< 2 Sarakuna 16 >

1 A shekara ta goma sha bakwai ta mulkin Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda ya fara mulki.
La dix-septième année de Pékach fils de Rémalia, Achaz fils de Jotham Roi de Juda, commença à régner.
2 Ahaz ya zama sarki yana da shekara ashirin, ya kuma yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima ba kamar Dawuda mahaifinsa ba. Ahaz bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa ba.
Achaz était âgé de vingt ans quand il commença à régner; et il régna seize ans à Jérusalem; et il ne fit point ce qui est droit devant l'Eternel son Dieu comme [avait fait] David son père.
3 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila har ya miƙa ɗansa hadaya a wuta, yana bin hanyoyin banƙyama na al’ummai da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Mais il suivit le train des Rois d'Israël, et même il fit passer son fils par le feu, selon les abominations des nations que l'Eternel avait chassées de devant les enfants d'Israël.
4 Ya miƙa hadaya, ya kuma ƙona turare a masujadan tudu, da kan tuddai, da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
Il sacrifiait aussi et faisait des encensements dans les hauts lieux, et sur les coteaux, et sous tout arbre verdoyant.
5 Sai Rezin sarkin Aram, da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su kai wa Urushalima hari, suka kuma kewaye Ahaz, amma ba su iya shan ƙarfinsa ba.
Alors Retsin Roi de Syrie, et Pékach fils de Rémalia Roi d'Israël, montèrent contre Jérusalem pour lui faire la guerre, et ils assiégèrent Achaz; mais ils n'en purent point venir à bout par les armes.
6 A wannan lokaci, Rezin sarkin Aram ya sāke ƙwato Elat wa Aram ta wurin korar Yahuda. Sa’an nan mutanen Edom suka mamaye Elat suna kuwa zaune a can har yau.
En ce temps-là Retsin Roi de Syrie, remit Elath en la puissance des Syriens, car il déposséda les Juifs d'Elath, et les Syriens entrèrent à Elath, et ils y ont demeuré jusqu'à ce jour.
7 Ahaz ya aika a faɗa wa Tiglat-Fileser sarkin Assuriya cewa, “Ni abokin tarayyarka ne kuma mai dogara da kai. Ka haura ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra’ila waɗanda suke kawo mini hari.”
Or Achaz avait envoyé des messagers à Tiglath-piléser Roi des Assyriens, pour lui dire: Je suis ton serviteur, et ton fils; monte et délivre-moi de la main du Roi des Syriens, et de la main du Roi d'Israël, qui s'élèvent contre moi.
8 Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyar da suke a haikalin Ubangiji da suke kuma a ma’ajin fada ya aika wa sarkin Assuriya kyauta.
Et Achaz avait pris l'argent et l'or qui s'était trouvé dans la maison de l'Eternel, et dans les trésors de la maison Royale, et il l'avait envoyé en don au Roi d'Assyrie.
9 Sai sarkin Assuriya ya ji roƙonsa. Ya tashi ya fāɗa wa Damaskus da hari ya kuma kame ta. Ya kwashi mazaunanta zuwa Kir, ya kuma kashe Rezin.
Et le Roi d'Assyrie y acquiesça, et monta à Damas, et la prit, et en transporta le peuple à Kir, et fit mourir Retsin.
10 Sa’an nan sarki Ahaz ya tafi Damaskus don yă sadu da Tiglat-Fileser sarkin Assuriya. Da ya kai can sai ya ga wani bagade a Damaskus, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayanin bagaden.
Alors le Roi Achaz s'en alla au devant de Tiglath-piléser Roi d'Assyrie, à Damas; et le Roi Achaz ayant vu l'autel qui était à Damas, envoya à Urie le Sacrificateur la figure et le modèle de cet autel, selon toute la façon qu'il avait.
11 Saboda haka Uriya firist ya gina bagaden bisa ga tsarin da Sarki Ahaz ya aika masa daga Damaskus, ya kuma gama shi kafin Sarki Ahaz yă dawo.
Et Urie le Sacrificateur bâtit un autel, suivant tout ce que le Roi Achaz avait mandé de Damas; Urie le Sacrificateur le fit tout semblable, en attendant que le Roi Achaz fût revenu de Damas.
12 Da sarki ya dawo daga Damaskus ya ga bagaden, sai ya tafi kusa da shi ya kuma miƙa hadaya a bisansa.
Et quand le Roi Achaz fut revenu de Damas, et eut vu l'autel, il s'en approcha, et offrit sur cet autel;
13 Ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa da ta hatsi, ya zuba hadayarsa ta sha, ya kuma yayyafa jinin hadayunsa ta zumunci a bisa bagaden.
Et fit fumer son holocauste et son sacrifice, et versa ses aspersions, et répandit le sang de ses sacrifices de prospérité sur cet autel-là.
14 Sai ya cire bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi a gaban haikalin wato, tsakanin ƙofar shiga haikalin Ubangiji da sabon bagaden. Ya ajiye shi a gefen arewa na sabon bagaden.
Et quant à l'autel d'airain qui était devant l'Eternel, il le fit reculer de devant la maison, d'entre l'autel et la maison de l'Eternel, et le mit à côté de cet [autre] autel, vers le Septentrion.
15 Sarkin Ahaz ya umarci Uriya cewa, “A kan babban sabon bagade, ka miƙa hadayar ƙonawa ta safe, da hadayar hatsi ta yamma, da hadayar sarki ta ƙonawa da hadayarsa ta hatsi, da hadaya ta dukan jama’ar ƙasar, tare da hadayan hatsinsu da kuma ta sha. Ka yayyafa jinin hadayun ƙonawa a kan bagade. Amma zan yi amfani da bagaden tagulla don neman bishewa.”
Et le Roi Achaz commanda à Urie le Sacrificateur, et lui dit: Fais fumer l'holocauste du matin, et l'oblation du soir, et l'holocauste du Roi avec son gâteau, et l'holocauste de tout le peuple du pays avec leurs gâteaux et leurs aspersions sur le grand autel, et répands tout le sang des holocaustes et tout le sang des sacrifices sur cet autel; mais l'autel d'airain sera pour moi, afin de m'y enquérir [du Seigneur].
16 Uriya firist kuwa ya yi duk abin da Sarki Ahaz ya umarta.
Et Urie le Sacrificateur fit comme le Roi Achaz lui avait commandé.
17 Sarkin Ahaz ya kawar da katakon ya kuma ɗauke tasoshin daga mazauninsu da ake iya matsarwa. Ya ɗauke ƙaton kwano mai suna Teku daga kan bijiman tagullar da ya tallafe su ya ajiye a kan mazaunin dutse.
Le Roi Achaz retrancha aussi les embattements des soubassements, et en ôta les cuviers qui étaient dessus, et fit ôter la mer de dessus les bœufs d'airain, qui étaient dessous, et la mit sur un pavé de pierre.
18 Ya kawar da rumfa Asabbacin da aka gina a haikalin, ya kuma kawar da mashigin sarki na waje da haikalin Ubangiji, duk dai don yă gamshi sarkin Assuriya.
Il ôta aussi de la maison de l'Eternel le couvert du Sabbat qu'on avait bâti au Temple, et l'entrée du Roi qui était en dehors, à cause du Roi des Assyriens.
19 Game da sauran ayyukan mulkin Ahaz, abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Le reste des faits d'Achaz, lesquels il a faits, n'est-il pas écrit au Livre des Chroniques des Rois de Juda?
20 Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi da su a Birnin Dawuda. Hezekiya ɗansa kuma ya gāje shi.
Puis Achaz s'endormit avec ses pères, et fut enseveli avec eux en la Cité de David; et Ezéchias son fils régna en sa place.

< 2 Sarakuna 16 >