< 2 Sarakuna 17 >

1 A shekara ta goma sha biyu ta mulkin Ahaz sarkin Yahuda, Hosheya ɗan Ela ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki na shekara tara.
La douzième année d’Achaz, roi de Juda, Osée, fils d’Éla, commença de régner à Samarie sur Israël; [il régna] neuf ans.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar na sarakunan Isra’ilan da suka riga shi ba.
Et il fit ce qui est mauvais aux yeux de l’Éternel, non pas toutefois comme les rois d’Israël qui avaient été avant lui.
3 Shalmaneser sarkin Assuriya ya kawo wa Hosheya wanda dā abokin tarayyarsa ne, hari har Hosheya ya biya shi haraji.
Shalmanéser, roi d’Assyrie, monta contre lui, et Osée devint son serviteur, et lui envoya des présents.
4 Amma sarkin Assuriya ya gane cewa Hosheya mai cin amana ne, gama ya aika da wakilai wurin So sarkin Masar, ya kuma daina aika wa sarkin Assuriya haraji yadda ya saba yi kowace shekara. Saboda haka Shalmaneser ya kama shi ya sa a kurkuku.
Et le roi d’Assyrie découvrit qu’Osée conspirait; car [Osée] avait envoyé des messagers à Sô, roi d’Égypte, et il n’envoyait pas de présents au roi d’Assyrie comme [il avait fait] d’année en année; et le roi d’Assyrie l’enferma dans une prison et le lia.
5 Sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar Hosheya gaba ɗaya farmaki, ya kewaye Samariya na tsawon shekara uku.
Et le roi d’Assyrie monta par tout le pays, et monta à Samarie, et l’assiégea trois ans.
6 A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, sarkin Assuriya ya ci Samariya da yaƙi ya kuma kwashe Isra’ilawa zuwa Assuriya. Ya tsugunar da su a Hala, da a Gozan a bakin Kogin Habor da kuma a garuruwan Medes.
La neuvième année d’Osée, le roi d’Assyrie prit Samarie, et il transporta Israël en Assyrie, et les fit habiter à Khalakh, et sur le Khabor, fleuve de Gozan, et dans les villes des Mèdes.
7 Duk wannan ya faru ne saboda Isra’ilawa sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fitar da su daga Masar daga ƙarƙashin ikon Fir’auna sarkin Masar. Sun yi wa waɗansu alloli sujada
Et il était arrivé que les fils d’Israël avaient péché contre l’Éternel, leur Dieu, qui les avait fait monter du pays d’Égypte, de dessous la main du Pharaon, roi d’Égypte, et qu’ils avaient révéré d’autres dieux.
8 suka kuma bi gurbin al’umman da Ubangiji ya kora a gabansu, da kuma ayyukan da sarakuna Isra’ila suka gabatar.
Et ils marchèrent dans les statuts des nations que l’Éternel avait dépossédées devant les fils d’Israël, et [dans ceux] que les rois d’Israël avaient établis.
9 Isra’ilawa a ɓoye sun aikata abubuwan da ba daidai ba ga Ubangiji Allahnsu. Tun daga hasumiyoyi har zuwa birane masu katanga, sun gina wa kansu wuraren sujada na tudu a dukan garuruwansu.
Et les fils d’Israël firent en secret contre l’Éternel, leur Dieu, des choses qui ne sont pas droites; et ils se bâtirent des hauts lieux dans toutes leurs villes, depuis la tour des gardes jusqu’à la ville forte;
10 Suka kafa keɓaɓɓun duwatsu da kuma ginshiƙan Ashera a kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
et ils se dressèrent des statues et des ashères sur toute haute colline et sous tout arbre vert,
11 Suka ƙona turare a kan kowane tudu, kamar dai yadda al’umman da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka yi muguntan da ya sa Ubangiji ya yi fushi.
et firent fumer là de l’encens sur tous les hauts lieux, comme les nations que l’Éternel avait transportées de devant eux; et ils firent des choses mauvaises, pour provoquer à colère l’Éternel;
12 Suka bauta wa gumaka, ko da yake Ubangiji ya ce, “Ba za ku yi wannan ba.”
et ils servirent les idoles, au sujet desquelles l’Éternel leur avait dit: Vous ne ferez point cela.
13 Ubangiji ya yi wa Isra’ila da Yahuda kashedi ta bakin dukan annabawansa da kuma masu duba, cewa, “Ku juyo daga mugayen ayyukanku. Ku yi biyayya da umarnai da farillaina, bisa ga dukan Dokar da na dokaci kakanninku su bi, waɗanda na kuma bayar ta wurin bayina, annabawa.”
Et l’Éternel rendit témoignage contre Israël et contre Juda par tous les prophètes, tous les voyants, disant: Détournez-vous de vos mauvaises voies; et gardez mes commandements, mes statuts, selon toute la loi que j’ai commandée à vos pères et que je vous ai envoyée par mes serviteurs les prophètes.
14 Amma ba su saurare ni ba don sun kangare kamar kakanninsu, waɗanda ba su amince da Ubangiji Allahnsu ba.
Et ils n’écoutèrent pas, et roidirent leur cou comme le cou de leurs pères, qui n’avaient pas cru l’Éternel, leur Dieu.
15 Suka yi watsi da farillansa da yarjejjeniyar da ya ƙulla da kakanninsu, da kuma kashedin da ya yi musu. Suka bi gumaka marasa amfani, wannan ya sa su ma kansu suka zama marasa amfani. Suka kwaikwayi sauran ƙasashen da suke kewaye da su, ko da yake Ubangiji ya umarce su cewa, “Kada ku yi rayuwa irin tasu,” suka kuwa yi abin da Ubangiji ya hana su.
Et ils rejetèrent ses statuts, et son alliance qu’il avait faite avec leurs pères, et ses témoignages qu’il leur avait donnés, et ils marchèrent après la vanité, et agirent vainement, et en suivant les nations qui étaient autour d’eux, touchant lesquelles l’Éternel leur avait commandé de ne pas faire comme elles.
16 Suka wofinta dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu gumakan zubi na siffar’yan maruƙa biyu, da kuma ginshiƙin Ashera. Suka rusuna wa rundunan taurari, suka kuma yi wa Ba’al sujada.
Et ils abandonnèrent tous les commandements de l’Éternel, leur Dieu, et se firent des images de fonte, deux veaux, et se firent des ashères, et se prosternèrent devant toute l’armée des cieux, et servirent Baal.
17 Suka miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ta wuta. Suka yi duba, suka yi sihiri suka kuma ba da kansu ga mugunta a gaban Ubangiji; suka sa ya yi fushi.
Et ils firent passer leurs fils et leurs filles par le feu, et pratiquèrent la divination et s’adonnèrent aux enchantements, et se vendirent pour faire ce qui est mauvais aux yeux de l’Éternel, pour le provoquer à colère.
18 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi ƙwarai da Isra’ila, ya kuma kawar da su daga gabansa. Kabilar Yahuda kaɗai aka bari,
Et l’Éternel fut très irrité contre Israël, et les ôta de devant sa face; il n’en resta que la seule tribu de Juda.
19 ko Yahuda ma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba. Sun bi gurbin da Isra’ila ta kawo.
Et Juda non plus ne garda pas les commandements de l’Éternel, son Dieu; et ils marchèrent dans les statuts qu’Israël avait établis.
20 Saboda haka Ubangiji ya wofinta mutanen Isra’ila; ya azabtar da su, ya kuma ba da su a hannun masu kwasar ganima, sai da ya shafe su ƙaƙaf daga gabansa.
Et l’Éternel rejeta toute la semence d’Israël, et il les affligea, et les livra en la main des pillards, jusqu’à ce qu’il les ait rejetés de devant sa face.
21 Sa’ad da ya ware Isra’ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat sarki a kansu. Yerobowam ya rinjayi Isra’ila daga ƙin Ubangiji, ya sa suka aikata babban zunubi.
Car Israël s’était séparé de la maison de David, et avait fait roi Jéroboam, fils de Nebath; et Jéroboam avait détourné violemment Israël de suivre l’Éternel, et les avait fait commettre un grand péché.
22 Isra’ila suka nace cikin dukan zunuban Yerobowam, ba su kuwa rabu da su ba
Et les fils d’Israël marchèrent dans tous les péchés que Jéroboam avait commis; ils ne s’en détournèrent point,
23 har Ubangiji ya kawar da su daga gabansa, kamar yadda ya gargaɗe su ta bakin bayinsa annabawa. Saboda haka aka kwashi mutanen Isra’ila daga ƙasarsu zuwa bauta a Assuriya, har wa yau kuwa suna can.
jusqu’à ce que l’Éternel ôta Israël de devant sa face, comme il avait dit par tous ses serviteurs les prophètes; et Israël fut transporté de dessus sa terre en Assyrie, [où il est] jusqu’à ce jour.
24 Sarkin Assuriya ya kawo mutane daga Babilon, Kuta, Afa, Hamat da Sefarfayim ya zaunar da su a garuruwan Samariya don su maya gurbin Isra’ilawa. Suka mallaki Samariya suka kuma zauna a garuruwansu.
Et le roi d’Assyrie fit venir [des gens] de Babel, et de Cuth, et d’Avva, et de Hamath, et de Sepharvaïm, et [les] fit habiter dans les villes de la Samarie, à la place des fils d’Israël; et ils possédèrent la Samarie, et habitèrent dans ses villes.
25 Sa’ad da suka fara zama a can, ba su bauta wa Ubangiji ba; saboda haka ya aika da zakoki a tsakaninsu suka karkashe waɗansu mutane.
Et il arriva, quand ils commencèrent d’y habiter, qu’ils ne craignaient pas l’Éternel, et l’Éternel envoya contre eux des lions qui les tuaient.
26 Sai aka faɗa wa sarkin Assuriya cewa, “Mutanen da ka kwashe ka zaunar a garuruwan Samariya fa ba su san abin da allahn ƙasar yake bukata ba. Saboda haka allahn ƙasar ya tura zakoki a cikinsu, waɗanda suke karkashe su, domin mutanen ba su san abin da yake bukata ba.”
Et on parla au roi d’Assyrie, disant: Les nations que tu as transportées et que tu as fait habiter dans les villes de Samarie ne connaissent pas la coutume du dieu du pays, et il a envoyé contre elles des lions, et voici, [ces lions] les font mourir, parce qu’elles ne connaissent pas la coutume du dieu du pays.
27 Sai sarkin Assuriya ya ba da umarni cewa, “A sami wani daga cikin firistocin da aka kwaso zuwa bauta daga Samariya, yă koma yă zauna a can, yă koya wa mutanen abin da allahn ƙasar yake bukata.”
Et le roi d’Assyrie commanda, disant: Faites aller là quelqu’un des sacrificateurs que vous en avez transportés; et qu’il aille et qu’il demeure là, et qu’il leur enseigne la coutume du dieu du pays.
28 Saboda haka ɗaya daga cikin firistocin da aka kawo bauta daga Samariya ya dawo ya zauna a Betel, ya koya musu yadda za su yi sujada ga Ubangiji.
Et un des sacrificateurs qu’on avait transportés de Samarie, vint et habita à Béthel, et il leur enseignait comment ils devaient craindre l’Éternel.
29 Duk da haka, jama’ar kowace ƙasa, suka ƙera tasu alloli a garuruwa masu yawa inda suke zaune, suka sa su a masujadan da mutanen Samariya suka gina a kan tuddai.
Et chaque nation se fit ses dieux, et elles les placèrent dans les maisons des hauts lieux que les Samaritains avaient faites, chaque nation dans ses villes où elle habitait.
30 Mutane daga Babilon suka ƙera Sukkot Benot, mutane daga Kut suka ƙera Nergal, mutane daga Hamat suka ƙera Ashima;
Et les hommes de Babel firent Succoth-Benoth; et les hommes de Cuth firent Nergal; et les hommes de Hamath firent Ashima;
31 Awwiyawa suka ƙera Nibhaz da Tartak, Sefarfayawa kuwa suka ƙone’ya’yansu a wuta a matsayi hadayu ga Adrammelek da Anammelek allolin Sefarfayim.
et les Avviens firent Nibkhaz et Tharthak; et les Sepharviens brûlaient au feu leurs fils à Adrammélec et à Anammélec, les dieux de Sepharvaïm.
32 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka zaɓi mutanensu su yi musu hidima a matsayin firistoci a masujadan da suke kan tuddai.
Et ils craignaient l’Éternel, et se firent d’entre toutes les classes [du peuple] des sacrificateurs des hauts lieux, qui offraient [des sacrifices] pour eux dans les maisons des hauts lieux:
33 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma sun bauta wa allolinsu bisa ga al’adun ƙasashen da suka fito.
ils craignaient l’Éternel, et ils servaient leurs dieux selon la coutume des nations d’où ils avaient été transportés.
34 Har yă zuwa yau, sun nace da ayyukansu na dā. Ba sa yin wa Ubangiji sujada, ba sa kuma bin dokoki da farillansa, dokoki da umarnan da Ubangiji ya ba wa zuriyar Yaƙub, wadda ya ba wa suna Isra’ila.
Jusqu’à ce jour ils font selon leurs premières coutumes: ils ne craignent pas l’Éternel, et ils ne font pas selon leurs statuts et selon leurs coutumes, ni selon la loi et selon le commandement que l’Éternel avait commandés aux fils de Jacob, qu’il nomma Israël.
35 Da Ubangiji ya ƙulla alkawari da Isra’ilawa, ya dokace su cewa, “Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada ko ku durƙusa a gabansu ku bauta musu, ko ku miƙa musu hadaya.
Et l’Éternel avait fait alliance avec eux, et il leur avait commandé, disant: Vous ne craindrez point d’autres dieux, et vous ne vous prosternerez point devant eux; et vous ne les servirez point, et ne leur sacrifierez point.
36 Amma Ubangiji wanda ya fito da ku daga Masar da iko mai girma da hannu mai ƙarfi, shi ne za ku yi masa sujada. Gare shi za ku durƙusa ku kuma miƙa masa hadayu.
Mais l’Éternel seul, qui vous a fait monter du pays d’Égypte par une grande force et à bras étendu, lui, vous le craindrez, et vous vous prosternerez devant lui, et à lui vous sacrifierez.
37 Dole kullum ku mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da farillan, dokoki da umarnan da ya rubuta muku. Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada.
Et les statuts, et les ordonnances, et la loi, et le commandement, qu’il a écrits pour vous, vous prendrez garde à les pratiquer tous les jours; et vous ne craindrez pas d’autres dieux.
38 Kada ku manta da alkawarin da na ƙulla da ku, kada ku yi sujada ga waɗansu alloli.
Et vous n’oublierez pas l’alliance que j’ai faite avec vous, et vous ne craindrez pas d’autres dieux;
39 Maimakon haka, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada; shi ne zai cece ku daga hannun abokan gābanku.”
mais vous craindrez l’Éternel, votre Dieu, et lui vous délivrera de la main de tous vos ennemis.
40 Amma ba su saurara ba, suka nace da ayyukansu na dā.
Et ils n’écoutèrent pas, mais ils firent selon leur première coutume.
41 Ko ma yayinda mutanen nan suke yi wa Ubangiji sujada, ba su daina bauta wa gumakansu ba. Har yă zuwa yau,’ya’yansu da jikokinsu sun ci gaba da bin gurbin kakanninsu.
Et ces nations-là craignaient l’Éternel, et servaient leurs images; leurs fils aussi, et les fils de leurs fils, font jusqu’à ce jour comme leurs pères ont fait.

< 2 Sarakuna 17 >