< 2 Sarakuna 17 >

1 A shekara ta goma sha biyu ta mulkin Ahaz sarkin Yahuda, Hosheya ɗan Ela ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki na shekara tara.
Elah’s son Hoshea began to rule Israel after King Ahaz had ruled Judah for twelve years. Hoshea ruled in Samaria for nine years.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar na sarakunan Isra’ilan da suka riga shi ba.
He did many things that Yahweh considered to be evil, but he did not do as many evil things as the previous kings of Israel had done.
3 Shalmaneser sarkin Assuriya ya kawo wa Hosheya wanda dā abokin tarayyarsa ne, hari har Hosheya ya biya shi haraji.
[The army of] King Shalmaneser of Assyria attacked and defeated [the army of] King Hoshea. As a result, the Israelis were forced to pay a lot of tribute/taxes to Assyria each year.
4 Amma sarkin Assuriya ya gane cewa Hosheya mai cin amana ne, gama ya aika da wakilai wurin So sarkin Masar, ya kuma daina aika wa sarkin Assuriya haraji yadda ya saba yi kowace shekara. Saboda haka Shalmaneser ya kama shi ya sa a kurkuku.
But several years later, Hoshea secretly planned to rebel against the rulers of Assyria. He sent messengers to So/Osorkon, the king of Egypt, [asking if his army could help the Israelis fight against the army of Assyria]. Hoshea also stopped paying the tribute/taxes that he had been paying to Assyria every year. But the king of Assyria found out about those things, so he told his officers to put Hoshea in prison.
5 Sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar Hosheya gaba ɗaya farmaki, ya kewaye Samariya na tsawon shekara uku.
Then he [brought the army of] Assyria to Israel, and they attacked everywhere in that land. His army surrounded Samaria [city] for three years.
6 A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, sarkin Assuriya ya ci Samariya da yaƙi ya kuma kwashe Isra’ilawa zuwa Assuriya. Ya tsugunar da su a Hala, da a Gozan a bakin Kogin Habor da kuma a garuruwan Medes.
Finally, after King Hoshea had been ruling Israel for nine years, the army of Assyria [MTY] [forcefully entered] the city [and] captured [the people]. They took the Israeli people to Assyria and forced some of them to live in Halah [town]. They forced others to live near the Habor River in Gozan district. They forced others to live in the towns where the Mede people-group lived.
7 Duk wannan ya faru ne saboda Isra’ilawa sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fitar da su daga Masar daga ƙarƙashin ikon Fir’auna sarkin Masar. Sun yi wa waɗansu alloli sujada
Those things happened because the Israeli people had sinned against Yahweh their God. He had rescued their [ancestors] from the power [MTY] of the king of Egypt and brought them [safely] out of Egypt, but later they began to worship other gods.
8 suka kuma bi gurbin al’umman da Ubangiji ya kora a gabansu, da kuma ayyukan da sarakuna Isra’ila suka gabatar.
They imitated the things that the heathen/pagan people-groups did. Those were the groups that Yahweh had expelled as the Israelis occupied their land. The Israeli people also did the evil things that the kings of Israel (introduced/showed to them).
9 Isra’ilawa a ɓoye sun aikata abubuwan da ba daidai ba ga Ubangiji Allahnsu. Tun daga hasumiyoyi har zuwa birane masu katanga, sun gina wa kansu wuraren sujada na tudu a dukan garuruwansu.
The Israeli people also secretly did many things that were not pleasing to Yahweh their God. They built shrines [to worship idols] in all their cities, including small towns and big cities with walls around them.
10 Suka kafa keɓaɓɓun duwatsu da kuma ginshiƙan Ashera a kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
They set up stone pillars [to honor gods], and poles [to worship the goddess] Asherah at the top of every high hill and under every [big] tree.
11 Suka ƙona turare a kan kowane tudu, kamar dai yadda al’umman da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka yi muguntan da ya sa Ubangiji ya yi fushi.
The Israelis burned incense in every place where they worshiped those gods, just like the people-groups who lived there previously had done—the groups that Yahweh had expelled from the land. The Israelis did many wicked things that caused Yahweh to become angry.
12 Suka bauta wa gumaka, ko da yake Ubangiji ya ce, “Ba za ku yi wannan ba.”
Yahweh warned them many times that they should not worship idols, but they did it anyway.
13 Ubangiji ya yi wa Isra’ila da Yahuda kashedi ta bakin dukan annabawansa da kuma masu duba, cewa, “Ku juyo daga mugayen ayyukanku. Ku yi biyayya da umarnai da farillaina, bisa ga dukan Dokar da na dokaci kakanninku su bi, waɗanda na kuma bayar ta wurin bayina, annabawa.”
Yahweh frequently sent his prophets and (seers/those who saw visions from Yahweh) to warn the people of Israel and the people of Judah. The message that Yahweh gave them was, “Turn away from all your evil behavior. Obey my commands and my laws, the laws that I told your ancestors [to obey] and which I told the prophets who served me to tell to you [again].”
14 Amma ba su saurare ni ba don sun kangare kamar kakanninsu, waɗanda ba su amince da Ubangiji Allahnsu ba.
But the Israeli people would not pay attention. They were stubborn [IDM] just like their ancestors were. Just like their ancestors did, they refused to believe in Yahweh their God.
15 Suka yi watsi da farillansa da yarjejjeniyar da ya ƙulla da kakanninsu, da kuma kashedin da ya yi musu. Suka bi gumaka marasa amfani, wannan ya sa su ma kansu suka zama marasa amfani. Suka kwaikwayi sauran ƙasashen da suke kewaye da su, ko da yake Ubangiji ya umarce su cewa, “Kada ku yi rayuwa irin tasu,” suka kuwa yi abin da Ubangiji ya hana su.
They rejected Yahweh’s laws and the agreement that he had made with their ancestors. They ignored Yahweh’s warnings. They worshiped worthless idols and as a result they themselves became worthless. Although Yahweh had commanded them not to imitate the evil behavior of the people-groups that lived near them, they disobeyed that command.
16 Suka wofinta dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu gumakan zubi na siffar’yan maruƙa biyu, da kuma ginshiƙin Ashera. Suka rusuna wa rundunan taurari, suka kuma yi wa Ba’al sujada.
The Israeli people disobeyed all of Yahweh’s commands. They made two metal calves [to worship]. They set up two poles [to worship the goddess] Asherah, and they worshiped [the god] Baal, and the sun, the moon, and the stars.
17 Suka miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ta wuta. Suka yi duba, suka yi sihiri suka kuma ba da kansu ga mugunta a gaban Ubangiji; suka sa ya yi fushi.
They also burned their own sons and daughters to be sacrifices [to those gods]. They went to fortune-tellers and they practiced sorcery. They continually chose [MET] to do [all kinds of] evil things that caused Yahweh to become angry.
18 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi ƙwarai da Isra’ila, ya kuma kawar da su daga gabansa. Kabilar Yahuda kaɗai aka bari,
So, because Yahweh was very angry with the Israeli people, he allowed [their enemies] to take them away [from their country]. Only the people of the tribe of Judah were left [in the land].
19 ko Yahuda ma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba. Sun bi gurbin da Isra’ila ta kawo.
But even the people of Judah did not obey the commands of Yahweh their God. They imitated the evil customs that the Israelis had introduced.
20 Saboda haka Ubangiji ya wofinta mutanen Isra’ila; ya azabtar da su, ya kuma ba da su a hannun masu kwasar ganima, sai da ya shafe su ƙaƙaf daga gabansa.
So Yahweh rejected all the people of Israel and of Judah. He punished them by allowing the armies of other nations to defeat them [and take them away]. He got rid of all of them.
21 Sa’ad da ya ware Isra’ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat sarki a kansu. Yerobowam ya rinjayi Isra’ila daga ƙin Ubangiji, ya sa suka aikata babban zunubi.
Earlier, when Yahweh allowed the people of Israel to separate/break away from the area [MTY] that King David [had estabished], they chose Jeroboam, the son of Nebat, to be their king. Then Jeroboam enticed the people of Israel to stop worshiping Yahweh [and to worship idols instead]. He led them to commit great sins.
22 Isra’ila suka nace cikin dukan zunuban Yerobowam, ba su kuwa rabu da su ba
And the Israeli people continued to do the evil things that Jeroboam introduced. They did not turn away from those sins,
23 har Ubangiji ya kawar da su daga gabansa, kamar yadda ya gargaɗe su ta bakin bayinsa annabawa. Saboda haka aka kwashi mutanen Isra’ila daga ƙasarsu zuwa bauta a Assuriya, har wa yau kuwa suna can.
until finally Yahweh got rid of them. That was just what his prophets had warned would happen. The Israeli people were taken away to the land of Assyria, and they still remain there.
24 Sarkin Assuriya ya kawo mutane daga Babilon, Kuta, Afa, Hamat da Sefarfayim ya zaunar da su a garuruwan Samariya don su maya gurbin Isra’ilawa. Suka mallaki Samariya suka kuma zauna a garuruwansu.
The king of Assyria [ordered his soldiers to] take [groups of] people from Babylon, Cuthah, Avva, Hamath, and Sepharvaim [cities] to [the] Samaria [region], and to resettle them in the towns there, to take the place of the Israelis [who lived there previously]. Those people took control over [the whole] Samaria [region] and lived in the towns there.
25 Sa’ad da suka fara zama a can, ba su bauta wa Ubangiji ba; saboda haka ya aika da zakoki a tsakaninsu suka karkashe waɗansu mutane.
But those people [who came from other countries] did not worship Yahweh when they first arrived in Samaria. So Yahweh sent lions to kill some of them.
26 Sai aka faɗa wa sarkin Assuriya cewa, “Mutanen da ka kwashe ka zaunar a garuruwan Samariya fa ba su san abin da allahn ƙasar yake bukata ba. Saboda haka allahn ƙasar ya tura zakoki a cikinsu, waɗanda suke karkashe su, domin mutanen ba su san abin da yake bukata ba.”
Then those people sent a message to the king of Assyria. They wrote, “We people who have resettled in the towns in Samaria do not know how to worship the God [that the Israelis worshiped] in this land. So he has sent lions among us to kill us, because we have not worshiped him correctly.”
27 Sai sarkin Assuriya ya ba da umarni cewa, “A sami wani daga cikin firistocin da aka kwaso zuwa bauta daga Samariya, yă koma yă zauna a can, yă koya wa mutanen abin da allahn ƙasar yake bukata.”
[When] the king of Assyria [read this letter, he] commanded [his officers], “You brought many priests here from Samaria. Send one of them back there. Tell him to teach the people who are now living there how to worship correctly the God whom the Israelis worshiped in that land.”
28 Saboda haka ɗaya daga cikin firistocin da aka kawo bauta daga Samariya ya dawo ya zauna a Betel, ya koya musu yadda za su yi sujada ga Ubangiji.
So [the officers did that]. They sent one of the Israeli priests back to Samaria. That priest went to live in Bethel [city], and he taught the people there how to worship Yahweh.
29 Duk da haka, jama’ar kowace ƙasa, suka ƙera tasu alloli a garuruwa masu yawa inda suke zaune, suka sa su a masujadan da mutanen Samariya suka gina a kan tuddai.
But the people [who returned from Babylon and started to live in Samaria and] continued to make their own idols. They placed them in the shrines that the Israelis had built there. The people of each people-group made idols in the cities in which they were living.
30 Mutane daga Babilon suka ƙera Sukkot Benot, mutane daga Kut suka ƙera Nergal, mutane daga Hamat suka ƙera Ashima;
The people from Babylon made idols to represent their god Succoth-Benoth. The people from Cuthah made idols to represent their god Nergal. The people from Hamath made idols to represent their god Ashima.
31 Awwiyawa suka ƙera Nibhaz da Tartak, Sefarfayawa kuwa suka ƙone’ya’yansu a wuta a matsayi hadayu ga Adrammelek da Anammelek allolin Sefarfayim.
The people of Avva made idols to represent their gods Nibhaz and Tartak. The people from Sepharvaim sacrificed their own children. They completely burned them [in pits where hot fires were kept burning, ] as offerings to their gods Adrammelech and Anammelech.
32 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka zaɓi mutanensu su yi musu hidima a matsayin firistoci a masujadan da suke kan tuddai.
But those people also worshiped Yahweh, and they appointed from among their own groups many people to be priests at the shrines on the tops of the hills, in order that those priests could offer sacrifices for them there.
33 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma sun bauta wa allolinsu bisa ga al’adun ƙasashen da suka fito.
So they revered Yahweh, but they also worshiped their own gods, just as the people living in the countries from which they had been taken to Samaria did.
34 Har yă zuwa yau, sun nace da ayyukansu na dā. Ba sa yin wa Ubangiji sujada, ba sa kuma bin dokoki da farillansa, dokoki da umarnan da Ubangiji ya ba wa zuriyar Yaƙub, wadda ya ba wa suna Isra’ila.
They still keep their old customs. They really do not worship Yahweh, and they do not obey all the laws and commands that Yahweh gave to the descendants of Jacob, to whom he gave the new name Israel.
35 Da Ubangiji ya ƙulla alkawari da Isra’ilawa, ya dokace su cewa, “Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada ko ku durƙusa a gabansu ku bauta musu, ko ku miƙa musu hadaya.
Yahweh had previously made an agreement with their ancestors, commanding them not to worship other gods or bow down to honor them or do other things to please them or offer sacrifices to them.
36 Amma Ubangiji wanda ya fito da ku daga Masar da iko mai girma da hannu mai ƙarfi, shi ne za ku yi masa sujada. Gare shi za ku durƙusa ku kuma miƙa masa hadayu.
He had said to them, “You must have an awesome respect for me, Yahweh, the one who brought you out of Egypt with my very great power [DOU]. I am the one whom you must bow down to honor, and I am the one to whom you must offer sacrifices.
37 Dole kullum ku mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da farillan, dokoki da umarnan da ya rubuta muku. Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada.
You must always obey the laws and commands that I [told Moses to] write for you. You must not worship other gods.
38 Kada ku manta da alkawarin da na ƙulla da ku, kada ku yi sujada ga waɗansu alloli.
And you must not forget the agreement that I made with your ancestors. You must not revere other gods.
39 Maimakon haka, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada; shi ne zai cece ku daga hannun abokan gābanku.”
Instead, you must revere me, Yahweh, your God. If you do that, I will rescue you from the power [MTY] of all your enemies.”
40 Amma ba su saurara ba, suka nace da ayyukansu na dā.
But the people [from those foreign nations] would not heed what Yahweh said. Instead, they continued to adhere to their old customs.
41 Ko ma yayinda mutanen nan suke yi wa Ubangiji sujada, ba su daina bauta wa gumakansu ba. Har yă zuwa yau,’ya’yansu da jikokinsu sun ci gaba da bin gurbin kakanninsu.
So, they worshiped Yahweh, but they also worshiped their idols. And their descendants still do the same thing.

< 2 Sarakuna 17 >