< 2 Sarakuna 17 >

1 A shekara ta goma sha biyu ta mulkin Ahaz sarkin Yahuda, Hosheya ɗan Ela ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki na shekara tara.
In the twelfth year of Achaz king of Juda, Osee the son of Ela reigned in Samaria over Israel nine years.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar na sarakunan Isra’ilan da suka riga shi ba.
And he did evil before the Lord: but not as the kings of Israel that had been before him.
3 Shalmaneser sarkin Assuriya ya kawo wa Hosheya wanda dā abokin tarayyarsa ne, hari har Hosheya ya biya shi haraji.
Against him came up Salmanasar king of the Assyrians, and Osee became his servant, and paid him tribute.
4 Amma sarkin Assuriya ya gane cewa Hosheya mai cin amana ne, gama ya aika da wakilai wurin So sarkin Masar, ya kuma daina aika wa sarkin Assuriya haraji yadda ya saba yi kowace shekara. Saboda haka Shalmaneser ya kama shi ya sa a kurkuku.
And when the king of the Assyrians found that Osee endeavouring to rebel had sent messengers to Sua the king of Egypt, that he might not pay tribute to the king of the Assyrians, as he had done every year, he besieged him, bound him, and cast him into prison,
5 Sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar Hosheya gaba ɗaya farmaki, ya kewaye Samariya na tsawon shekara uku.
And he went through all the land: and going up to Samaria, he besieged it three years.
6 A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, sarkin Assuriya ya ci Samariya da yaƙi ya kuma kwashe Isra’ilawa zuwa Assuriya. Ya tsugunar da su a Hala, da a Gozan a bakin Kogin Habor da kuma a garuruwan Medes.
And in the ninth year of Osee, the king of the Assyrians took Samaria, and carried Israel away to Assyria: and he placed them in Hala and Habor by the river of Gozan, in the cities of the Medes.
7 Duk wannan ya faru ne saboda Isra’ilawa sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fitar da su daga Masar daga ƙarƙashin ikon Fir’auna sarkin Masar. Sun yi wa waɗansu alloli sujada
For so it was that the children of Israel had sinned against the Lord their God, who brought them out of the land of Egypt, from under the hand of Pharao king of Egypt, and they worshipped strange gods.
8 suka kuma bi gurbin al’umman da Ubangiji ya kora a gabansu, da kuma ayyukan da sarakuna Isra’ila suka gabatar.
And they walked according to the way of the nations which the Lord had destroyed in the sight of the children of Israel and of the kings of Israel: because they had done in like manner.
9 Isra’ilawa a ɓoye sun aikata abubuwan da ba daidai ba ga Ubangiji Allahnsu. Tun daga hasumiyoyi har zuwa birane masu katanga, sun gina wa kansu wuraren sujada na tudu a dukan garuruwansu.
And the children of Israel offended the Lord their God with things that were not right: and built them high places in all their cities from the tower of the watchmen to the fenced city.
10 Suka kafa keɓaɓɓun duwatsu da kuma ginshiƙan Ashera a kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
And they made them statues and groves on every high hill, and under every shady tree:
11 Suka ƙona turare a kan kowane tudu, kamar dai yadda al’umman da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka yi muguntan da ya sa Ubangiji ya yi fushi.
And they burnt incense there upon altars after the manner of the nations which the Lord had removed from their face: and they did wicked things, provoking the Lord.
12 Suka bauta wa gumaka, ko da yake Ubangiji ya ce, “Ba za ku yi wannan ba.”
And they worshipped abominations, concerning which the Lord had commanded them that they should not do this thing.
13 Ubangiji ya yi wa Isra’ila da Yahuda kashedi ta bakin dukan annabawansa da kuma masu duba, cewa, “Ku juyo daga mugayen ayyukanku. Ku yi biyayya da umarnai da farillaina, bisa ga dukan Dokar da na dokaci kakanninku su bi, waɗanda na kuma bayar ta wurin bayina, annabawa.”
And the Lord testified to them in Israel and in Juda by the hand of all the prophets and seers, saying: Return from your wicked ways, and keep my precepts, and ceremonies, according to all the law which I commanded your fathers: and as I have sent to you in the hand of my servants the prophets.
14 Amma ba su saurare ni ba don sun kangare kamar kakanninsu, waɗanda ba su amince da Ubangiji Allahnsu ba.
And they hearkened not, but hardened their necks like to the neck of their fathers, who would not obey the Lord their God.
15 Suka yi watsi da farillansa da yarjejjeniyar da ya ƙulla da kakanninsu, da kuma kashedin da ya yi musu. Suka bi gumaka marasa amfani, wannan ya sa su ma kansu suka zama marasa amfani. Suka kwaikwayi sauran ƙasashen da suke kewaye da su, ko da yake Ubangiji ya umarce su cewa, “Kada ku yi rayuwa irin tasu,” suka kuwa yi abin da Ubangiji ya hana su.
And they rejected his ordinances and the covenant that he made with their fathers, and the testimonies which he testified against them: and they followed vanities, and acted vainly: and they followed the nations that were round about them, concerning which the Lord had commanded them that they should not do as they did.
16 Suka wofinta dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu gumakan zubi na siffar’yan maruƙa biyu, da kuma ginshiƙin Ashera. Suka rusuna wa rundunan taurari, suka kuma yi wa Ba’al sujada.
And they forsook all the precepts of the Lord their God: and made to themselves two molten calves, and groves, and adored all the host of heaven: and they served Baal.
17 Suka miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ta wuta. Suka yi duba, suka yi sihiri suka kuma ba da kansu ga mugunta a gaban Ubangiji; suka sa ya yi fushi.
And consecrated their sons, and their daughters through fire: and they gave themselves to divinations, and soothsayings: and they delivered themselves up to do evil before the Lord, to provoke him.
18 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi ƙwarai da Isra’ila, ya kuma kawar da su daga gabansa. Kabilar Yahuda kaɗai aka bari,
And the Lord was very angry with Israel, and removed them from his sight, and there remained only the tribe of Juda.
19 ko Yahuda ma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba. Sun bi gurbin da Isra’ila ta kawo.
But neither did Juda itself keep the commandments of the Lord their God: but they walked in the errors of Israel, which they had wrought.
20 Saboda haka Ubangiji ya wofinta mutanen Isra’ila; ya azabtar da su, ya kuma ba da su a hannun masu kwasar ganima, sai da ya shafe su ƙaƙaf daga gabansa.
And the Lord cast off all the seed of Israel, and afflicted them and delivered them into the hand of spoilers, till he cast them away from his face:
21 Sa’ad da ya ware Isra’ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat sarki a kansu. Yerobowam ya rinjayi Isra’ila daga ƙin Ubangiji, ya sa suka aikata babban zunubi.
Even from that time, when Israel was rent from the house of David, and made Jeroboam son of Nabat their king: for Jeroboam separated Israel from the Lord, and made them commit a great sin.
22 Isra’ila suka nace cikin dukan zunuban Yerobowam, ba su kuwa rabu da su ba
And the children of Israel walked in all the sins of Jeroboam, which he had done: and they departed not from them,
23 har Ubangiji ya kawar da su daga gabansa, kamar yadda ya gargaɗe su ta bakin bayinsa annabawa. Saboda haka aka kwashi mutanen Isra’ila daga ƙasarsu zuwa bauta a Assuriya, har wa yau kuwa suna can.
Till the Lord removed Israel from his face, as he had spoken in the hand of all his servants the prophets: and Israel was carried away out of their land to Assyria, unto this day.
24 Sarkin Assuriya ya kawo mutane daga Babilon, Kuta, Afa, Hamat da Sefarfayim ya zaunar da su a garuruwan Samariya don su maya gurbin Isra’ilawa. Suka mallaki Samariya suka kuma zauna a garuruwansu.
And the king of the Assyrians brought people from Babylon, and from Cutha, and from Avah, and from Emath, and from Sepharvaim: and placed them in the cities of Samaria instead of the children of Israel: and they possessed Samaria, and dwelt in the cities thereof.
25 Sa’ad da suka fara zama a can, ba su bauta wa Ubangiji ba; saboda haka ya aika da zakoki a tsakaninsu suka karkashe waɗansu mutane.
And when they began to dwell there, they feared not the Lord: and the Lord sent lions among them, which killed them.
26 Sai aka faɗa wa sarkin Assuriya cewa, “Mutanen da ka kwashe ka zaunar a garuruwan Samariya fa ba su san abin da allahn ƙasar yake bukata ba. Saboda haka allahn ƙasar ya tura zakoki a cikinsu, waɗanda suke karkashe su, domin mutanen ba su san abin da yake bukata ba.”
And it was told the king of the Assyrians, and it was said: The nations which thou hast removed, and made to dwell in the cities of Samaria, know not the ordinances of the God of the land: and the Lord hath sent lions among them: and behold they kill them, because they know not the manner of the God of the land.
27 Sai sarkin Assuriya ya ba da umarni cewa, “A sami wani daga cikin firistocin da aka kwaso zuwa bauta daga Samariya, yă koma yă zauna a can, yă koya wa mutanen abin da allahn ƙasar yake bukata.”
And the king of the Assyrians commanded, saying: Carry thither one of the priests whom you brought from thence captive, and let him go, and dwell with them: and let him teach them the ordinances of the God of the land.
28 Saboda haka ɗaya daga cikin firistocin da aka kawo bauta daga Samariya ya dawo ya zauna a Betel, ya koya musu yadda za su yi sujada ga Ubangiji.
So one of the priests who had been carried away captive from Samaria, came and dwelt in Bethel, and taught them how they should worship the Lord.
29 Duk da haka, jama’ar kowace ƙasa, suka ƙera tasu alloli a garuruwa masu yawa inda suke zaune, suka sa su a masujadan da mutanen Samariya suka gina a kan tuddai.
And every nation made gods of their own, and put them in the temples of the high places, which the Samaritans had made, every nation in their cities where they dwelt.
30 Mutane daga Babilon suka ƙera Sukkot Benot, mutane daga Kut suka ƙera Nergal, mutane daga Hamat suka ƙera Ashima;
For the men of Babylon made Sochothbenoth: and the Cuthites made Nergel: and the men of Emath made Asima.
31 Awwiyawa suka ƙera Nibhaz da Tartak, Sefarfayawa kuwa suka ƙone’ya’yansu a wuta a matsayi hadayu ga Adrammelek da Anammelek allolin Sefarfayim.
And the Hevites made Nebahaz and Tharthac. And they that were of Sepharvaim burnt their children in fire, to Adramelech and Anamelech the gods of Sepharvaim.
32 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka zaɓi mutanensu su yi musu hidima a matsayin firistoci a masujadan da suke kan tuddai.
And nevertheless they worshipped the Lord. And they made to themselves, of the lowest of the people, priests of the high places, and they placed them in the temples of the high places.
33 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma sun bauta wa allolinsu bisa ga al’adun ƙasashen da suka fito.
And when they worshipped the Lord, they served also their own gods according to the custom of the nations out of which they were brought to Samaria:
34 Har yă zuwa yau, sun nace da ayyukansu na dā. Ba sa yin wa Ubangiji sujada, ba sa kuma bin dokoki da farillansa, dokoki da umarnan da Ubangiji ya ba wa zuriyar Yaƙub, wadda ya ba wa suna Isra’ila.
Unto this day they followed the old manner: they fear not the Lord, neither do they keep his ceremonies, and judgments, and law, and the commandment, which the Lord commanded the children of Jacob, whom he surnamed Israel:
35 Da Ubangiji ya ƙulla alkawari da Isra’ilawa, ya dokace su cewa, “Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada ko ku durƙusa a gabansu ku bauta musu, ko ku miƙa musu hadaya.
With whom he made a covenant, and charged them, saying: You shall not fear strange gods, nor shall you adore them, nor worship them, nor sacrifice to them.
36 Amma Ubangiji wanda ya fito da ku daga Masar da iko mai girma da hannu mai ƙarfi, shi ne za ku yi masa sujada. Gare shi za ku durƙusa ku kuma miƙa masa hadayu.
But the Lord your God, who brought you out of the land of Egypt with great power, and a stretched out arm, him shall you fear, and him shall you adore, and to him shall you sacrifice.
37 Dole kullum ku mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da farillan, dokoki da umarnan da ya rubuta muku. Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada.
And the ceremonies, and judgments, and law, and the commandment, which he wrote for you, you shall observe to do them always: and you shall not fear strange gods.
38 Kada ku manta da alkawarin da na ƙulla da ku, kada ku yi sujada ga waɗansu alloli.
And the covenant that he made with you, you shall not forget: neither shall ye worship strange gods,
39 Maimakon haka, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada; shi ne zai cece ku daga hannun abokan gābanku.”
But fear the Lord your God, and he shall deliver you out of the hand of all your enemies.
40 Amma ba su saurara ba, suka nace da ayyukansu na dā.
But they did not hearken, but did according to their old custom.
41 Ko ma yayinda mutanen nan suke yi wa Ubangiji sujada, ba su daina bauta wa gumakansu ba. Har yă zuwa yau,’ya’yansu da jikokinsu sun ci gaba da bin gurbin kakanninsu.
So these nations feared the Lord, but nevertheless served also their idols: their children also and grandchildren, as their fathers did, so do they unto this day.

< 2 Sarakuna 17 >