< 2 Sarakuna 17 >

1 A shekara ta goma sha biyu ta mulkin Ahaz sarkin Yahuda, Hosheya ɗan Ela ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki na shekara tara.
Idet tolvte Akas's, Judas Konges, Aar blev Hosea, Elas Søn, Konge i Samaria over Israel i ni Aar.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar na sarakunan Isra’ilan da suka riga shi ba.
Og han gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne, dog ikke som Israels Konger, som vare før ham.
3 Shalmaneser sarkin Assuriya ya kawo wa Hosheya wanda dā abokin tarayyarsa ne, hari har Hosheya ya biya shi haraji.
Salmanasser, Kongen af Assyrien, drog op imod ham; og Hosea blev hans Tjener og gav ham Skænk.
4 Amma sarkin Assuriya ya gane cewa Hosheya mai cin amana ne, gama ya aika da wakilai wurin So sarkin Masar, ya kuma daina aika wa sarkin Assuriya haraji yadda ya saba yi kowace shekara. Saboda haka Shalmaneser ya kama shi ya sa a kurkuku.
Men Kongen af Assyrien saa et Forbund deri, at Hosea havde sendt Bud til So, Kongen af Ægypten, og ikke bragt Skat til Kongen af Assyrien Aar for Aar; da satte Kongen af Assyrien ham fast og lagde ham bunden i et Fængsel.
5 Sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar Hosheya gaba ɗaya farmaki, ya kewaye Samariya na tsawon shekara uku.
Thi Kongen af Assyrien drog op i det ganske Land og drog op til Samaria og belejrede den i tre Aar.
6 A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, sarkin Assuriya ya ci Samariya da yaƙi ya kuma kwashe Isra’ilawa zuwa Assuriya. Ya tsugunar da su a Hala, da a Gozan a bakin Kogin Habor da kuma a garuruwan Medes.
I Hoseas niende Aar indtog Kongen af Assyrien Samaria og førte Israel bort til Assyrien; og han lod dem bo i Hala og i Habor ved Floden Gosan og i Medernes Stæder.
7 Duk wannan ya faru ne saboda Isra’ilawa sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fitar da su daga Masar daga ƙarƙashin ikon Fir’auna sarkin Masar. Sun yi wa waɗansu alloli sujada
Og det skete, fordi Israels Børn havde syndet imod Herren deres Gud, som havde ført dem op af Ægyptens Land, fra at være under Faraos, Kongen af Ægyptens, Magt, og fordi de frygtede andre Guder;
8 suka kuma bi gurbin al’umman da Ubangiji ya kora a gabansu, da kuma ayyukan da sarakuna Isra’ila suka gabatar.
og de vandrede i de Hedningers Skikke, hvilke Herren havde fordrevet for Israels Børns Ansigt, og i dem, som Israels Konger havde indført;
9 Isra’ilawa a ɓoye sun aikata abubuwan da ba daidai ba ga Ubangiji Allahnsu. Tun daga hasumiyoyi har zuwa birane masu katanga, sun gina wa kansu wuraren sujada na tudu a dukan garuruwansu.
og Israels Børn skjulte Ting, som ikke var ret for Herren deres Gud og byggede sig Høje i alle Stæder, fra Vogternes Taarn indtil hver fast Stad;
10 Suka kafa keɓaɓɓun duwatsu da kuma ginshiƙan Ashera a kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
og de oprejste sig Støtter og Astartebilleder paa hver ophøjet Høj og under hvert grønt Træ;
11 Suka ƙona turare a kan kowane tudu, kamar dai yadda al’umman da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka yi muguntan da ya sa Ubangiji ya yi fushi.
og de gjorde Røgelse der paa alle Højene ligesom Hedningerne, hvilke Herren havde bortført fra deres Ansigt, og de gjorde onde Ting til at opirre Herren;
12 Suka bauta wa gumaka, ko da yake Ubangiji ya ce, “Ba za ku yi wannan ba.”
og de tjente de stygge Afguder, om hvilke Herren havde sagt til dem: I skulle ikke gøre denne Ting;
13 Ubangiji ya yi wa Isra’ila da Yahuda kashedi ta bakin dukan annabawansa da kuma masu duba, cewa, “Ku juyo daga mugayen ayyukanku. Ku yi biyayya da umarnai da farillaina, bisa ga dukan Dokar da na dokaci kakanninku su bi, waɗanda na kuma bayar ta wurin bayina, annabawa.”
og Herren lod vidne i Israel og i Juda ved alle sine Profeter, alle Seere, sigende: Vender om fra eders onde Veje og holder mine Bud, mine Skikke, efter den hele Lov, som jeg bød eders Fædre, og efter det, som jeg sendte til eder om ved mine Tjenere, Profeterne;
14 Amma ba su saurare ni ba don sun kangare kamar kakanninsu, waɗanda ba su amince da Ubangiji Allahnsu ba.
men de havde ikke været lydige, men de forhærdede deres Nakke, ligesom deres Fædres Nakke, de, som ikke troede paa Herren deres Gud;
15 Suka yi watsi da farillansa da yarjejjeniyar da ya ƙulla da kakanninsu, da kuma kashedin da ya yi musu. Suka bi gumaka marasa amfani, wannan ya sa su ma kansu suka zama marasa amfani. Suka kwaikwayi sauran ƙasashen da suke kewaye da su, ko da yake Ubangiji ya umarce su cewa, “Kada ku yi rayuwa irin tasu,” suka kuwa yi abin da Ubangiji ya hana su.
tilmed forkastede de hans Skikke og hans Pagt, som han havde gjort med deres Fædre, og hans Vidnesbyrd, som han havde vidnet for dem, og de vandrede efter Forfængelighed og bleve forfængelige, og efter Hedningerne, der vare trindt omkring dem, om hvilke Herren havde budet dem, at de ikke skulde gøre som de;
16 Suka wofinta dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu gumakan zubi na siffar’yan maruƙa biyu, da kuma ginshiƙin Ashera. Suka rusuna wa rundunan taurari, suka kuma yi wa Ba’al sujada.
ja de forlode alle Herren deres Guds Bud og gjorde sig støbte Billeder, to Kalve, og de gjorde Astartebilleder og tilbade al Himmelens Hær og tjente Baal;
17 Suka miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ta wuta. Suka yi duba, suka yi sihiri suka kuma ba da kansu ga mugunta a gaban Ubangiji; suka sa ya yi fushi.
og de lode deres Sønner og deres Døtre gaa igennem Ilden og omgikkes med Spaadom og agtede paa Fugleskrig og solgte sig til at gøre det, som var ondt for Herrens Øjne, for at opirre ham: —
18 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi ƙwarai da Isra’ila, ya kuma kawar da su daga gabansa. Kabilar Yahuda kaɗai aka bari,
derfor blev Herren saare vred paa Israel og bortdrev dem fra sit Ansigt; der blev ingen tilovers uden Judas Stamme alene.
19 ko Yahuda ma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba. Sun bi gurbin da Isra’ila ta kawo.
Heller ikke Juda holdt Herrens, deres Guds, Bud; men de vandrede efter Israels Skikke, som de havde indført.
20 Saboda haka Ubangiji ya wofinta mutanen Isra’ila; ya azabtar da su, ya kuma ba da su a hannun masu kwasar ganima, sai da ya shafe su ƙaƙaf daga gabansa.
Saa forkastede Herren al Israels Sæd og plagede dem og gav dem i Røveres Hænder, indtil han havde bortstødt dem fra sit Ansigt.
21 Sa’ad da ya ware Isra’ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat sarki a kansu. Yerobowam ya rinjayi Isra’ila daga ƙin Ubangiji, ya sa suka aikata babban zunubi.
Thi Israel havde revet sig løs fra Davids Hus, og de gjorde Jeroboam, Nebats Søn, til Konge; og Jeroboam drog Israel bort fra Herren og kom dem til at synde en stor Synd.
22 Isra’ila suka nace cikin dukan zunuban Yerobowam, ba su kuwa rabu da su ba
Og Israels Børn vandrede i alle Jeroboams Synder, som han gjorde; de vege ikke derfra,
23 har Ubangiji ya kawar da su daga gabansa, kamar yadda ya gargaɗe su ta bakin bayinsa annabawa. Saboda haka aka kwashi mutanen Isra’ila daga ƙasarsu zuwa bauta a Assuriya, har wa yau kuwa suna can.
indtil Herren bortdrev Israel fra sit Ansigt, saaledes som han havde sagt ved alle sine Tjenere, Profeterne; saa blev Israel bortført fra sit Land til Assyrien indtil denne Dag.
24 Sarkin Assuriya ya kawo mutane daga Babilon, Kuta, Afa, Hamat da Sefarfayim ya zaunar da su a garuruwan Samariya don su maya gurbin Isra’ilawa. Suka mallaki Samariya suka kuma zauna a garuruwansu.
Og Kongen af Assyrien lod komme Folk af Babel og af Kut og af Ava og af Hamath og Sefarvajm og lod dem bo i Samarias Stæder, i Israels Børns Sted, og de indtoge Samaria til Ejendom og boede i dens Stæder.
25 Sa’ad da suka fara zama a can, ba su bauta wa Ubangiji ba; saboda haka ya aika da zakoki a tsakaninsu suka karkashe waɗansu mutane.
Og det skete, der de begyndte at bo der, at de ikke frygtede Herren; da sendte Herren Løver iblandt dem, og disse sønderreve nogle af dem.
26 Sai aka faɗa wa sarkin Assuriya cewa, “Mutanen da ka kwashe ka zaunar a garuruwan Samariya fa ba su san abin da allahn ƙasar yake bukata ba. Saboda haka allahn ƙasar ya tura zakoki a cikinsu, waɗanda suke karkashe su, domin mutanen ba su san abin da yake bukata ba.”
Derfor sagde de til Kongen af Assyrien: De Hedninger, som du lod forflytte og bo i Samarias Stæder, kende ikke, hvad der er ret imod Landets Gud; derfor sendte han Løver iblandt dem, og se, disse sønderreve dem, fordi de ikke kende, hvad der er ret imod Landets Gud.
27 Sai sarkin Assuriya ya ba da umarni cewa, “A sami wani daga cikin firistocin da aka kwaso zuwa bauta daga Samariya, yă koma yă zauna a can, yă koya wa mutanen abin da allahn ƙasar yake bukata.”
Da bød Kongen af Assyrien og sagde: Fører en af de Præster derhen, som I bortførte derfra, og lader ham drage hen og bo der, at han kan lære dem, hvad der er ret imod Landets Gud.
28 Saboda haka ɗaya daga cikin firistocin da aka kawo bauta daga Samariya ya dawo ya zauna a Betel, ya koya musu yadda za su yi sujada ga Ubangiji.
Saa kom en af Præsterne, som de havde bortført fra Samaria, og boede i Bethel og lærte dem, hvorledes de skulde frygte Herren.
29 Duk da haka, jama’ar kowace ƙasa, suka ƙera tasu alloli a garuruwa masu yawa inda suke zaune, suka sa su a masujadan da mutanen Samariya suka gina a kan tuddai.
Men hvert Folk gjorde sig sin Gud, og de satte dem i Husene paa de Høje, som Samaritanerne gjorde, hvert Folk i sine Stæder, hvori de boede.
30 Mutane daga Babilon suka ƙera Sukkot Benot, mutane daga Kut suka ƙera Nergal, mutane daga Hamat suka ƙera Ashima;
Thi de Mænd af Babel havde gjort Sukoth-Benoth, og de Mænd af Kut havde gjort Nergal, og de Mænd af Hamath havde gjort Asima,
31 Awwiyawa suka ƙera Nibhaz da Tartak, Sefarfayawa kuwa suka ƙone’ya’yansu a wuta a matsayi hadayu ga Adrammelek da Anammelek allolin Sefarfayim.
og de al Ava havde gjort Nibhas og Tharthak, og de af Sefarvajm opbrændte deres Sønner i Ilden for Adramelek og Anamelek, Sefarvajms Guder.
32 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka zaɓi mutanensu su yi musu hidima a matsayin firistoci a masujadan da suke kan tuddai.
De frygtede ogsaa Herren og gjorde sig i Flæng Præster paa Højene og gjorde Offer for dem i Husene paa Højene.
33 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma sun bauta wa allolinsu bisa ga al’adun ƙasashen da suka fito.
De frygtede Herren, og de tjente deres Guder efter de Hedningers Vis, som de vare bortførte fra.
34 Har yă zuwa yau, sun nace da ayyukansu na dā. Ba sa yin wa Ubangiji sujada, ba sa kuma bin dokoki da farillansa, dokoki da umarnan da Ubangiji ya ba wa zuriyar Yaƙub, wadda ya ba wa suna Isra’ila.
De gøre efter den første Vis, indtil denne Dag; de frygte ikke Herren, ej heller gøre de efter deres Skikke og efter deres Befalinger og efter Loven og efter Budet, som Herren bød Jakobs Børn, hvis Navn han kaldte Israel;
35 Da Ubangiji ya ƙulla alkawari da Isra’ilawa, ya dokace su cewa, “Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada ko ku durƙusa a gabansu ku bauta musu, ko ku miƙa musu hadaya.
og Herren gjorde en Pagt med dem og bød dem, sigende: I skulle ikke frygte andre Guder og ikke tilbede dem og ikke tjene dem og ikke ofre til dem.
36 Amma Ubangiji wanda ya fito da ku daga Masar da iko mai girma da hannu mai ƙarfi, shi ne za ku yi masa sujada. Gare shi za ku durƙusa ku kuma miƙa masa hadayu.
Men Herren, som førte eder op af Ægyptens Land med stor Kraft og med en udrakt Arm, ham skulle I frygte, og ham skulle I tilbede og ofre til.
37 Dole kullum ku mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da farillan, dokoki da umarnan da ya rubuta muku. Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada.
Og I skulle holde de Skikke og Befalinger og Loven og Budet, som han lod skrive for eder, at gøre derefter alle Dage; men I skulle ikke frygte andre Guder.
38 Kada ku manta da alkawarin da na ƙulla da ku, kada ku yi sujada ga waɗansu alloli.
Og I skulle ikke forglemme den Pagt, som jeg gjorde med eder, og ikke frygte andre Guder.
39 Maimakon haka, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada; shi ne zai cece ku daga hannun abokan gābanku.”
Men I skulle frygte Herren eders Gud, og han skal fri eder fra alle eders Fjenders Haand.
40 Amma ba su saurara ba, suka nace da ayyukansu na dā.
Dog, de hørte ikke; men de gjorde efter deres første Vis.
41 Ko ma yayinda mutanen nan suke yi wa Ubangiji sujada, ba su daina bauta wa gumakansu ba. Har yă zuwa yau,’ya’yansu da jikokinsu sun ci gaba da bin gurbin kakanninsu.
Saa frygtede disse Hedninger Herren og tjente deres Billeder; ogsaa deres Børn og deres Børnebørn, efter som deres Fædre gjorde, saa gøre de indtil denne Dag.

< 2 Sarakuna 17 >