< 2 Sarakuna 16 >
1 A shekara ta goma sha bakwai ta mulkin Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda ya fara mulki.
In the seventeenth year of Pekah, the son of Remaliah: Ahaz, the son of Jotham, reigned as king of Judah.
2 Ahaz ya zama sarki yana da shekara ashirin, ya kuma yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima ba kamar Dawuda mahaifinsa ba. Ahaz bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa ba.
Ahaz was twenty years old when he had begun to reign, and he reigned for sixteen years in Jerusalem. He did not do what was pleasing in the sight of the Lord, his God, as his father David did.
3 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila har ya miƙa ɗansa hadaya a wuta, yana bin hanyoyin banƙyama na al’ummai da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Instead, he walked in the way of the kings of Israel. Moreover, he even consecrated his son, making him pass through fire, in accord with the idols of the nations that the Lord destroyed before the sons of Israel.
4 Ya miƙa hadaya, ya kuma ƙona turare a masujadan tudu, da kan tuddai, da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
Also, he was immolating victims, and burning incense, in the high places, and on the hills, and under every leafy tree.
5 Sai Rezin sarkin Aram, da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su kai wa Urushalima hari, suka kuma kewaye Ahaz, amma ba su iya shan ƙarfinsa ba.
Then Rezin, the king of Syria, and Pekah, the son of Remaliah, the king of Israel, ascended to do battle against Jerusalem. And they besieged Ahaz, but they were not able to overcome him.
6 A wannan lokaci, Rezin sarkin Aram ya sāke ƙwato Elat wa Aram ta wurin korar Yahuda. Sa’an nan mutanen Edom suka mamaye Elat suna kuwa zaune a can har yau.
At that time, Rezin, the king of Syria, restored Elath to Syria, and he expelled the Judeans from Elath. And the Idumeans went into Elath, and they have lived there, even to this day.
7 Ahaz ya aika a faɗa wa Tiglat-Fileser sarkin Assuriya cewa, “Ni abokin tarayyarka ne kuma mai dogara da kai. Ka haura ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra’ila waɗanda suke kawo mini hari.”
Then Ahaz sent messengers to Tiglath-pileser, the king of the Assyrians, saying: “I am your servant, and I am your son. Ascend and accomplish my salvation from the hand of the king of Syria, and from the hand of the king of Israel, who have risen up together against me.”
8 Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyar da suke a haikalin Ubangiji da suke kuma a ma’ajin fada ya aika wa sarkin Assuriya kyauta.
And when he had collected the silver and the gold that could be found in the house of the Lord, and in the treasuries of the king, he sent it as a gift to the king of the Assyrians.
9 Sai sarkin Assuriya ya ji roƙonsa. Ya tashi ya fāɗa wa Damaskus da hari ya kuma kame ta. Ya kwashi mazaunanta zuwa Kir, ya kuma kashe Rezin.
And he agreed to his will. For the king of the Assyrians ascended against Damascus, and he laid waste to it. And he carried away its inhabitants to Cyrene. But Rezin he killed.
10 Sa’an nan sarki Ahaz ya tafi Damaskus don yă sadu da Tiglat-Fileser sarkin Assuriya. Da ya kai can sai ya ga wani bagade a Damaskus, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayanin bagaden.
And king Ahaz traveled to Damascus to meet Tiglath-pileser, the king of the Assyrians. And when he had seen the altar of Damascus, king Ahaz sent to Uriah, the priest, its pattern and likeness, according to all of its work.
11 Saboda haka Uriya firist ya gina bagaden bisa ga tsarin da Sarki Ahaz ya aika masa daga Damaskus, ya kuma gama shi kafin Sarki Ahaz yă dawo.
And Uriah, the priest, constructed an altar in accord with all that king Ahaz had commanded from Damascus. Uriah, the priest, did so, until king Ahaz arrived from Damascus.
12 Da sarki ya dawo daga Damaskus ya ga bagaden, sai ya tafi kusa da shi ya kuma miƙa hadaya a bisansa.
And when the king had arrived from Damascus, he saw the altar, and he venerated it. And he went up and immolated holocausts, with his own sacrifice.
13 Ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa da ta hatsi, ya zuba hadayarsa ta sha, ya kuma yayyafa jinin hadayunsa ta zumunci a bisa bagaden.
And he offered libations, and he poured out the blood of the peace offerings, which he had offered, upon the altar.
14 Sai ya cire bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi a gaban haikalin wato, tsakanin ƙofar shiga haikalin Ubangiji da sabon bagaden. Ya ajiye shi a gefen arewa na sabon bagaden.
But the altar of brass, which was before the Lord, he took away from the face of the temple, and from the place of the altar, and from the place of the temple of the Lord. And he positioned it at the side of the altar, toward the north.
15 Sarkin Ahaz ya umarci Uriya cewa, “A kan babban sabon bagade, ka miƙa hadayar ƙonawa ta safe, da hadayar hatsi ta yamma, da hadayar sarki ta ƙonawa da hadayarsa ta hatsi, da hadaya ta dukan jama’ar ƙasar, tare da hadayan hatsinsu da kuma ta sha. Ka yayyafa jinin hadayun ƙonawa a kan bagade. Amma zan yi amfani da bagaden tagulla don neman bishewa.”
Also, king Ahaz instructed Uriah, the priest, saying: “Upon the great altar, offer the morning holocaust, and the evening sacrifice, and the holocaust of the king, and his sacrifice, and the holocaust of the entire people of the land, and their sacrifices. But their libations, and all the blood of the holocaust, and all the blood of the victim, you shall pour out upon it. Then truly, the altar of brass shall be prepared for use at my will.”
16 Uriya firist kuwa ya yi duk abin da Sarki Ahaz ya umarta.
And so Uriah, the priest, acted in accord with all that king Ahaz had instructed to him.
17 Sarkin Ahaz ya kawar da katakon ya kuma ɗauke tasoshin daga mazauninsu da ake iya matsarwa. Ya ɗauke ƙaton kwano mai suna Teku daga kan bijiman tagullar da ya tallafe su ya ajiye a kan mazaunin dutse.
Then king Ahaz took away the engraved bases, and the basin that was upon them. And he took down the sea from the bronze oxen, which were holding it up. And he positioned it upon a layer of pavement stone.
18 Ya kawar da rumfa Asabbacin da aka gina a haikalin, ya kuma kawar da mashigin sarki na waje da haikalin Ubangiji, duk dai don yă gamshi sarkin Assuriya.
Also, the canopy for the Sabbath, which he had built in the temple, and the exterior entrance of the king, he converted into the temple of the Lord, because of the king of the Assyrians.
19 Game da sauran ayyukan mulkin Ahaz, abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Now the rest of the words of Ahaz that he did, have these not been written in the book of the words of the days of the kings of Judah?
20 Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi da su a Birnin Dawuda. Hezekiya ɗansa kuma ya gāje shi.
And Ahaz slept with his fathers, and he was buried with them in the city of David. And Hezekiah, his son, reigned in his place.