< 2 Sarakuna 17 >

1 A shekara ta goma sha biyu ta mulkin Ahaz sarkin Yahuda, Hosheya ɗan Ela ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki na shekara tara.
La douzième année d'Achaz Roi de Juda, Hosée fils d'Ela [commença] à régner à Samarie sur Israël, [et il régna] neuf ans.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar na sarakunan Isra’ilan da suka riga shi ba.
Et il fit ce qui déplaît à l'Eternel, non pas toutefois comme les Rois d'Israël qui avaient été avant lui.
3 Shalmaneser sarkin Assuriya ya kawo wa Hosheya wanda dā abokin tarayyarsa ne, hari har Hosheya ya biya shi haraji.
Salmanéser Roi des Assyriens monta contre lui, et Hosée lui fut asservi, et il lui envoyait des présents.
4 Amma sarkin Assuriya ya gane cewa Hosheya mai cin amana ne, gama ya aika da wakilai wurin So sarkin Masar, ya kuma daina aika wa sarkin Assuriya haraji yadda ya saba yi kowace shekara. Saboda haka Shalmaneser ya kama shi ya sa a kurkuku.
Mais le Roi des Assyriens découvrit une conspiration en Hosée; car Hosée avait envoyé des messagers vers So, Roi d'Egypte, et il n'envoyait plus de présents tous les ans au Roi d'Assyrie; c'est pourquoi le Roi des Assyriens l'enferma, et le mit en prison.
5 Sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar Hosheya gaba ɗaya farmaki, ya kewaye Samariya na tsawon shekara uku.
Le Roi des Assyriens monta par tout le pays, et monta à Samarie, et l'assiégea pendant trois ans.
6 A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, sarkin Assuriya ya ci Samariya da yaƙi ya kuma kwashe Isra’ilawa zuwa Assuriya. Ya tsugunar da su a Hala, da a Gozan a bakin Kogin Habor da kuma a garuruwan Medes.
La neuvième année d'Hosée, le Roi des Assyriens prit Samarie, et transporta les Israëlites en Assyrie, et les fit habiter à Chalach, et sur Chabor fleuve de Gozan, et dans les villes des Mèdes.
7 Duk wannan ya faru ne saboda Isra’ilawa sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fitar da su daga Masar daga ƙarƙashin ikon Fir’auna sarkin Masar. Sun yi wa waɗansu alloli sujada
Car il était arrivé que les enfants d'Israël avaient péché contre l'Eternel leur Dieu qui les avait fait monter hors du pays d'Egypte, de dessous la main de Pharaon Roi d'Egypte, et avaient révéré d'autres dieux.
8 suka kuma bi gurbin al’umman da Ubangiji ya kora a gabansu, da kuma ayyukan da sarakuna Isra’ila suka gabatar.
Et ils avaient suivi le train des nations que l'Eternel avait chassées de devant les enfants d'Israël, et le train des Rois d'Israël qu'ils avaient établis.
9 Isra’ilawa a ɓoye sun aikata abubuwan da ba daidai ba ga Ubangiji Allahnsu. Tun daga hasumiyoyi har zuwa birane masu katanga, sun gina wa kansu wuraren sujada na tudu a dukan garuruwansu.
Et les enfants d'Israël avaient fait couvertement des choses qui n'étaient point droites devant l'Eternel leur Dieu; et s'étaient bâti des hauts lieux par toutes leurs villes, depuis la tour des gardes jusqu'aux villes fortes.
10 Suka kafa keɓaɓɓun duwatsu da kuma ginshiƙan Ashera a kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
Ils s'étaient dressé des statues, et [planté] des bocages, sur toutes les hautes collines et sous tout arbre verdoyant.
11 Suka ƙona turare a kan kowane tudu, kamar dai yadda al’umman da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka yi muguntan da ya sa Ubangiji ya yi fushi.
Ils avaient fait là des encensements dans tous les hauts lieux, à l'imitation des nations que l'Eternel avait chassées de devant eux; et ils avaient fait des choses méchantes pour irriter l'Eternel.
12 Suka bauta wa gumaka, ko da yake Ubangiji ya ce, “Ba za ku yi wannan ba.”
Et ils avaient servi les dieux de fiente, au sujet desquels l'Eternel leur avait dit: Vous ne ferez point cela.
13 Ubangiji ya yi wa Isra’ila da Yahuda kashedi ta bakin dukan annabawansa da kuma masu duba, cewa, “Ku juyo daga mugayen ayyukanku. Ku yi biyayya da umarnai da farillaina, bisa ga dukan Dokar da na dokaci kakanninku su bi, waɗanda na kuma bayar ta wurin bayina, annabawa.”
Et l'Eternel avait sommé Israël et Juda par le moyen de tous les Prophètes, ayant toute sorte de vision, en disant: Détournez-vous de toutes vos méchantes voies; retournez, et gardez mes commandements, et mes statuts, selon toute la Loi que j'ai commandée à vos pères, et que je vous ai envoyée par mes serviteurs les Prophètes.
14 Amma ba su saurare ni ba don sun kangare kamar kakanninsu, waɗanda ba su amince da Ubangiji Allahnsu ba.
Mais ils n'avaient point écouté, et ils avaient roidi leur cou, comme leurs pères [avaient roidi] leur cou, lesquels n'avaient point cru à l'Eternel leur Dieu.
15 Suka yi watsi da farillansa da yarjejjeniyar da ya ƙulla da kakanninsu, da kuma kashedin da ya yi musu. Suka bi gumaka marasa amfani, wannan ya sa su ma kansu suka zama marasa amfani. Suka kwaikwayi sauran ƙasashen da suke kewaye da su, ko da yake Ubangiji ya umarce su cewa, “Kada ku yi rayuwa irin tasu,” suka kuwa yi abin da Ubangiji ya hana su.
Et ils avaient dédaigné ses statuts, et son alliance, qu'il avait traitée avec leurs pères, et ses témoignages, par lesquels il les avait sommés, et avaient marché après la vanité, et étaient devenus vains, et avaient suivi les nations qui étaient autour d'eux, touchant lesquelles l'Eternel avait commandé qu'ils ne fissent point comme elles.
16 Suka wofinta dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu gumakan zubi na siffar’yan maruƙa biyu, da kuma ginshiƙin Ashera. Suka rusuna wa rundunan taurari, suka kuma yi wa Ba’al sujada.
Et ayant abandonné tous les commandements de l'Eternel leur Dieu, ils s'étaient fait des simulacres de fonte, [c'est-à-dire] deux veaux, et avaient planté des bocages, et s'étaient prosternés devant toute l'armée des cieux, et avaient servi Bahal.
17 Suka miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ta wuta. Suka yi duba, suka yi sihiri suka kuma ba da kansu ga mugunta a gaban Ubangiji; suka sa ya yi fushi.
Ils avaient fait aussi passer leurs fils, et leurs filles par le feu, et s'étaient adonnés aux divinations, et aux enchantements, et s'étaient vendus pour faire ce qui déplaît à l'Eternel afin de l'irriter.
18 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi ƙwarai da Isra’ila, ya kuma kawar da su daga gabansa. Kabilar Yahuda kaɗai aka bari,
C'est pourquoi l'Eternel fut fort irrité contre Israël, et il les rejeta, en sorte qu'il n'y eut que la seule Tribu de Juda, qui restât.
19 ko Yahuda ma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba. Sun bi gurbin da Isra’ila ta kawo.
Et même Juda ne garda point les commandements de l'Eternel son Dieu, mais ils marchèrent dans les ordonnances qu'Israël avait établies.
20 Saboda haka Ubangiji ya wofinta mutanen Isra’ila; ya azabtar da su, ya kuma ba da su a hannun masu kwasar ganima, sai da ya shafe su ƙaƙaf daga gabansa.
C'est pourquoi l'Eternel rejeta toute la race d'Israël, car il les affligea, et les livra entre les mains de ceux qui les pillaient, jusqu'à ce qu'il les eût rejetés de devant sa face.
21 Sa’ad da ya ware Isra’ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat sarki a kansu. Yerobowam ya rinjayi Isra’ila daga ƙin Ubangiji, ya sa suka aikata babban zunubi.
Parce qu'Israël s'était retranché de la maison de David, et avait établi Roi Jéroboam fils de Nébat, car Jéroboam avait débauché Israël, afin qu'il ne suivît plus l'Eternel, et leur avait fait commettre un grand péché.
22 Isra’ila suka nace cikin dukan zunuban Yerobowam, ba su kuwa rabu da su ba
C'est pourquoi les enfants d'Israël marchèrent dans tous les péchés que Jéroboam avait faits, et ils ne s'en sont point retirés.
23 har Ubangiji ya kawar da su daga gabansa, kamar yadda ya gargaɗe su ta bakin bayinsa annabawa. Saboda haka aka kwashi mutanen Isra’ila daga ƙasarsu zuwa bauta a Assuriya, har wa yau kuwa suna can.
Jusqu'à ce que l'Eternel les a rejetés de devant soi, selon qu'il en avait parlé par le moyen de tous ses serviteurs les Prophètes; et Israël a été transporté de dessus la terre en Assyrie, jusqu'à ce jour.
24 Sarkin Assuriya ya kawo mutane daga Babilon, Kuta, Afa, Hamat da Sefarfayim ya zaunar da su a garuruwan Samariya don su maya gurbin Isra’ilawa. Suka mallaki Samariya suka kuma zauna a garuruwansu.
Et le Roi des Assyriens fit venir des gens de Babel, et de Cuth, et de Hava, et de Hamath, et de Sépharvajim, et les fit habiter dans les villes de Samarie, en la place des enfants d'Israël; et ils possédèrent la Samarie, et ils habitèrent dans ses villes.
25 Sa’ad da suka fara zama a can, ba su bauta wa Ubangiji ba; saboda haka ya aika da zakoki a tsakaninsu suka karkashe waɗansu mutane.
Or il arriva qu'au commencement qu'ils habitèrent là, ils ne révérèrent point l'Eternel, et l'Eternel envoya contr'eux des lions, qui les tuaient.
26 Sai aka faɗa wa sarkin Assuriya cewa, “Mutanen da ka kwashe ka zaunar a garuruwan Samariya fa ba su san abin da allahn ƙasar yake bukata ba. Saboda haka allahn ƙasar ya tura zakoki a cikinsu, waɗanda suke karkashe su, domin mutanen ba su san abin da yake bukata ba.”
Et on dit au Roi des Assyriens: Les nations que tu as transportées et fait habiter dans les villes de Samarie, ne savent pas la manière de servir le Dieu du pays; c'est pourquoi il a envoyé contr'eux des lions, et voilà, [ces lions] les tuent, parce qu'ils ne savent pas la manière de servir le Dieu du pays.
27 Sai sarkin Assuriya ya ba da umarni cewa, “A sami wani daga cikin firistocin da aka kwaso zuwa bauta daga Samariya, yă koma yă zauna a can, yă koya wa mutanen abin da allahn ƙasar yake bukata.”
Alors le Roi des Assyriens commanda, en disant: Faites aller là quelqu'un des Sacrificateurs que vous en avez transportés; qu'on aille donc, et qu'on demeure là, et qu'on enseigne la manière de servir le Dieu du pays.
28 Saboda haka ɗaya daga cikin firistocin da aka kawo bauta daga Samariya ya dawo ya zauna a Betel, ya koya musu yadda za su yi sujada ga Ubangiji.
Ainsi un des Sacrificateurs qu'on avait transportés de Samarie, vint et habita à Béthel, et il leur enseignait comment ils devaient révérer l'Eternel.
29 Duk da haka, jama’ar kowace ƙasa, suka ƙera tasu alloli a garuruwa masu yawa inda suke zaune, suka sa su a masujadan da mutanen Samariya suka gina a kan tuddai.
Mais chaque nation fit ses dieux, et ils les mirent dans les maisons des hauts lieux que les Samaritains avaient faits; chaque nation les mit dans ses villes où ils habitaient.
30 Mutane daga Babilon suka ƙera Sukkot Benot, mutane daga Kut suka ƙera Nergal, mutane daga Hamat suka ƙera Ashima;
Car les gens de Babel firent Succoth-benoth; et les gens de Cuth firent Nergal; et les gens de Hamath firent Asima.
31 Awwiyawa suka ƙera Nibhaz da Tartak, Sefarfayawa kuwa suka ƙone’ya’yansu a wuta a matsayi hadayu ga Adrammelek da Anammelek allolin Sefarfayim.
Et les Haviens firent Nibchaz et Tartac; mais ceux de Sépharvajim brûlaient leurs enfants au feu à Adrammélec et Hanammélec, les dieux de Sépharvajim.
32 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka zaɓi mutanensu su yi musu hidima a matsayin firistoci a masujadan da suke kan tuddai.
Toutefois ils révéraient l'Eternel, et ils établirent pour Sacrificateurs des hauts lieux des derniers d'entr'eux, qui leur faisaient [le service] dans les maisons des hauts lieux.
33 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma sun bauta wa allolinsu bisa ga al’adun ƙasashen da suka fito.
[Ainsi] ils révéraient l'Eternel, et en même temps ils servaient leurs dieux à la manière des nations qu'on avait transportées hors de là.
34 Har yă zuwa yau, sun nace da ayyukansu na dā. Ba sa yin wa Ubangiji sujada, ba sa kuma bin dokoki da farillansa, dokoki da umarnan da Ubangiji ya ba wa zuriyar Yaƙub, wadda ya ba wa suna Isra’ila.
Et jusqu'à ce jour ils font selon leurs premières coutumes; ils ne révèrent point l'Eternel, et néanmoins ils ne font ni selon leurs statuts et selon leurs ordonnances, ni selon la Loi [et] le commandement que l'Eternel Dieu donna aux enfants de Jacob, lequel il nomma Israël.
35 Da Ubangiji ya ƙulla alkawari da Isra’ilawa, ya dokace su cewa, “Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada ko ku durƙusa a gabansu ku bauta musu, ko ku miƙa musu hadaya.
Avec lesquels l'Eternel avait traité alliance, et auxquels il avait commandé, en disant: Vous ne révérerez point d'autres dieux, et ne vous prosternerez point devant eux; vous ne les servirez point, et vous ne leur sacrifierez point.
36 Amma Ubangiji wanda ya fito da ku daga Masar da iko mai girma da hannu mai ƙarfi, shi ne za ku yi masa sujada. Gare shi za ku durƙusa ku kuma miƙa masa hadayu.
Mais vous révérerez l'Eternel qui vous a fait monter hors du pays d'Egypte par une grande force, et avec un bras étendu; et vous vous prosternerez devant lui, et vous lui sacrifierez.
37 Dole kullum ku mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da farillan, dokoki da umarnan da ya rubuta muku. Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada.
Vous prendrez garde à faire toujours les statuts, les ordonnances, la Loi, et les commandements qu'il vous a écrits; et vous ne révérerez point d'autres dieux.
38 Kada ku manta da alkawarin da na ƙulla da ku, kada ku yi sujada ga waɗansu alloli.
Vous n'oublierez donc point l'alliance que j'ai traitée avec vous, et vous ne révérerez point d'autres dieux;
39 Maimakon haka, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada; shi ne zai cece ku daga hannun abokan gābanku.”
Mais vous révérerez l'Eternel votre Dieu, et il vous délivrera de la main de tous vos ennemis.
40 Amma ba su saurara ba, suka nace da ayyukansu na dā.
Mais ils n'écoutèrent point, et ils firent selon leurs premières coutumes.
41 Ko ma yayinda mutanen nan suke yi wa Ubangiji sujada, ba su daina bauta wa gumakansu ba. Har yă zuwa yau,’ya’yansu da jikokinsu sun ci gaba da bin gurbin kakanninsu.
Ainsi ces nations-là révéraient l'Eternel, et servaient en même temps leurs images; et leurs enfants, et les enfants de leurs enfants font jusqu'à ce jour comme leurs pères ont fait.

< 2 Sarakuna 17 >