< 2 Sarakuna 16 >

1 A shekara ta goma sha bakwai ta mulkin Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda ya fara mulki.
When Pekah had been ruling Israel for almost 17 years, Ahaz, the son of Jotham, became the king of Judah.
2 Ahaz ya zama sarki yana da shekara ashirin, ya kuma yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima ba kamar Dawuda mahaifinsa ba. Ahaz bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa ba.
He was 20 years old when he became the king [of Judah]. He ruled from Jerusalem for 16 years. He did not do things that pleased Yahweh his God, good things like his ancestor King David had done.
3 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila har ya miƙa ɗansa hadaya a wuta, yana bin hanyoyin banƙyama na al’ummai da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Instead, he was as sinful as the kings of Israel had been. He even sacrificed his son as an offering to idols. That was worse than the disgusting things that the people who previously lived there had done, people whom Yahweh had expelled as the Israelis were advancing through the land.
4 Ya miƙa hadaya, ya kuma ƙona turare a masujadan tudu, da kan tuddai, da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
Ahaz offered sacrifices and burned incense [to honor Yahweh] on the tops of many hills and under many [HYP] big trees, [instead of in Jerusalem as Yahweh had commanded].
5 Sai Rezin sarkin Aram, da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su kai wa Urushalima hari, suka kuma kewaye Ahaz, amma ba su iya shan ƙarfinsa ba.
While he was the king of Judah, King Rezin of Assyria and King Pekah of Israel [came with their armies] and attacked Jerusalem. They surrounded the city, but they could not conquer it.
6 A wannan lokaci, Rezin sarkin Aram ya sāke ƙwato Elat wa Aram ta wurin korar Yahuda. Sa’an nan mutanen Edom suka mamaye Elat suna kuwa zaune a can har yau.
At that time the [army of the] king of Edom expelled the people of Judah who were living in Elath [city]. Some of the people of Edom started to live there, and they are still living there.
7 Ahaz ya aika a faɗa wa Tiglat-Fileser sarkin Assuriya cewa, “Ni abokin tarayyarka ne kuma mai dogara da kai. Ka haura ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra’ila waɗanda suke kawo mini hari.”
King Ahaz sent messengers to King Tiglath-Pileser of Assyria, to tell this message to him: “I promise that I will completely do what you tell me to do, [as though] I [was] your son. Please come and rescue us from the armies of Syria and Israel who are attacking my country.”
8 Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyar da suke a haikalin Ubangiji da suke kuma a ma’ajin fada ya aika wa sarkin Assuriya kyauta.
Ahaz took the silver and gold that was in the palace and in the temple and sent it to Assyria to be a present/gift for the king of Assyria.
9 Sai sarkin Assuriya ya ji roƙonsa. Ya tashi ya fāɗa wa Damaskus da hari ya kuma kame ta. Ya kwashi mazaunanta zuwa Kir, ya kuma kashe Rezin.
So Tiglath-Pileser did what Ahaz requested. His army marched to Damascus and captured it, and they took the people of Damascus as prisoners to live in the capital city of Assyria, and executed [King] Rezin.
10 Sa’an nan sarki Ahaz ya tafi Damaskus don yă sadu da Tiglat-Fileser sarkin Assuriya. Da ya kai can sai ya ga wani bagade a Damaskus, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayanin bagaden.
When King Ahaz went to Damascus to meet King Tiglath-Pileser, he saw the altar that was there. So he sent to Uriah, the Supreme Priest [in Jerusalem], a drawing of the altar and a model that was exactly like the altar in Damascus.
11 Saboda haka Uriya firist ya gina bagaden bisa ga tsarin da Sarki Ahaz ya aika masa daga Damaskus, ya kuma gama shi kafin Sarki Ahaz yă dawo.
So Uriah built an altar [in Jerusalem], following the drawing that King Ahaz had sent. Uriah finished the altar before Ahaz returned [to Jerusalem] from Damascus.
12 Da sarki ya dawo daga Damaskus ya ga bagaden, sai ya tafi kusa da shi ya kuma miƙa hadaya a bisansa.
When the king returned from Damascus, he saw the altar. He went to it
13 Ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa da ta hatsi, ya zuba hadayarsa ta sha, ya kuma yayyafa jinin hadayunsa ta zumunci a bisa bagaden.
and burned animal sacrifices and a grain offering on it. He also poured a wine offering on it and threw on it the blood of the offerings to maintain fellowship with God.
14 Sai ya cire bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi a gaban haikalin wato, tsakanin ƙofar shiga haikalin Ubangiji da sabon bagaden. Ya ajiye shi a gefen arewa na sabon bagaden.
The old bronze altar which had been dedicated long ago to Yahweh was between the new altar and the temple, so Ahaz moved it to the north side of his new altar, [which was bigger than the old altar].
15 Sarkin Ahaz ya umarci Uriya cewa, “A kan babban sabon bagade, ka miƙa hadayar ƙonawa ta safe, da hadayar hatsi ta yamma, da hadayar sarki ta ƙonawa da hadayarsa ta hatsi, da hadaya ta dukan jama’ar ƙasar, tare da hadayan hatsinsu da kuma ta sha. Ka yayyafa jinin hadayun ƙonawa a kan bagade. Amma zan yi amfani da bagaden tagulla don neman bishewa.”
Then King Ahaz ordered Uriah: “Each morning put on this new altar the sacrifices that will be completely burned, and in the evening put on it the grain offering, along with my offering and the offerings that the people bring, ones that will be completely burned, and my grain offering and the people’s grain and wine offerings. Pour against the sides of the altar the blood of all the animals that are sacrificed. But the old bronze altar will be only for me to use to find out what Yahweh wants me to do.”
16 Uriya firist kuwa ya yi duk abin da Sarki Ahaz ya umarta.
So Uriah did what the king commanded him to do.
17 Sarkin Ahaz ya kawar da katakon ya kuma ɗauke tasoshin daga mazauninsu da ake iya matsarwa. Ya ɗauke ƙaton kwano mai suna Teku daga kan bijiman tagullar da ya tallafe su ya ajiye a kan mazaunin dutse.
King Ahaz told his workers to take off the frames of the carts [that were outside the temple] and to take down the basins that were on them. They also took down the bronze tank from the backs of the bronze [statues of the] oxen and put it on a stone foundation.
18 Ya kawar da rumfa Asabbacin da aka gina a haikalin, ya kuma kawar da mashigin sarki na waje da haikalin Ubangiji, duk dai don yă gamshi sarkin Assuriya.
Then to please the king of Assyria, Ahaz had them remove from the temple the roof under which the people walked into the temple on the Sabbath Day, and closed up the private entrance into the temple for the kings of Judah.
19 Game da sauran ayyukan mulkin Ahaz, abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
[If you want to know about] the other things that Ahaz did, they are written [RHQ] in the scroll called ‘The History of the Kings of Judah’.
20 Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi da su a Birnin Dawuda. Hezekiya ɗansa kuma ya gāje shi.
Ahaz died [EUP], and he was buried in [the part of Jerusalem called] ‘The City of David’, where his ancestors had been buried. Then his son Hezekiah became the king.

< 2 Sarakuna 16 >