezekiya sarkin Yahuda.
Te dongah Judah manghai Hezekiah loh Assyria manghai te Lakhish la a tah tih, “Ka tholh coeng, kai taeng lamloh mael lamtah kai soah na tloeng te ka phueih mai bitni,” a ti nah. Te dongah Assyria manghai loh Judah manghai Hezekiah lamkah cak talent ya thum neh sui talent sawmthum a phai sak.
15 Ya zama kuwa cewa, Hezekiya ya bayar da dukan azurfan da suke a haikalin Ubangiji da kuma a ma’ajin fadan sarki.
Hezekiah loh BOEIPA im neh manghai im thakvoh khuikah a hmuh cak boeih te a phai.
16 A wannan lokaci ne Hezekiya sarkin Yahuda ya ɓaɓɓalle zinariyan da aka dalaye ƙofofi da madogaran ƙofofin haikalin Ubangiji, ya ba sarkin Assuriya.
Te vaeng tue ah Hezekiah loh BOEIPA bawkim kah thohkhaih te a khong coeng. Rhungsut a ben te khaw Judah manghai Hezekiah loh Assyria manghai taengah a phai.
17 Sai sarkin Assuriya ya aika da babban shugaban sojojinsa, da shugaban dattawansa, da wakilinsa daga birnin Lakish tare da ƙungiyar sojoji masu yawa zuwa Urushalima domin su yaƙi Sarki Hezekiya. Da suka haura sai suka tsaya a wurin lambatun da yake kawo ruwa daga Tafkin Tudu, kusa da hanyar Filin Mai Wanki.
Te dongah Assyria manghai loh rhalboei neh Rabsaris khaw, Lakhish lamkah Rabshakeh khaw, Hezekiah manghai neh Jerusalem miping caem taengla a tueih. Cet uh tih Jerusalem a pha uh neh hno suk lo long ah yoeng uh tih a so tuibuem kah tuilong te a pha uh vaengah pai uh.
18 Suka kira sarki, sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka je wurinsu.
Manghai te a khue uh vaengah amih taengla im aka tawt Hilkiah capa Eliakim neh cadaek Shebna, cabu aka khoem Asaph capa Joah te cet.
19 Jagoran dogarawan sarkin Assuriya ya ce musu, “Ku ce wa Hezekiya, “‘Ga abin da babban sarkin Assuriya ya ce, da wa kake taƙama?
Te vaengah Rabshakeh loh amih te, “Hezekiah taengah thui uh laeh, manghai boei Assyria manghai loh he ni a. thui. Mebang pangtungnah nim na pangtung van he.
20 Ka ce kana da dabara da ƙarfin soji, amma bagu kawai kake yi. Da wa ka dogara har da za ka yi mini tawaye?
Hmuilai dongah ol kak nen tah caemtloek kah cilsuep neh thayung thamal na thui. Kai nan tloelh ham khaw u dongah nim na pangtung van coeng.
21 Na sani kana dogara da Masar, wadda take kamar karar masara, wadda in ka jingina a kai, za tă karye tă soki hannunka. Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga dukan wanda ya dogara da shi.
Capu conghol aka paep dongah na pangtung coeng te. Egypt dongah aka hangdang hlang tah a kut ah rhu vetih a toeh pah ni. Egypt manghai Pharaoh soah aka pangtung boeih khaw amah te tlam ni a om eh.
22 Sai ya ci gaba da cewa, in kuma ka ce mini “Muna dogara ga Ubangiji Allahnmu ne,” ba masujadansa da bagadansa ne Hezekiya ya ciccire, yana ce wa Urushalima da Yahuda, “Dole ku yi sujada a gaban wannan bagade a Urushalima”?
Kai taengah, “Ka Pathen BOEIPA taengah ka pangtung uh,’ na ti uh khaming. Anih loh Hezekiah neh a hmuensang te khaw, a hmueihtuk te khaw a khoe moenih a? Te vaengah Judah taeng neh Jerusalem taengah, 'Jerusalem kah hmueihtuk hmai ah he thothueng uh,’ a ti nah ta.
23 “‘Yanzu, ka zo ku shirya da shugabana, sarkin Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sami mahayansu!
Tahae ah ka boeipa Assyria manghai neh rhikhang laeh. A soah aka ngol nan paek thai atah nang te marhang thawng hnih he kam pae eh.
24 Yaya za ka yi tsayayya da mafi ƙanƙantan hafsan shugabana, ko da kana dogara da Masar don kekunan yaƙi da mahaya dawakai?
Egypt kah leng neh marhang caem dongah na pangtung cakhaw ka boei kah sal rhoek khuiah rhalboei ca pakhat kah maelhmai te metlam na mael eh?
25 Ban da haka ma, kana gani cewa na zo in hallaka wannan wuri ne ba tare da na ji daga Ubangiji ba? Ubangiji da kansa ne ya ce da ni in kawo wa wannan ƙasa hari in hallaka ta.’”
BOEIPA lamkah mueh la he hmuen la ka pawk aya? Te te phae ham te BOEIPA loh kai taengah, 'Khohmuen he caeh thil lamtah khopuei te phae laeh,’ a ti,” a ti nah.
26 Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce wa jagoran dakarun, “Muna roƙonka ka yi wa bayinka magana da harshen Arameyik da yake muna ji. Kada ka yi mana magana da Yahudanci domin kada mutanen da suke bisa katanga su ji!”
Te vaengah Hilkiah capa Eliakim, Shebna neh Joah loh Rabshakeh te, “Na sal rhoek taengah Aramaih ol la thui mai, ka yakming u ngawn dongah vongtung sokah pilnam hna ah he kaimih ham Judah ol la thui boel mai,” a ti nah.
27 Amma shugaban sojojin ya ce, “Ai, ba gare ku da sarkinku kaɗai ne shugabana ya aike ni ba. Amma har ga mutanen da suke zaune a kan katangar birnin, waɗanda za su ci kashinsu, su sha fitsarinsu!”
Tedae Rabshakeh loh amih te, “He ol thui ham he ka boei loh na boei taeng neh nang taeng bueng ah kai n'tueih nim? Vongtung soah aka ngol tih a khawt aka sok, nangmih bangla a khopha dongkah a yun tui aka o hlang rhoek taengah moenih a?” a ti nah.
28 Sai shugaban sojojin ya yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji muryar babban sarki, sarkin Assuriya!
Te phoeiah Rabshakeh te pai tih Judah ol neh a len la pang. Te phoeiah a thui tih, “Assyria manghai boei kah manghai ol he hnatun uh.
29 Ga abin da sarki ya faɗa; kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku. Ba zai iya cetonku daga hannuna ba.
Manghai loh he ni a. thui. Nangmih te Hezekiah loh n'rhaithi boel saeh. A kut lamloh nangmih n'huul ham a coeng moenih.
30 Kada ku yarda Hezekiya yă rinjaye ku cewa ku dogara ga Allah, sa’ad da ya ce da ku, ‘Ba shakka Ubangiji zai cece mu; yana ce da ku birnin nan ba zai faɗa a hannun sarkin Assuriya ba.’
Nangmih te Hezekiah loh BOEIPA dongah m'pangtung sak tih, “BOEIPA loh mamih n'huul rhoe n'huul ni, khopuei he khaw Assyria manghai kut ah pae mahpawh,’ a ti moenih a?
31 “Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya ce, ku shirya zaman lafiya da ni, ku fito zuwa wurina. Kowane ɗayanku kuwa zai ci’ya’yan inabinsa da’ya’yan ɓaurensa, yă kuma sha ruwa daga randarsa,
Hezekiah ol te hnatun uh boeh. Assyria manghai loh he ni a. thui. Kai taengah yoethennah mah saii uh. Kai taengla ha mop uh lamtah hlang loh amah misur neh amah thaibu te rhip ca saeh. Hlang loh amah kah tuito tui te o saeh.
32 har lokacin da zan zo in kwashe ku, in kai ku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasa mai yalwar hatsi, da ruwan inabi, da abinci, da gonakin inabi, da itatuwan zaitun, da zuma, don ku rayu, kada ku mutu! “Kada ku saurari Hezekiya, don karya yake muku, sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’
Kai taengla na pawk hlan vaengah namah khohmuen banghui khohmuen la nangmih kang khuen coeng. Te tah cangpai neh misur thai khohmuen ni, buh neh misur khohmuen ni, olive situi neh khoitui khohmuen ni. Te dongah hing uh lamtah duek uh boeh. Hezekiah ol te hnatun uh boeh. Nangmih m'vueh m'vuehtih, “BOEIPA loh mamih n'huul bitni.
33 Akwai allahn wata al’ummar da ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
Namtom pathen rhoek loh a khohmuen dongah hlang te Assyria manghai kut lamloh a huul khaw a huul uh nim?
34 Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim, da na Hena, da na Iffa? Sun cece Samariya daga hannuna?
Khamath neh Arpad pathen rhoek te melae? Hena Sepharvaim neh Ivvah pathen rhoek te melae?’ a ti. Ka kut lamloh Samaria a huul uh tang a?
35 Wanne a cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa da gare ni? Shugaban sojojin ya kuma ci gaba da cewa, ta yaya Ubangiji zai ceci Urushalima daga hannuna?”
Khohmuen pathen boeih khuiah khaw ka kut lamloh a khohmuen aka huul te unim? BOEIPA loh Jerusalem te kai kut lamkah a huul tang aya?,” a ti nah.
36 Amma mutane suka yi shiru ba su amsa masa ba, domin sarki ya umarta cewa, “Kada ku amsa masa.”
Tedae manghai kah olpaek loh, “Anih te doo uh boeh,” a ti nah dongah pilnam khaw ngam tih anih te ol pakhat khaw doo uh van pawh.
37 Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf, marubuci, suka je wurin Hezekiya da tufafinsu a kece, suka faɗa masa abin da shugaban sojojin ya faɗa.
Te phoeiah im aka tawt Hilkiah capa Eliakim, cadaek Shebna, khocil aka khoem Asaph capa Joah tah himbai aka phen Hezekiah taengla cet uh tih Rabshakeh kah ol te a taengah a puen pauh.