< 2 Sarakuna 15 >

1 A shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Yerobowam sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya, sarkin Yahuda ya fara mulki.
Jerobeama, Israēla ķēniņa, divdesmit septītā gadā Azarija, Amacījas, Jūda ķēniņa, dēls, palika par ķēniņu.
2 Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya daga Urushalima.
Viņš bija sešpadsmit gadus vecs, kad viņš palika par ķēniņu, un valdīja piecdesmit un divus gadus Jeruzālemē. Un viņa mātei bija vārds Jekalija no Jeruzālemes.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
Un viņš darīja, kas Tam Kungam labi patika, kā viņa tēvs Amacīja bija darījis.
4 Amma bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane kuwa suka yi ta yin hadaya da ƙona turare a can.
Tikai kalnu altāri vien netapa nopostīti, bet ļaudis upurēja un kvēpināja vēl pa kalniem.
5 Ubangiji ya sa wa sarki ciwon kuturta har mutuwarsa, ya kuma zauna a keɓe. Yotam ɗan sarki, shi ne ya gudanar da sha’anin fada, ya kuma shugabanci mutanen ƙasar.
Un Tas Kungs sita ķēniņu, ka tas palika spitālīgs līdz savas miršanas dienai, un viņš dzīvoja slimnieku namā. Bet Jotams, ķēniņa dēls, bija pār to namu un tiesāja tās zemes ļaudis.
6 Game da sauran ayyukan mulkin Azariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Kas vēl par Azariju stāstāms, un viss, ko viņš darījis, tas ir rakstīts Jūda ķēniņu laiku grāmatā.
7 Azariya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi kusa da su a Birnin Dawuda. Yotam ɗansa, kuma ya gāje shi.
Un Azarija aizmiga saviem tēviem pakaļ, un to apraka pie viņa tēviem Dāvida pilī, un Jotams, viņa dēls, palika par ķēniņu viņa vietā.
8 A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Zakariya ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki wata shida.
Azarijas, Jūda ķēniņa, trīsdesmit astotā gadā Zaharija, Jerobeama dēls, palika par ķēniņu pār Israēli Samarijā, un valdīja sešus mēnešus,
9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi. Bai bar aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi ba.
Un darīja, kas Tam Kungam nepatika, kā viņa tēvi bija darījuši; viņš neatstājās no Jerobeama, Nebata dēla, grēkiem, kas Israēli bija pavedis uz grēkiem.
10 Sai Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zakariya maƙarƙashiya. Ya tasam masa a gaban jama’a, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
Un Šalums, Jabesa dēls, cēla dumpi pret viņu un to kāva ļaužu priekšā un to nokāva un palika par ķēniņu viņa vietā.
11 Game da sauran ayyukan mulkin Zakariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Un kas vēl par Zahariju stāstāms, redzi, tas ir rakstīts Israēla ķēniņu laiku grāmatā.
12 Ta haka maganar Ubangiji da ya yi wa Yehu ta cika, wadda ya ce, “Zuriyarka za tă zauna a kursiyin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
Šis bija Tā Kunga vārds, ko viņš bija runājis uz Jeū sacīdams: līdz ceturtam augumam tavi bērni sēdēs uz Israēla goda krēsla; un tā tas noticis.
13 Shallum ɗan Yabesh ya zama sarki a shekara ta talatin da tara ta mulkin Uzziya sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki na wata ɗaya a Samariya.
Šalums, Jabesa dēls, palika par ķēniņu Uzijas, Jūda ķēniņa, trīsdesmit devītā gadā un valdīja vienu mēnesi Samarijā.
14 Sa’an nan Menahem ɗan Gadi ya gangara daga Tirza ya haura zuwa Samariya. Ya tasam wa Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
Jo Menaēms, Gadus dēls, cēlās no Tircas un nāca uz Samariju, un kāva Šalumu, Jabesa dēlu, Samarijā un to nokāva un palika par ķēniņu viņa vietā.
15 Game da sauran ayyukan mulkin Shallum, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Un kas vēl par Šalumu stāstāms, un tas dumpis, ko viņš cēlis, redzi, tas ir rakstīts Israēla ķēniņu laiku grāmatā.
16 A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
Tad Menaēms kāva Tivzu un visu, kas tur bija, un viņas robežas no Tircas nākdams, tāpēc ka tie viņam nebija (vārtus) atdarījuši, un viņš to kāva un pāršķēla visas grūtās sievas.
17 A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya zama sarkin Isra’ila, ya yi mulki a Samariya shekara goma.
Azarijas, Jūda ķēniņa, trīsdesmit devītā gadā Menaēms, Gadus dēls, palika par ķēniņu pār Israēli un valdīja desmit gadus Samarijā.
18 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A duk tsawon mulkinsa, bai rabu da zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya sa Isra’ila suka aikata ba.
Un viņš darīja, kas Tam Kungam nepatika, un kamēr dzīvoja, viņš neatstājās no Jerobeama, Nebata dēla, grēkiem, kas Israēli bija pavedis uz grēkiem.
19 Sai Ful sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar hari, Menahem kuwa ya ba shi talenti dubu na azurfa don yă sami goyon bayansa, yă kuma ƙarfafa kahuwa mulkin.
Tad Pūls, Asīrijas ķēniņš, nāca pret to zemi, un Menaēms deva Pūlam tūkstoš talentus sudraba, lai viņa roka ar to būtu, ka varētu stiprināties savā valstībā.
20 Menahem ya tara kuɗin ne ta hanyar haraji a Isra’ila inda ya sa kowane attajiri ya ba da shekel hamsin don a ba sarkin Assuriya. Sa’an nan sarkin Assuriya ya janye, bai ƙara kasance a ƙasar ba.
Un Menaēms to naudu izspieda no Israēla, un ikkatram bagātam bija jādod Asīrijas ķēniņam par ikkatru vīru piecdesmit sudraba sēķeli. Tad Asīrijas ķēniņš griezās atpakaļ un nepalika vairs tai zemē
21 Game da sauran ayyukan mulkin Menahem, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Un kas vēl stāstāms par Menaēmu, un viss, ko viņš darījis, tas ir rakstīts Israēla ķēniņu laiku grāmatā.
22 Menahem ya huta tare da kakanninsa. Fekahiya ɗansa kuma ya gāje shi.
Un Menaēms aizmiga saviem tēviem pakaļ, un Pekaja, viņa dēls, palika par ķēniņu viņa vietā.
23 A shekara ta hamsin ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekara biyu.
Azarijas, Jūda ķēniņa, piecdesmitā gadā Pekaja, Menaēma dēls, palika par ķēniņu pār Israēli Samarijā, un valdīja divus gadus,
24 Fekahiya ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat wanda ya sa Isra’ila ya aikata ba.
Un darīja, kas Tam Kungam nepatika; viņš neatstājās no Jerobeama, Nebata dēla, grēkiem, kas Israēli bija pavedis uz grēkiem.
25 Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
Un Peka, Remalijas dēls, viņa virsnieks, cēla dumpi pret viņu un to kāva Samarijā, ķēniņa nama pagalmā, ar Argobu un ar Arju; un pie viņa bija piecdesmit vīri no Gileādas bērniem, un viņš to nokāva, un palika par ķēniņu viņa vietā.
26 Game da sauran ayyukan mulkin Fekahiya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Un kas vēl stāstāms par Pekaju, un viss, ko viņš darījis, redzi, tas ir rakstīts Israēla ķēniņu laiku grāmatā.
27 A shekara ta hamsin da biyu ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Feka ɗan Remaliya ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya yi mulki shekara ashirin.
Azarijas, Jūda ķēniņa, piecdesmit otrā gadā Peka, Remalijas dēls, palika par ķēniņu pār Israēli Samarijā un valdīja divdesmit gadus.
28 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai kauce wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta yi ba.
Un viņš darīja, kas Tam Kungam nepatika; viņš neatstājās no Jerobeama, Nebata dēla, grēkiem, kas Israēli bija pavedis uz grēkiem.
29 A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
Pekas, Israēla ķēniņa, laikā Tiglat Pilezers, Asīrijas ķēniņš, atnāca un uzņēma Jonu un AbelBetMaāku un Janoū un Ķedesu un Hacoru un Gileādu un Galileju un visu Naftalus zemi, un tos noveda uz Asīriju.
30 Sa’an nan Hosheya ɗan Ela ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya. Ya fāɗa masa ya kuma kashe shi, sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki a shekara ta shirin ta mulkin Yotam ɗan Uzziya.
Un Hoseja, Elas dēls, cēla dumpi pret Peku, Remalijas dēlu, un to sita un nokāva un palika par ķēniņu viņa vietā Jotama, Uzijas dēla, divdesmitā gadā.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Feka da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Un kas vēl par Peku stāstāms, un viss, ko viņš darījis, redzi, tas ir rakstīts Israēla ķēniņu laiku grāmatā.
32 A shekara ta biyu ta mulkin Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Uzziya sarkin Yahuda ya fara mulki.
Pekas, Remalijas dēla, Israēla ķēniņa, otrā gadā Jotams, Uzijas dēls, palika par ķēniņu pār Jūdu.
33 Ya zama sarki yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
Divdesmit pieci gadus viņš bija vecs, kad palika par ķēniņu, un valdīja sešpadsmit gadus Jeruzālemē, un viņa mātei bija vārds Jeruza, Cadaka meita.
34 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa Uzziya ya yi.
Un viņš darīja, kas Tam Kungam labi patika, kā viņa tēvs Uzija bija darījis, tā viņš darīja.
35 Duk da haka, bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙona turare a can. Yotam ya sāke gina Ƙofar Bisa ta haikalin Ubangiji.
Tikai kalnu altāri vien netapa nopostīti, ļaudis upurēja un kvēpināja vēl pa kalniem. Šis uztaisīja tos augšvārtus pie Tā Kunga nama.
36 Game da sauran ayyukan mulkin Yotam da aikin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Un kas vēl par Jotamu stāstāms, un viss, ko viņš darījis, tas ir rakstīts Jūda ķēniņu laiku grāmatā.
37 (A kwanakin nan Ubangiji ya fara aikan Rezin sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, su yi gāba da Yahuda.)
Tanī laikā Tas Kungs sāka uz Jūdu sūtīt Recinu, Sīriešu ķēniņu un Peku, Remalijas dēlu.
38 Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda, birnin mahaifinsa. Ahaz ɗansa kuma ya gāje shi.
Un Jotams aizmiga saviem tēviem pakaļ, un tapa aprakts pie saviem tēviem Dāvida, sava tēva, pilī. Un Ahazs, viņa dēls, palika par ķēniņu viņa vietā.

< 2 Sarakuna 15 >