< 2 Sarakuna 15 >
1 A shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Yerobowam sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya, sarkin Yahuda ya fara mulki.
In the twenty-seventh year of Jeroboam king of Israel, Azariah son of Amaziah, king of Judah, has reigned;
2 Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya daga Urushalima.
he was a son of sixteen years in his reigning, and he has reigned fifty-two years in Jerusalem, and the name of his mother [is] Jecholiah of Jerusalem,
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
and he does that which [is] right in the eyes of YHWH, according to all that his father Amaziah did,
4 Amma bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane kuwa suka yi ta yin hadaya da ƙona turare a can.
only, the high places have not been removed—the people are still sacrificing and making incense in high places.
5 Ubangiji ya sa wa sarki ciwon kuturta har mutuwarsa, ya kuma zauna a keɓe. Yotam ɗan sarki, shi ne ya gudanar da sha’anin fada, ya kuma shugabanci mutanen ƙasar.
And YHWH strikes the king, and he is a leper to the day of his death, and he dwells in a separate house, and Jotham son of the king [is] over the house, judging the people of the land.
6 Game da sauran ayyukan mulkin Azariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
And the rest of the matters of Azariah and all that he did, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Judah?
7 Azariya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi kusa da su a Birnin Dawuda. Yotam ɗansa, kuma ya gāje shi.
And Azariah lies with his fathers, and they bury him with his fathers in the city of David, and his son Jotham reigns in his stead.
8 A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Zakariya ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki wata shida.
In the thirty-eighth year of Azariah king of Judah, Zechariah son of Jeroboam has reigned over Israel in Samaria, six months,
9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi. Bai bar aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi ba.
and he does evil in the eyes of YHWH as his fathers did; he has not turned aside from the sins of Jeroboam son of Nebat that he caused Israel to sin.
10 Sai Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zakariya maƙarƙashiya. Ya tasam masa a gaban jama’a, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
And Shallum son of Jabesh conspires against him, and strikes him before the people, and puts him to death, and reigns in his stead.
11 Game da sauran ayyukan mulkin Zakariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the matters of Zechariah, behold, they are written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Israel.
12 Ta haka maganar Ubangiji da ya yi wa Yehu ta cika, wadda ya ce, “Zuriyarka za tă zauna a kursiyin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
It [is] the word of YHWH that He spoke to Jehu, saying, “Sons of the fourth [generation] sit on the throne of Israel for you”; and it is so.
13 Shallum ɗan Yabesh ya zama sarki a shekara ta talatin da tara ta mulkin Uzziya sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki na wata ɗaya a Samariya.
Shallum son of Jabesh has reigned in the thirty-ninth year of Uzziah king of Judah, and he reigns a month of days in Samaria;
14 Sa’an nan Menahem ɗan Gadi ya gangara daga Tirza ya haura zuwa Samariya. Ya tasam wa Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
and Menahem son of Gadi goes up from Tirzah and comes to Samaria, and strikes Shallum son of Jabesh in Samaria, and puts him to death, and reigns in his stead.
15 Game da sauran ayyukan mulkin Shallum, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the matters of Shallum and his conspiracy that he made, behold, they are written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Israel.
16 A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
Then Menahem strikes Tiphsah, and all who [are] in it, and its borders from Tirzah, for it did not open [to him], and he strikes [it], [and] he has ripped up all its pregnant women.
17 A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya zama sarkin Isra’ila, ya yi mulki a Samariya shekara goma.
In the thirty-ninth year of Azariah king of Judah, Menahem son of Gadi has reigned over Israel in Samaria, ten years.
18 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A duk tsawon mulkinsa, bai rabu da zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya sa Isra’ila suka aikata ba.
And he does evil in the eyes of YHWH; he has not turned aside from the sins of Jeroboam son of Nebat that he caused Israel to sin, all his days.
19 Sai Ful sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar hari, Menahem kuwa ya ba shi talenti dubu na azurfa don yă sami goyon bayansa, yă kuma ƙarfafa kahuwa mulkin.
Pul king of Asshur has come against the land, and Menahem gives one thousand talents of silver to Pul, for his hand being with him to strengthen the kingdom in his hand.
20 Menahem ya tara kuɗin ne ta hanyar haraji a Isra’ila inda ya sa kowane attajiri ya ba da shekel hamsin don a ba sarkin Assuriya. Sa’an nan sarkin Assuriya ya janye, bai ƙara kasance a ƙasar ba.
And Menahem brings out the silver [from] Israel, [from] all the mighty men of wealth, to give to the king of Asshur, fifty shekels of silver for each one, and the king of Asshur turns back and has not stayed there in the land.
21 Game da sauran ayyukan mulkin Menahem, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the matters of Menahem and all that he did, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Israel?
22 Menahem ya huta tare da kakanninsa. Fekahiya ɗansa kuma ya gāje shi.
And Menahem lies with his fathers, and his son Pekahiah reigns in his stead.
23 A shekara ta hamsin ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekara biyu.
In the fiftieth year of Azariah king of Judah, Pekahiah son of Menahem has reigned over Israel in Samaria, two years,
24 Fekahiya ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat wanda ya sa Isra’ila ya aikata ba.
and he does evil in the eyes of YHWH; he has not turned aside from the sins of Jeroboam son of Nebat that he caused Israel to sin.
25 Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
And Pekah son of Remaliah, his captain, conspires against him, and strikes him in Samaria, in the high place of the house of the king with Argob and Arieh; and fifty men of the sons of the Gileadites [were] with him, and he puts him to death, and reigns in his stead.
26 Game da sauran ayyukan mulkin Fekahiya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the matters of Pekahiah and all that he did, behold, they are written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Israel.
27 A shekara ta hamsin da biyu ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Feka ɗan Remaliya ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya yi mulki shekara ashirin.
In the fifty-second year of Azariah king of Judah, Pekah son of Remaliah has reigned over Israel in Samaria, twenty years,
28 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai kauce wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta yi ba.
and he does evil in the eyes of YHWH, he has not turned aside from the sins of Jeroboam son of Nebat that he caused Israel to sin.
29 A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
In the days of Pekah king of Israel, Tiglath-Pileser king of Asshur has come, and takes Ijon, and Abel-Beth-Maachah, and Janoah, and Kedesh, and Hazor, and Gilead, and Galilee, all the land of Naphtali, and removes them to Asshur.
30 Sa’an nan Hosheya ɗan Ela ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya. Ya fāɗa masa ya kuma kashe shi, sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki a shekara ta shirin ta mulkin Yotam ɗan Uzziya.
And Hoshea son of Elah makes a conspiracy against Pekah son of Remaliah, and strikes him, and puts him to death, and reigns in his stead, in the twentieth year of Jotham son of Uzziah.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Feka da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the matters of Pekah and all that he did, behold, they are written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Israel.
32 A shekara ta biyu ta mulkin Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Uzziya sarkin Yahuda ya fara mulki.
In the second year of Pekah son of Remaliah, king of Israel, Jotham son of Uzziah, king of Judah, has reigned.
33 Ya zama sarki yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
He was a son of twenty-five years in his reigning, and he has reigned sixteen years in Jerusalem, and the name of his mother [is] Jerusha daughter of Zadok,
34 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa Uzziya ya yi.
and he does that which [is] right in the eyes of YHWH; he has done according to all that his father Uzziah did.
35 Duk da haka, bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙona turare a can. Yotam ya sāke gina Ƙofar Bisa ta haikalin Ubangiji.
Only, the high places have not been removed—the people are still sacrificing and making incense in high places; he has built the high gate of the house of YHWH.
36 Game da sauran ayyukan mulkin Yotam da aikin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
And the rest of the matters of Jotham and all that he did, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Judah?
37 (A kwanakin nan Ubangiji ya fara aikan Rezin sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, su yi gāba da Yahuda.)
In those days YHWH has begun to send Rezin king of Amram and Pekah son of Remaliah against Judah.
38 Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda, birnin mahaifinsa. Ahaz ɗansa kuma ya gāje shi.
And Jotham lies with his fathers, and is buried with his fathers in the city of his father David, and his son Ahaz reigns in his stead.