< 2 Sarakuna 16 >

1 A shekara ta goma sha bakwai ta mulkin Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda ya fara mulki.
Ngomnyaka wetshumi lesikhombisa kaPheka indodana kaRemaliya uAhazi indodana kaJothamu inkosi yakoJuda waba yinkosi.
2 Ahaz ya zama sarki yana da shekara ashirin, ya kuma yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima ba kamar Dawuda mahaifinsa ba. Ahaz bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa ba.
UAhazi wayeleminyaka engamatshumi amabili lapho esiba yinkosi; wabusa iminyaka elitshumi lesithupha eJerusalema. Kenzanga-ke okulungileyo emehlweni eNkosi uNkulunkulu wakhe, njengoDavida uyise.
3 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila har ya miƙa ɗansa hadaya a wuta, yana bin hanyoyin banƙyama na al’ummai da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Kodwa wahamba ngendlela yamakhosi akoIsrayeli, yebo, futhi wenza indodana yakhe idabule emlilweni, njengezinengiso zezizwe iNkosi eyazixotsha elifeni phambi kwabantwana bakoIsrayeli.
4 Ya miƙa hadaya, ya kuma ƙona turare a masujadan tudu, da kan tuddai, da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
Wanikela imihlatshelo watshisa impepha endaweni eziphakemeyo laphezu kwamaqaqa langaphansi kwaso sonke isihlahla esiluhlaza.
5 Sai Rezin sarkin Aram, da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su kai wa Urushalima hari, suka kuma kewaye Ahaz, amma ba su iya shan ƙarfinsa ba.
Khona uRezini inkosi yeSiriya loPheka indodana kaRemaliya, inkosi yakoIsrayeli, benyukela eJerusalema ukulwa, bamvimbezela uAhazi kodwa kababanga lakho ukunqoba.
6 A wannan lokaci, Rezin sarkin Aram ya sāke ƙwato Elat wa Aram ta wurin korar Yahuda. Sa’an nan mutanen Edom suka mamaye Elat suna kuwa zaune a can har yau.
Ngalesosikhathi uRezini inkosi yeSiriya wabuyisela iElathi eSiriya, waxotsha amaJuda eElathi; amaSiriya asesiza eElathi ahlala khona kuze kube lamuhla.
7 Ahaz ya aika a faɗa wa Tiglat-Fileser sarkin Assuriya cewa, “Ni abokin tarayyarka ne kuma mai dogara da kai. Ka haura ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra’ila waɗanda suke kawo mini hari.”
UAhazi wasethuma izithunywa kuTigilathi Pileseri inkosi yeAsiriya esithi: Ngiyinceku yakho lendodana yakho; yenyuka ungisindise esandleni senkosi yeSiriya lesandleni senkosi yakoIsrayeli abangivukelayo.
8 Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyar da suke a haikalin Ubangiji da suke kuma a ma’ajin fada ya aika wa sarkin Assuriya kyauta.
UAhazi wasethatha isiliva legolide okwakutholwa endlini kaJehova lenothweni yendlu yenkosi, wathumela isipho enkosini yeAsiriya.
9 Sai sarkin Assuriya ya ji roƙonsa. Ya tashi ya fāɗa wa Damaskus da hari ya kuma kame ta. Ya kwashi mazaunanta zuwa Kir, ya kuma kashe Rezin.
Inkosi yeAsiriya yasimlalela, ngoba inkosi yeAsiriya yenyuka imelene leDamaseko yayithumba, yabathumbela eKiri abantu bayo, yabulala uRezini.
10 Sa’an nan sarki Ahaz ya tafi Damaskus don yă sadu da Tiglat-Fileser sarkin Assuriya. Da ya kai can sai ya ga wani bagade a Damaskus, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayanin bagaden.
Inkosi uAhazi yasisiya eDamaseko ukuhlangana loTigilathi Pileseri inkosi yeAsiriya, yabona ilathi elaliseDamaseko. Inkosi uAhazi yasithumela kuUriya umpristi isimo selathi lomfanekiso walo njengokwenziwa kwalo konke.
11 Saboda haka Uriya firist ya gina bagaden bisa ga tsarin da Sarki Ahaz ya aika masa daga Damaskus, ya kuma gama shi kafin Sarki Ahaz yă dawo.
U-Uriya umpristi wasesakha ilathi njengakho konke uAhazi akuthumela kuvela eDamaseko; uUriya umpristi wenza njalo, yaze yafika inkosi uAhazi ivela eDamaseko.
12 Da sarki ya dawo daga Damaskus ya ga bagaden, sai ya tafi kusa da shi ya kuma miƙa hadaya a bisansa.
Inkosi isibuyile eDamaseko inkosi yalibona ilathi. Inkosi yasondela elathini, yanikela phezu kwalo.
13 Ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa da ta hatsi, ya zuba hadayarsa ta sha, ya kuma yayyafa jinin hadayunsa ta zumunci a bisa bagaden.
Yasitshisa umnikelo wayo wokutshiswa lomnikelo wayo wokudla, yathela umnikelo wayo wokunathwayo, yafafaza igazi leminikelo yokuthula eyayilayo phezu kwelathi.
14 Sai ya cire bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi a gaban haikalin wato, tsakanin ƙofar shiga haikalin Ubangiji da sabon bagaden. Ya ajiye shi a gefen arewa na sabon bagaden.
Kodwa ilathi lethusi elaliphambi kweNkosi yaliletha lisuka phambi kwendlu, lisuka phakathi kwelathi lendlu yeNkosi, yalifaka ehlangothini lwenyakatho lwelathi.
15 Sarkin Ahaz ya umarci Uriya cewa, “A kan babban sabon bagade, ka miƙa hadayar ƙonawa ta safe, da hadayar hatsi ta yamma, da hadayar sarki ta ƙonawa da hadayarsa ta hatsi, da hadaya ta dukan jama’ar ƙasar, tare da hadayan hatsinsu da kuma ta sha. Ka yayyafa jinin hadayun ƙonawa a kan bagade. Amma zan yi amfani da bagaden tagulla don neman bishewa.”
Inkosi uAhazi yasimlaya uUriya umpristi isithi: Phezu kwelathi elikhulu tshisa umnikelo wokutshiswa wekuseni, lomnikelo wokudla wantambama, lomnikelo wokutshiswa wenkosi, lomnikelo wayo wokudla, lomnikelo wokutshiswa wabo bonke abantu belizwe, lomnikelo wabo wokudla, leminikelo yabo yokunathwayo; ufafaze phezu kwalo lonke igazi lomnikelo wokutshiswa lalo lonke igazi lomhlatshelo. Kodwa ilathi lethusi lizakuba ngelami ukubuza ngalo.
16 Uriya firist kuwa ya yi duk abin da Sarki Ahaz ya umarta.
U-Uriya umpristi wasesenza njengakho konke inkosi uAhazi eyayikulayile.
17 Sarkin Ahaz ya kawar da katakon ya kuma ɗauke tasoshin daga mazauninsu da ake iya matsarwa. Ya ɗauke ƙaton kwano mai suna Teku daga kan bijiman tagullar da ya tallafe su ya ajiye a kan mazaunin dutse.
Inkosi uAhazi yasiquma imiphetho yezisekelo, yasusa inditshi yokugezela kuzo, yethula ulwandle phezu kwenkabi zethusi ezazingaphansi kwalo, yalubeka phezu kokugandelwe ngamatshe.
18 Ya kawar da rumfa Asabbacin da aka gina a haikalin, ya kuma kawar da mashigin sarki na waje da haikalin Ubangiji, duk dai don yă gamshi sarkin Assuriya.
Lokwembesiweyo kwesabatha ababekwakhe endlini, lentuba yenkosi phandle, yakususa endlini yeNkosi, ngenxa yenkosi yeAsiriya.
19 Game da sauran ayyukan mulkin Ahaz, abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Ezinye-ke zezindaba zikaAhazi azenzayo, kazibhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoJuda?
20 Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi da su a Birnin Dawuda. Hezekiya ɗansa kuma ya gāje shi.
UAhazi waselala laboyise, wangcwatshelwa kuboyise emzini kaDavida. UHezekhiya indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.

< 2 Sarakuna 16 >