< 2 Sarakuna 15 >

1 A shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Yerobowam sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya, sarkin Yahuda ya fara mulki.
La vingt-septième année de Jéroboam Roi d'Israël, Hazaria fils d'Amatsia Roi de Juda régnait.
2 Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya daga Urushalima.
Il était âgé de seize ans quand il commença à régner, et il régna cinquante-deux ans à Jérusalem; sa mère avait nom Jécolia, [et] était de Jérusalem.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
Il fit ce qui est droit devant l'Eternel, comme avait fait Amatsia son père.
4 Amma bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane kuwa suka yi ta yin hadaya da ƙona turare a can.
Tellement qu'il n'y eut que les hauts lieux qui ne furent point ôtés; le peuple sacrifiait encore et faisait des encensements sur les hauts lieux.
5 Ubangiji ya sa wa sarki ciwon kuturta har mutuwarsa, ya kuma zauna a keɓe. Yotam ɗan sarki, shi ne ya gudanar da sha’anin fada, ya kuma shugabanci mutanen ƙasar.
r l'Eternel frappa le Roi, qui fut lépreux jusqu'au jour qu'il mourut, et il demeura dans une maison séquestrée; et Jotham fils du Roi avait la charge de la maison, jugeant le peuple du pays.
6 Game da sauran ayyukan mulkin Azariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Le reste des faits de Hazaria, tout ce, dis-je, qu'il a fait, n'est-il pas écrit au Livre des Chroniques des Rois de Juda?
7 Azariya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi kusa da su a Birnin Dawuda. Yotam ɗansa, kuma ya gāje shi.
Et Hazaria s'endormit avec ses pères, et fut enseveli avec ses pères en la Cité de David, et Jotham son fils régna en sa place.
8 A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Zakariya ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki wata shida.
La trente-huitième année de Hazaria Roi de Juda, Zacharie fils de Jéroboam commença à régner sur Israël à Samarie, [et il régna] six mois.
9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi. Bai bar aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi ba.
Et il fit ce gui déplaît à l'Eternel, comme avaient fait ses pères; il ne se détourna point des péchés de Jéroboam fils de Nébat, par lesquels il avait fait pécher Israël.
10 Sai Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zakariya maƙarƙashiya. Ya tasam masa a gaban jama’a, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
Or Sallum fils de Jabés, fit une conspiration contre lui, et le frappa en la présence du peuple, et le tua, et il régna en sa place.
11 Game da sauran ayyukan mulkin Zakariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Quant au reste des faits de Zacharie, voilà, ils sont écrits au Livre des Chroniques des Rois d'Israël.
12 Ta haka maganar Ubangiji da ya yi wa Yehu ta cika, wadda ya ce, “Zuriyarka za tă zauna a kursiyin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
C'est là la parole de l'Eternel laquelle il avait prononcée à Jéhu, en disant: Tes fils seront assis sur le trône d'Israël jusqu'à la quatrième génération; et il arriva ainsi.
13 Shallum ɗan Yabesh ya zama sarki a shekara ta talatin da tara ta mulkin Uzziya sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki na wata ɗaya a Samariya.
Sallum fils de Jabés commença à régner la trente-neuvième année d'Hozias Roi de Juda, et il ne régna que l'espace d'un mois entier à Samarie.
14 Sa’an nan Menahem ɗan Gadi ya gangara daga Tirza ya haura zuwa Samariya. Ya tasam wa Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
Car Ménahem fils de Gadi, qui était de Tirtsa, monta, et entra dans Samarie, et frappa Sallum fils de Jabés à Samarie, et le tua, et il régna en sa place.
15 Game da sauran ayyukan mulkin Shallum, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Quant au reste des faits de Sallum, et quant à la conspiration qu'il fit, voilà, ces choses sont écrites au Livre des Chroniques des Rois d'Israël.
16 A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
Et Ménahem battit Tiphsah, et tous ceux qui étaient dedans, et dans sa contrée, depuis Tirtsa, parce qu'elle ne lui avait point ouvert [les portes], et les tua; et il fendit toutes les femmes grosses qui s'y trouvèrent.
17 A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya zama sarkin Isra’ila, ya yi mulki a Samariya shekara goma.
La trente-neuvième année de Hazaria Roi de Juda, Ménahem fils de Gadi, commença à régner sur Israël, [il régna] dix ans en Samarie.
18 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A duk tsawon mulkinsa, bai rabu da zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya sa Isra’ila suka aikata ba.
Et il fit ce qui déplaît à l'Eternel; il ne se détourna point des péchés de Jéroboam fils de Nébat, par lesquels il avait fait pécher Israël, durant tout son temps.
19 Sai Ful sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar hari, Menahem kuwa ya ba shi talenti dubu na azurfa don yă sami goyon bayansa, yă kuma ƙarfafa kahuwa mulkin.
Alors Pul, Roi des Assyriens, vint contre le pays; et Ménahem donna mille talents d'argent à Pul, afin qu'il lui aidât à affermir son Royaume entre ses mains.
20 Menahem ya tara kuɗin ne ta hanyar haraji a Isra’ila inda ya sa kowane attajiri ya ba da shekel hamsin don a ba sarkin Assuriya. Sa’an nan sarkin Assuriya ya janye, bai ƙara kasance a ƙasar ba.
Et Ménahem tira cet argent d'Israël, de tous ceux qui étaient puissants en biens, pour le donner au Roi des Assyriens, de chacun cinquante sicles d'argent; ainsi le Roi des Assyriens s'en retourna, et ne s'arrêta point au pays.
21 Game da sauran ayyukan mulkin Menahem, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Le reste des faits de Ménahem, tout ce, dis-je, qu'il a fait, n'est-il pas écrit au Livre des Chroniques des Rois d'Israël?
22 Menahem ya huta tare da kakanninsa. Fekahiya ɗansa kuma ya gāje shi.
Et Ménahem s'endormit avec ses pères, et Pékachia son fils régna en sa place.
23 A shekara ta hamsin ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekara biyu.
La cinquantième année d'Hazaria Roi de Juda, Pékachia fils de Ménahem commença à régner sur Israël à Samarie, [et il régna] deux ans.
24 Fekahiya ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat wanda ya sa Isra’ila ya aikata ba.
Et il fit ce qui déplaît à l'Eternel, et ne se détourna point des péchés de Jéroboam fils de Nébat, par lesquels il avait fait pécher Israël.
25 Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
Et Pékach fils de Rémalia son capitaine fit une conspiration contre lui, et le frappa à Samarie, au palais de la maison Royale, avec Argob et Arié, ayant avec soi cinquante hommes des enfants des Galaadites; ainsi il le tua, et il régna en sa place.
26 Game da sauran ayyukan mulkin Fekahiya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Le reste des actions de Pékachia, tout ce, dis-je, qu'il a fait, voilà, il est écrit au Livre des Chroniques des Rois d'Israël.
27 A shekara ta hamsin da biyu ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Feka ɗan Remaliya ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya yi mulki shekara ashirin.
La cinquante et deuxième année d'Hazaria Roi de Juda, Pékach fils de Rémalia commença à régner sur Israël à Samarie, [et il régna] vingt ans.
28 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai kauce wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta yi ba.
Et il fit ce qui déplaît à l'Eternel, il ne se détourna point des péchés de Jéroboam fils de Nébat, par lesquels il avait fait pécher Israël.
29 A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
Aux jours de Pékach Roi d'Israël, Tiglath-piléser Roi des. Assyriens, vint, et prit Hijon, et Abel-bethmahaca, et Janoah, et Kédés, et Hatsor, et Galaad, et la Galilée, même tout le pays de Nephthali, et en transporta le peuple en Assyrie.
30 Sa’an nan Hosheya ɗan Ela ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya. Ya fāɗa masa ya kuma kashe shi, sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki a shekara ta shirin ta mulkin Yotam ɗan Uzziya.
Or Hosée, fils d'Ela, fit une conspiration contre Pékach fils de Rémalia, et le frappa, et le tua, et il régna en sa place la vingtième année de Jotham fils de Hozias.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Feka da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Le reste des faits de Pékach, tout ce, dis-je, qu'il a fait, voilà, il est écrit au Livre des Chroniques des Rois d'Israël.
32 A shekara ta biyu ta mulkin Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Uzziya sarkin Yahuda ya fara mulki.
La seconde année de Pékach fils de Rémalia Roi d'Israël, Jotham fils de Hozias, Roi de Juda commença à régner.
33 Ya zama sarki yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
Il était âgé de vingt et cinq ans quand il commença à régner; et il régna seize ans à Jérusalem; sa mère avait nom Jérusa, [et] était fille de Tsadok.
34 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa Uzziya ya yi.
Il fit ce qui est droit devant l'Eternel; il fit comme Hozias son père avait fait.
35 Duk da haka, bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙona turare a can. Yotam ya sāke gina Ƙofar Bisa ta haikalin Ubangiji.
De sorte qu'il n'y eut que les hauts lieux qui ne furent point ôtés, le peuple sacrifiait encore et faisait des encensements dans les hauts lieux; ce fut lui qui bâtit la plus haute porte de la maison de l'Eternel.
36 Game da sauran ayyukan mulkin Yotam da aikin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Le reste des faits de Jotham, tout ce, dis-je, qu'il a fait, n'est-il pas écrit au Livre des Chroniques des Rois de Juda?
37 (A kwanakin nan Ubangiji ya fara aikan Rezin sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, su yi gāba da Yahuda.)
En ces jours-là l'Eternel commença d'envoyer contre Juda Retsin Roi de Syrie et Pékach fils de Rémalia.
38 Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda, birnin mahaifinsa. Ahaz ɗansa kuma ya gāje shi.
Et Jotham s'endormit avec ses pères, et fut enseveli en la Cité de David son père, et Achaz son fils régna en sa place.

< 2 Sarakuna 15 >