< 2 Sarakuna 17 >
1 A shekara ta goma sha biyu ta mulkin Ahaz sarkin Yahuda, Hosheya ɗan Ela ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki na shekara tara.
La douzième année d'Achaz, roi de Juda, Osée, fils d'Éla, régna à Samarie sur Israël pendant neuf ans.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar na sarakunan Isra’ilan da suka riga shi ba.
Il fit ce qui est mal aux yeux de Yahvé, mais pas comme les rois d'Israël qui l'ont précédé.
3 Shalmaneser sarkin Assuriya ya kawo wa Hosheya wanda dā abokin tarayyarsa ne, hari har Hosheya ya biya shi haraji.
Shalmaneser, roi d'Assyrie, monta contre lui; Hoshea devint son serviteur et lui apporta un tribut.
4 Amma sarkin Assuriya ya gane cewa Hosheya mai cin amana ne, gama ya aika da wakilai wurin So sarkin Masar, ya kuma daina aika wa sarkin Assuriya haraji yadda ya saba yi kowace shekara. Saboda haka Shalmaneser ya kama shi ya sa a kurkuku.
Le roi d'Assyrie découvrit une conspiration chez Hosée, car il avait envoyé des messagers à So, roi d'Égypte, et n'avait pas offert de tribut au roi d'Assyrie, comme il l'avait fait d'année en année. C'est pourquoi le roi d'Assyrie se saisit de lui et le fit mettre en prison.
5 Sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar Hosheya gaba ɗaya farmaki, ya kewaye Samariya na tsawon shekara uku.
Puis le roi d'Assyrie parcourut tout le pays, monta à Samarie et l'assiégea pendant trois ans.
6 A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, sarkin Assuriya ya ci Samariya da yaƙi ya kuma kwashe Isra’ilawa zuwa Assuriya. Ya tsugunar da su a Hala, da a Gozan a bakin Kogin Habor da kuma a garuruwan Medes.
La neuvième année d'Osée, le roi d'Assyrie prit Samarie et emmena Israël en Assyrie. Il les plaça à Halah, sur le Habor, le fleuve de Gozan, et dans les villes des Mèdes.
7 Duk wannan ya faru ne saboda Isra’ilawa sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fitar da su daga Masar daga ƙarƙashin ikon Fir’auna sarkin Masar. Sun yi wa waɗansu alloli sujada
C'est parce que les enfants d'Israël avaient péché contre l'Éternel, leur Dieu, qui les avait fait monter du pays d'Égypte, de dessous la main de Pharaon, roi d'Égypte, et qu'ils avaient craint d'autres dieux,
8 suka kuma bi gurbin al’umman da Ubangiji ya kora a gabansu, da kuma ayyukan da sarakuna Isra’ila suka gabatar.
et suivi les lois des nations que l'Éternel avait chassées devant les enfants d'Israël, et des rois d'Israël, qu'ils avaient établis.
9 Isra’ilawa a ɓoye sun aikata abubuwan da ba daidai ba ga Ubangiji Allahnsu. Tun daga hasumiyoyi har zuwa birane masu katanga, sun gina wa kansu wuraren sujada na tudu a dukan garuruwansu.
Les enfants d'Israël firent en secret des choses injustes à l'égard de Yahvé, leur Dieu; ils se bâtirent des hauts lieux dans toutes leurs villes, depuis la tour de guet jusqu'à la ville fortifiée;
10 Suka kafa keɓaɓɓun duwatsu da kuma ginshiƙan Ashera a kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
ils se dressèrent des colonnes et des mâts d'Astarté sur toute colline élevée et sous tout arbre vert;
11 Suka ƙona turare a kan kowane tudu, kamar dai yadda al’umman da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka yi muguntan da ya sa Ubangiji ya yi fushi.
Ils brûlèrent de l'encens sur tous les hauts lieux, comme le faisaient les nations que Yahvé avait chassées avant eux, et ils firent des choses méchantes pour irriter Yahvé.
12 Suka bauta wa gumaka, ko da yake Ubangiji ya ce, “Ba za ku yi wannan ba.”
Ils servirent des idoles dont Yahvé leur avait dit: « Tu ne feras pas cela ». »
13 Ubangiji ya yi wa Isra’ila da Yahuda kashedi ta bakin dukan annabawansa da kuma masu duba, cewa, “Ku juyo daga mugayen ayyukanku. Ku yi biyayya da umarnai da farillaina, bisa ga dukan Dokar da na dokaci kakanninku su bi, waɗanda na kuma bayar ta wurin bayina, annabawa.”
Mais l'Éternel a rendu témoignage à Israël et à Juda, par tous les prophètes et tous les voyants, en disant: « Revenez de vos mauvaises voies, et observez mes commandements et mes statuts, selon toute la loi que j'ai prescrite à vos pères et que je vous ai envoyée par mes serviteurs les prophètes. »
14 Amma ba su saurare ni ba don sun kangare kamar kakanninsu, waɗanda ba su amince da Ubangiji Allahnsu ba.
Mais ils n'ont pas voulu écouter, et ils ont endurci leur cou, comme le cou de leurs pères qui n'ont pas cru en Yahvé, leur Dieu.
15 Suka yi watsi da farillansa da yarjejjeniyar da ya ƙulla da kakanninsu, da kuma kashedin da ya yi musu. Suka bi gumaka marasa amfani, wannan ya sa su ma kansu suka zama marasa amfani. Suka kwaikwayi sauran ƙasashen da suke kewaye da su, ko da yake Ubangiji ya umarce su cewa, “Kada ku yi rayuwa irin tasu,” suka kuwa yi abin da Ubangiji ya hana su.
Ils rejetèrent ses lois et l'alliance qu'il avait conclue avec leurs pères, et les témoignages qu'il leur avait adressés; ils suivirent la vanité, ils devinrent vains, et ils suivirent les nations qui les entouraient, au sujet desquelles l'Éternel leur avait ordonné de ne pas faire comme elles.
16 Suka wofinta dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu gumakan zubi na siffar’yan maruƙa biyu, da kuma ginshiƙin Ashera. Suka rusuna wa rundunan taurari, suka kuma yi wa Ba’al sujada.
Ils abandonnèrent tous les commandements de l'Éternel, leur Dieu, et se firent des images en fonte, deux veaux, ils se firent une idole, ils se prosternèrent devant toute l'armée du ciel et servirent Baal.
17 Suka miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ta wuta. Suka yi duba, suka yi sihiri suka kuma ba da kansu ga mugunta a gaban Ubangiji; suka sa ya yi fushi.
Ils firent passer leurs fils et leurs filles par le feu, utilisèrent la divination et les enchantements, et se vendirent pour faire ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, pour l'irriter.
18 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi ƙwarai da Isra’ila, ya kuma kawar da su daga gabansa. Kabilar Yahuda kaɗai aka bari,
C'est pourquoi l'Éternel fut très irrité contre Israël, et il l'éloigna de sa vue. Il ne resta plus que la tribu de Juda seule.
19 ko Yahuda ma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba. Sun bi gurbin da Isra’ila ta kawo.
Juda aussi n'a pas gardé les commandements de l'Éternel, son Dieu, et il a suivi les lois d'Israël qu'il avait établies.
20 Saboda haka Ubangiji ya wofinta mutanen Isra’ila; ya azabtar da su, ya kuma ba da su a hannun masu kwasar ganima, sai da ya shafe su ƙaƙaf daga gabansa.
L'Éternel rejeta toute la descendance d'Israël, il l'affligea et la livra entre les mains de pillards, jusqu'à ce qu'il l'eût chassée de sa vue.
21 Sa’ad da ya ware Isra’ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat sarki a kansu. Yerobowam ya rinjayi Isra’ila daga ƙin Ubangiji, ya sa suka aikata babban zunubi.
Car il arracha Israël de la maison de David, et ils firent roi Jéroboam, fils de Nebath; et Jéroboam éloigna Israël de la suite de l'Éternel, et lui fit commettre un grand péché.
22 Isra’ila suka nace cikin dukan zunuban Yerobowam, ba su kuwa rabu da su ba
Les enfants d'Israël marchèrent dans tous les péchés que Jéroboam avait commis; ils ne s'en détournèrent pas
23 har Ubangiji ya kawar da su daga gabansa, kamar yadda ya gargaɗe su ta bakin bayinsa annabawa. Saboda haka aka kwashi mutanen Isra’ila daga ƙasarsu zuwa bauta a Assuriya, har wa yau kuwa suna can.
jusqu'à ce que Yahvé eût éloigné Israël de sa face, comme il l'avait annoncé par tous ses serviteurs les prophètes. C'est ainsi qu'Israël fut transporté hors de son pays, en Assyrie, jusqu'à ce jour.
24 Sarkin Assuriya ya kawo mutane daga Babilon, Kuta, Afa, Hamat da Sefarfayim ya zaunar da su a garuruwan Samariya don su maya gurbin Isra’ilawa. Suka mallaki Samariya suka kuma zauna a garuruwansu.
Le roi d'Assyrie fit venir des gens de Babylone, de Cuthah, d'Avva, de Hamath et de Sépharvaïm, et les plaça dans les villes de Samarie à la place des enfants d'Israël; ils possédèrent Samarie et habitèrent dans ses villes.
25 Sa’ad da suka fara zama a can, ba su bauta wa Ubangiji ba; saboda haka ya aika da zakoki a tsakaninsu suka karkashe waɗansu mutane.
Au début de leur séjour dans cette ville, ils ne craignaient pas Yahvé. L'Éternel envoya contre eux des lions qui tuèrent quelques-uns d'entre eux.
26 Sai aka faɗa wa sarkin Assuriya cewa, “Mutanen da ka kwashe ka zaunar a garuruwan Samariya fa ba su san abin da allahn ƙasar yake bukata ba. Saboda haka allahn ƙasar ya tura zakoki a cikinsu, waɗanda suke karkashe su, domin mutanen ba su san abin da yake bukata ba.”
Ils parlèrent alors au roi d'Assyrie, en disant: « Les nations que tu as emmenées et placées dans les villes de Samarie ne connaissent pas la loi du dieu du pays. C'est pourquoi il a envoyé des lions parmi elles; et voici qu'ils les tuent, parce qu'elles ne connaissent pas la loi du dieu du pays. »
27 Sai sarkin Assuriya ya ba da umarni cewa, “A sami wani daga cikin firistocin da aka kwaso zuwa bauta daga Samariya, yă koma yă zauna a can, yă koya wa mutanen abin da allahn ƙasar yake bukata.”
Alors le roi d'Assyrie donna cet ordre: « Porte là l'un des prêtres que tu as fait venir de là-bas; qu'il aille y demeurer, et qu'il leur enseigne la loi du dieu du pays. »
28 Saboda haka ɗaya daga cikin firistocin da aka kawo bauta daga Samariya ya dawo ya zauna a Betel, ya koya musu yadda za su yi sujada ga Ubangiji.
L'un des prêtres qu'ils avaient emmenés de Samarie vint habiter à Béthel et leur enseigna comment ils devaient craindre Yahvé.
29 Duk da haka, jama’ar kowace ƙasa, suka ƙera tasu alloli a garuruwa masu yawa inda suke zaune, suka sa su a masujadan da mutanen Samariya suka gina a kan tuddai.
Mais chaque nation se fit ses propres dieux et les plaça dans les maisons des hauts lieux que les Samaritains avaient construits, chaque nation dans les villes qu'elle habitait.
30 Mutane daga Babilon suka ƙera Sukkot Benot, mutane daga Kut suka ƙera Nergal, mutane daga Hamat suka ƙera Ashima;
Les hommes de Babylone firent Succoth Benoth, les hommes de Cuth firent Nergal, les hommes de Hamath firent Ashima,
31 Awwiyawa suka ƙera Nibhaz da Tartak, Sefarfayawa kuwa suka ƙone’ya’yansu a wuta a matsayi hadayu ga Adrammelek da Anammelek allolin Sefarfayim.
les Avvites firent Nibhaz et Tartak, et les Sépharvites brûlèrent leurs enfants au feu en l'honneur d'Adrammelech et d'Anammelech, les dieux de Sépharvaïm.
32 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka zaɓi mutanensu su yi musu hidima a matsayin firistoci a masujadan da suke kan tuddai.
Ils craignaient Yahvé, et ils se firent des prêtres des hauts lieux, qui sacrifiaient pour eux dans les maisons des hauts lieux.
33 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma sun bauta wa allolinsu bisa ga al’adun ƙasashen da suka fito.
Ils craignaient l'Éternel, et ils servaient leurs propres dieux, selon les coutumes des nations parmi lesquelles ils avaient été transportés.
34 Har yă zuwa yau, sun nace da ayyukansu na dā. Ba sa yin wa Ubangiji sujada, ba sa kuma bin dokoki da farillansa, dokoki da umarnan da Ubangiji ya ba wa zuriyar Yaƙub, wadda ya ba wa suna Isra’ila.
Aujourd'hui encore, ils font ce qu'ils faisaient auparavant. Ils ne craignent pas Yahvé, et ils ne suivent ni les lois, ni les ordonnances, ni la loi, ni le commandement que Yahvé a prescrits aux enfants de Jacob, qu'il a appelés Israël,
35 Da Ubangiji ya ƙulla alkawari da Isra’ilawa, ya dokace su cewa, “Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada ko ku durƙusa a gabansu ku bauta musu, ko ku miƙa musu hadaya.
avec lesquels Yahvé avait fait alliance et leur avait donné cet ordre: « Vous ne craindrez point d'autres dieux, vous ne vous prosternerez point devant eux, vous ne les servirez point, et vous ne leur offrirez point de sacrifices;
36 Amma Ubangiji wanda ya fito da ku daga Masar da iko mai girma da hannu mai ƙarfi, shi ne za ku yi masa sujada. Gare shi za ku durƙusa ku kuma miƙa masa hadayu.
mais vous craindrez Yahvé, qui vous a fait monter du pays d'Égypte avec une grande puissance et un bras étendu; vous vous prosternerez devant lui et vous lui offrirez des sacrifices.
37 Dole kullum ku mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da farillan, dokoki da umarnan da ya rubuta muku. Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada.
Les statuts et les ordonnances, la loi et le commandement qu'il a écrits pour vous, vous les mettrez en pratique à jamais. Vous ne craindrez pas d'autres dieux.
38 Kada ku manta da alkawarin da na ƙulla da ku, kada ku yi sujada ga waɗansu alloli.
Vous n'oublierez pas l'alliance que j'ai conclue avec vous. Tu ne craindras pas d'autres dieux.
39 Maimakon haka, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada; shi ne zai cece ku daga hannun abokan gābanku.”
Mais tu craindras Yahvé ton Dieu, et il te délivrera de la main de tous tes ennemis. »
40 Amma ba su saurara ba, suka nace da ayyukansu na dā.
Mais ils n'écoutèrent pas, et ils firent ce qu'ils faisaient auparavant.
41 Ko ma yayinda mutanen nan suke yi wa Ubangiji sujada, ba su daina bauta wa gumakansu ba. Har yă zuwa yau,’ya’yansu da jikokinsu sun ci gaba da bin gurbin kakanninsu.
Ces nations craignaient donc Yahvé et servaient aussi leurs images gravées. Leurs enfants firent de même, et les enfants de leurs enfants aussi. Ils font comme leurs pères jusqu'à ce jour.