< 2 Sarakuna 17 >
1 A shekara ta goma sha biyu ta mulkin Ahaz sarkin Yahuda, Hosheya ɗan Ela ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki na shekara tara.
Léta dvanáctého Achasa krále Judského kraloval Ozee syn Ela v Samaří nad Izraelem devět let.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar na sarakunan Isra’ilan da suka riga shi ba.
A činil to, což jest zlého před očima Hospodinovýma, ač ne tak jako jiní králové Izraelští, kteříž byli před ním.
3 Shalmaneser sarkin Assuriya ya kawo wa Hosheya wanda dā abokin tarayyarsa ne, hari har Hosheya ya biya shi haraji.
Proti němuž přitáhl Salmanazar král Assyrský. I učiněn jest Ozee služebníkem jeho, a dával mu plat.
4 Amma sarkin Assuriya ya gane cewa Hosheya mai cin amana ne, gama ya aika da wakilai wurin So sarkin Masar, ya kuma daina aika wa sarkin Assuriya haraji yadda ya saba yi kowace shekara. Saboda haka Shalmaneser ya kama shi ya sa a kurkuku.
Shledal pak král Assyrský při Ozee puntování; nebo poslal posly k Sua králi Egyptskému, a neposílal králi Assyrskému ročního platu. Protož oblehl ho král Assyrský, a svázaného dal do žaláře.
5 Sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar Hosheya gaba ɗaya farmaki, ya kewaye Samariya na tsawon shekara uku.
I táhl král Assyrský po vší zemi; přitáhl také do Samaří, a ležel u ní tři léta.
6 A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, sarkin Assuriya ya ci Samariya da yaƙi ya kuma kwashe Isra’ilawa zuwa Assuriya. Ya tsugunar da su a Hala, da a Gozan a bakin Kogin Habor da kuma a garuruwan Medes.
Léta pak devátého Ozee vzal král Assyrský Samaří, a přenesl Izraele do Assyrie, a osadil je v Chelach a v Chabor při řece Gozan, a v městech Médských.
7 Duk wannan ya faru ne saboda Isra’ilawa sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fitar da su daga Masar daga ƙarƙashin ikon Fir’auna sarkin Masar. Sun yi wa waɗansu alloli sujada
To se stalo, proto že hřešili synové Izraelští proti Hospodinu Bohu svému, kterýž je vyvedl z země Egyptské, aby nebyli pod mocí Faraona krále Egyptského, a ctili bohy cizí,
8 suka kuma bi gurbin al’umman da Ubangiji ya kora a gabansu, da kuma ayyukan da sarakuna Isra’ila suka gabatar.
Chodíce v ustanoveních pohanů, (kteréž byl vyvrhl Hospodin od tváři synů Izraelských), a králů Izraelských, kteráž nařídili.
9 Isra’ilawa a ɓoye sun aikata abubuwan da ba daidai ba ga Ubangiji Allahnsu. Tun daga hasumiyoyi har zuwa birane masu katanga, sun gina wa kansu wuraren sujada na tudu a dukan garuruwansu.
Přesto pokrytě se měli synové Izraelští, činíce to, což není dobrého před Hospodinem Bohem svým, a vzdělali sobě výsosti ve všech městech svých, od věže strážných až do města hrazeného.
10 Suka kafa keɓaɓɓun duwatsu da kuma ginshiƙan Ashera a kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
A nastavěli sobě obrazů i hájů na všelikém pahrbku vysokém, a pod každým stromem zeleným,
11 Suka ƙona turare a kan kowane tudu, kamar dai yadda al’umman da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka yi muguntan da ya sa Ubangiji ya yi fushi.
Zapalujíce tam vonné věci na všech výsostech, rovně jako pohané, kteréž vyhnal Hospodin od tváři jejich. A činili věci nejhorší, popouzejíce Hospodina.
12 Suka bauta wa gumaka, ko da yake Ubangiji ya ce, “Ba za ku yi wannan ba.”
A sloužili bohům nečistým, o nichž byl Hospodin řekl jim, aby nečinili toho.
13 Ubangiji ya yi wa Isra’ila da Yahuda kashedi ta bakin dukan annabawansa da kuma masu duba, cewa, “Ku juyo daga mugayen ayyukanku. Ku yi biyayya da umarnai da farillaina, bisa ga dukan Dokar da na dokaci kakanninku su bi, waɗanda na kuma bayar ta wurin bayina, annabawa.”
I osvědčoval Hospodin proti Izraelovi a proti Judovi skrze všecky proroky i všecky vidoucí, řka: Odvraťte se od cest svých zlých, a ostříhejte přikázaní mých a ustanovení mých vedlé všeho zákona, kterýž jsem vydal otcům vašim, a kterýž jsem poslal k vám skrze služebníky své proroky.
14 Amma ba su saurare ni ba don sun kangare kamar kakanninsu, waɗanda ba su amince da Ubangiji Allahnsu ba.
Však neposlechli, ale zatvrdili šíji svou, jako i otcové jejich šíje své, kteříž nevěřili v Hospodina Boha svého.
15 Suka yi watsi da farillansa da yarjejjeniyar da ya ƙulla da kakanninsu, da kuma kashedin da ya yi musu. Suka bi gumaka marasa amfani, wannan ya sa su ma kansu suka zama marasa amfani. Suka kwaikwayi sauran ƙasashen da suke kewaye da su, ko da yake Ubangiji ya umarce su cewa, “Kada ku yi rayuwa irin tasu,” suka kuwa yi abin da Ubangiji ya hana su.
A opovrhli ustanovení jeho i smlouvu jeho, kterouž učinil s otci jejich, i osvědčování jeho, kterýmiž se jim osvědčoval, a odešli po marnosti, a marní učiněni jsou, následujíce pohanů, kteříž byli vůkol nich, o nichž jim byl přikázal Hospodin, aby nečinili jako oni.
16 Suka wofinta dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu gumakan zubi na siffar’yan maruƙa biyu, da kuma ginshiƙin Ashera. Suka rusuna wa rundunan taurari, suka kuma yi wa Ba’al sujada.
A opustivše všecka přikázaní Hospodina Boha svého, udělali sobě slitinu, dvé telat a háj, a klaněli se všemu vojsku nebeskému; sloužili také Bálovi.
17 Suka miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ta wuta. Suka yi duba, suka yi sihiri suka kuma ba da kansu ga mugunta a gaban Ubangiji; suka sa ya yi fushi.
A vodili syny své a dcery své skrze oheň, a obírali se s hádáním a kouzly, a tak vydali se v činění toho, což jest zlé před očima Hospodinovýma, popouzejíce ho.
18 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi ƙwarai da Isra’ila, ya kuma kawar da su daga gabansa. Kabilar Yahuda kaɗai aka bari,
Protož rozhněval se Hospodin náramně na Izraele, a zahnal je od tváři své, nezanechav z nich nic, kromě samého pokolení Judova.
19 ko Yahuda ma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba. Sun bi gurbin da Isra’ila ta kawo.
Ano i Juda neostříhal přikázaní Hospodina Boha svého, ale chodili v ustanoveních Izraelských, kteráž byli nařídili.
20 Saboda haka Ubangiji ya wofinta mutanen Isra’ila; ya azabtar da su, ya kuma ba da su a hannun masu kwasar ganima, sai da ya shafe su ƙaƙaf daga gabansa.
A protož opovrhl Hospodin všecko símě Izraelské a ssužoval je, a vydal je v ruku loupežníků, až je i zavrhl od tváři své.
21 Sa’ad da ya ware Isra’ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat sarki a kansu. Yerobowam ya rinjayi Isra’ila daga ƙin Ubangiji, ya sa suka aikata babban zunubi.
Nebo odtrhl Izraele od domu Davidova, a krále ustanovili Jeroboáma syna Nebatova, Jeroboám pak odvrátil Izraele od následování Hospodina, a přivedl je k hřešení hříchem velikým.
22 Isra’ila suka nace cikin dukan zunuban Yerobowam, ba su kuwa rabu da su ba
A chodili synové Izraelští ve všech hříších Jeroboámových, kteréž on činil, a neodstoupili od nich,
23 har Ubangiji ya kawar da su daga gabansa, kamar yadda ya gargaɗe su ta bakin bayinsa annabawa. Saboda haka aka kwashi mutanen Isra’ila daga ƙasarsu zuwa bauta a Assuriya, har wa yau kuwa suna can.
Až zavrhl Hospodin Izraele od tváři své, jakož byl mluvil skrze všecky služebníky své proroky. I vyhnán jest Izrael z země své do Assyrie až do tohoto dne.
24 Sarkin Assuriya ya kawo mutane daga Babilon, Kuta, Afa, Hamat da Sefarfayim ya zaunar da su a garuruwan Samariya don su maya gurbin Isra’ilawa. Suka mallaki Samariya suka kuma zauna a garuruwansu.
Potom král Assyrský přivedl lidi z Babylona, a z Kut a z Ava, a z Emat a z Sefarvaim, a osadil je v městech Samařských místo synů Izraelských, kteříž opanovavše Samaří, bydlili v městech jejich.
25 Sa’ad da suka fara zama a can, ba su bauta wa Ubangiji ba; saboda haka ya aika da zakoki a tsakaninsu suka karkashe waɗansu mutane.
I stalo se, když tam bydliti počali, a nesloužili Hospodinu, že poslal na ně Hospodin lvy, kteříž je dávili.
26 Sai aka faɗa wa sarkin Assuriya cewa, “Mutanen da ka kwashe ka zaunar a garuruwan Samariya fa ba su san abin da allahn ƙasar yake bukata ba. Saboda haka allahn ƙasar ya tura zakoki a cikinsu, waɗanda suke karkashe su, domin mutanen ba su san abin da yake bukata ba.”
Protož mluvili králi Assyrskému, řkouce: Národové ti, kteréž jsi přenesl a osadil v městech Samařských, neznají obyčeje Boha země té; protož poslal na ně lvy, kteříž je hubí, proto že neznají obyčeje Boha země té.
27 Sai sarkin Assuriya ya ba da umarni cewa, “A sami wani daga cikin firistocin da aka kwaso zuwa bauta daga Samariya, yă koma yă zauna a can, yă koya wa mutanen abin da allahn ƙasar yake bukata.”
I přikázal král Assyrský, řka: Doveďte tam jednoho z těch kněží, kteréž jste odtud přivedli, a odejdouce, nechť tam bydlí, a učí je obyčeji Boha země té.
28 Saboda haka ɗaya daga cikin firistocin da aka kawo bauta daga Samariya ya dawo ya zauna a Betel, ya koya musu yadda za su yi sujada ga Ubangiji.
Přišel tedy jeden z kněží, kteréž byli přivedli z Samaří, a bydlil v Bethel, a učil je, jak by měli sloužiti Hospodinu.
29 Duk da haka, jama’ar kowace ƙasa, suka ƙera tasu alloli a garuruwa masu yawa inda suke zaune, suka sa su a masujadan da mutanen Samariya suka gina a kan tuddai.
A však nadělali sobě jeden každý národ bohů svých, kteréž stavěli v domě výsostí, jichž byli nadělali Samařští, jeden každý národ v městech svých, v nichž bydlili.
30 Mutane daga Babilon suka ƙera Sukkot Benot, mutane daga Kut suka ƙera Nergal, mutane daga Hamat suka ƙera Ashima;
Muži zajisté Babylonští udělali Sukkot Benot, muži pak Kutští udělali Nergale, a muži Ematští udělali Asima.
31 Awwiyawa suka ƙera Nibhaz da Tartak, Sefarfayawa kuwa suka ƙone’ya’yansu a wuta a matsayi hadayu ga Adrammelek da Anammelek allolin Sefarfayim.
Hevejští tolikéž udělali Nibchaz a Tartak, a Sefarvaimští pálili syny své ohněm Adramelechovi a Anamelechovi, bohům Sefarvaimským.
32 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka zaɓi mutanensu su yi musu hidima a matsayin firistoci a masujadan da suke kan tuddai.
A tak sloužili Hospodinu, nadělavše sobě z počtu svého kněží výsostí, kteříž přisluhovali jim v domích výsostí.
33 Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma sun bauta wa allolinsu bisa ga al’adun ƙasashen da suka fito.
Hospodina ctili, však předce bohům svým sloužili vedlé obyčeje těch národů, odkudž převedeni byli.
34 Har yă zuwa yau, sun nace da ayyukansu na dā. Ba sa yin wa Ubangiji sujada, ba sa kuma bin dokoki da farillansa, dokoki da umarnan da Ubangiji ya ba wa zuriyar Yaƙub, wadda ya ba wa suna Isra’ila.
A do dnes činí vedlé obyčejů starých; nebojí se Hospodina, a nečiní vedlé ustanovení a úsudků jeho, ani vedlé zákona a přikázaní, kteráž vydal Hospodin synům Jákobovým, jehož nazval Izraelem.
35 Da Ubangiji ya ƙulla alkawari da Isra’ilawa, ya dokace su cewa, “Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada ko ku durƙusa a gabansu ku bauta musu, ko ku miƙa musu hadaya.
Učinil také byl Hospodin s nimi smlouvu, a přikázal jim, řka: Nebudete ctíti bohů cizích, ani se jim klaněti, ani jim sloužiti, ani jim obětovati.
36 Amma Ubangiji wanda ya fito da ku daga Masar da iko mai girma da hannu mai ƙarfi, shi ne za ku yi masa sujada. Gare shi za ku durƙusa ku kuma miƙa masa hadayu.
Ale Hospodina, kterýž vás vyvedl z země Egyptské v síle veliké a v rameni vztaženém, toho ctíti budete, a jemu se klaněti, a jemu obětovati.
37 Dole kullum ku mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da farillan, dokoki da umarnan da ya rubuta muku. Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada.
Také ustanovení a úsudků, i zákona a přikázaní, kteráž napsal vám, ostříhati budete, plníce je po všecky dny, a nebudete ctíti bohů cizích.
38 Kada ku manta da alkawarin da na ƙulla da ku, kada ku yi sujada ga waɗansu alloli.
Nadto na smlouvu, kterouž jsem učinil s vámi, nezapomínejte, aniž ctěte bohů cizích.
39 Maimakon haka, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada; shi ne zai cece ku daga hannun abokan gābanku.”
Ale Hospodina Boha vašeho se bojte; onť vás vysvobodí z ruky všech nepřátel vašich.
40 Amma ba su saurara ba, suka nace da ayyukansu na dā.
A však neposlechli, ale vedlé obyčeje svého starého činili.
41 Ko ma yayinda mutanen nan suke yi wa Ubangiji sujada, ba su daina bauta wa gumakansu ba. Har yă zuwa yau,’ya’yansu da jikokinsu sun ci gaba da bin gurbin kakanninsu.
A tak ti národové ctili Hospodina, a však proto rytinám svým sloužili. Takž i synové jejich a synové synů jejich vedlé toho, což činili otcové jejich, také činí až do dnešního dne.