< 2 Sarakuna 15 >

1 A shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Yerobowam sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya, sarkin Yahuda ya fara mulki.
In the twenty and seventh year of Jerobo'am the king of Israel became 'Azaryah, the son of Amazyah king of Judah, king.
2 Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya daga Urushalima.
Sixteen years old was he when he became king, and two and fifty years did he reign in Jerusalem. And his mother's name was Yecholyahu of Jerusalem.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
And he did what is right in the eyes of the Lord, in accordance with all that Amazyahu his father had done;
4 Amma bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane kuwa suka yi ta yin hadaya da ƙona turare a can.
Nevertheless the high-places were not removed: as yet the people sacrificed and burnt incense on the high-places.
5 Ubangiji ya sa wa sarki ciwon kuturta har mutuwarsa, ya kuma zauna a keɓe. Yotam ɗan sarki, shi ne ya gudanar da sha’anin fada, ya kuma shugabanci mutanen ƙasar.
And the Lord afflicted the king with leprosy, and he was a leper unto the day of his death, and he dwelt in the leper-house. And Jotham the king's son was over the house, [and] judged the people of the land.
6 Game da sauran ayyukan mulkin Azariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
And the rest of the acts of 'Azaryahu, and all that he did, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Judah.
7 Azariya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi kusa da su a Birnin Dawuda. Yotam ɗansa, kuma ya gāje shi.
And 'Azaryah slept with his fathers; and they buried him with his fathers in the city of David: and Jotham his son became king in his stead.
8 A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Zakariya ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki wata shida.
In the thirty and eighth year of 'Azaryahu the king of Judah became Zechariah the son of Jerobo'am king over Israel in Samaria [for] six months.
9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi. Bai bar aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi ba.
And he did what is evil in the eyes of the Lord, as his fathers had done: he departed not from the sins of Jerobo'am the son of Nebat, who induced Israel to sin.
10 Sai Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zakariya maƙarƙashiya. Ya tasam masa a gaban jama’a, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
And Shallum the son of Yabesh conspired against him, and smote him before the people, and put him to death, and became king in his stead.
11 Game da sauran ayyukan mulkin Zakariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the acts of Zechariah, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Israel.
12 Ta haka maganar Ubangiji da ya yi wa Yehu ta cika, wadda ya ce, “Zuriyarka za tă zauna a kursiyin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
This was the word of the Lord which he spoke unto Jehu, saying, Sons of the fourth generation shall sit after thee on the throne of Israel. And so it came to pass.
13 Shallum ɗan Yabesh ya zama sarki a shekara ta talatin da tara ta mulkin Uzziya sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki na wata ɗaya a Samariya.
Shallum the son of Yabesh became king in the nine and thirtieth year of 'Uzziyah the king of Judah; and he reigned for the space of one month in Samaria.
14 Sa’an nan Menahem ɗan Gadi ya gangara daga Tirza ya haura zuwa Samariya. Ya tasam wa Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
Then went up Menachem the son of Gadi from Thirzah, and came to Samaria, and smote Shallum the son of Yabesh in Samaria, and put him to death, and became king in his stead.
15 Game da sauran ayyukan mulkin Shallum, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the acts of Shallum, and his conspiracy which he made, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Israel.
16 A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
At that time did Menachem smite Thiphsach, and all that was therein, and its territory from Thirzah; because they opened not to him, he smote it; and all the pregnant women therein he ripped up.
17 A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya zama sarkin Isra’ila, ya yi mulki a Samariya shekara goma.
In the nine and thirtieth year of 'Azaryah the king of Judah became Menachem the son of Gadi king over Israel, [for] ten years, in Samaria.
18 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A duk tsawon mulkinsa, bai rabu da zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya sa Isra’ila suka aikata ba.
And he did what is evil in the eyes of the Lord: he departed not from the sins of Jerobo'am the son of Nebat, who induced Israel to sin, all his days.
19 Sai Ful sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar hari, Menahem kuwa ya ba shi talenti dubu na azurfa don yă sami goyon bayansa, yă kuma ƙarfafa kahuwa mulkin.
[Then] came Pul the king of Assyria against the land: and Menachem gave Pul a thousand talents of silver, that his hand might be with him to strengthen the kingdom in his hand.
20 Menahem ya tara kuɗin ne ta hanyar haraji a Isra’ila inda ya sa kowane attajiri ya ba da shekel hamsin don a ba sarkin Assuriya. Sa’an nan sarkin Assuriya ya janye, bai ƙara kasance a ƙasar ba.
And Menachem exacted the money from all Israel, from all the mighty men of the army, to give to the king of Assyria, fifty shekels of silver from every man; and the king of Assyria then returned and stayed not there in the land.
21 Game da sauran ayyukan mulkin Menahem, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the acts of Menachem, and all that he did, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Israel.
22 Menahem ya huta tare da kakanninsa. Fekahiya ɗansa kuma ya gāje shi.
And Menachem slept with his fathers; and Pekachyah his son became king in his stead.
23 A shekara ta hamsin ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekara biyu.
In the fiftieth year of 'Azaryah the king of Judah became Pekachyah the son of Menachem king over Israel in Samaria, [for] two years.
24 Fekahiya ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat wanda ya sa Isra’ila ya aikata ba.
And he did what is evil m the eyes of the Lord: he departed not from the sins of Jerobo'am the son of Nebat, who induced Israel to sin.
25 Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
And Pekach the son of Remalyahu, an officer of his, conspired against him, and smote him in Samaria, in the fortress of the king's house, with the aid of Argob and the Aryeh, and with him were fifty men of the children of the Gil'adites: and he put him to death, and became king in his stead.
26 Game da sauran ayyukan mulkin Fekahiya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the acts of Pekachyah, and all that he did, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Israel.
27 A shekara ta hamsin da biyu ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Feka ɗan Remaliya ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya yi mulki shekara ashirin.
In the fifty-second year of 'Azaryah the king of Judah became Pekach the son of Remalyahu king over Israel in Samaria, [for] twenty years.
28 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai kauce wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta yi ba.
And he did what is evil in the eyes of the Lord: he departed not from the sins of Jerobo'am the son of Nebat, who induced Israel to sin.
29 A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
In the days of Pekach the king of Israel came Tiglath-pilesser the king of Assyria, and took 'Iyon, and Abel-beth, ma'achah, and Yanoach, and Kedesh, and Chazor, and Gil'ad, and Galilee, all the land of Naphtali, and led them away as exiles to Assyria.
30 Sa’an nan Hosheya ɗan Ela ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya. Ya fāɗa masa ya kuma kashe shi, sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki a shekara ta shirin ta mulkin Yotam ɗan Uzziya.
And Hoshea' the son of Elah made a conspiracy against Pekach the son of Remalyahu, and smote him, and put him to death, and became king in his stead, in the twentieth year of Jotham the son of 'Uzziyah.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Feka da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the acts of Pekach, and all that he did, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Israel.
32 A shekara ta biyu ta mulkin Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Uzziya sarkin Yahuda ya fara mulki.
In the second year of Pekach the son of Remalyahu the king of Israel became Jotham, the son of 'Uzziyah the king of Judah, king.
33 Ya zama sarki yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
Five and twenty years old was he when he became king, and sixteen years did he reign in Jerusalem. And his mother's name was Yerusha, the daughter of Zadok.
34 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa Uzziya ya yi.
And he did what is right in the eyes of the Lord: in accordance with all that 'Uzziyahu his father had done, [so] did he.
35 Duk da haka, bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙona turare a can. Yotam ya sāke gina Ƙofar Bisa ta haikalin Ubangiji.
Nevertheless, the high-places were not removed: as yet the people sacrificed and burnt incense on the high-places. He it was that built the upper gate of the house of the Lord.
36 Game da sauran ayyukan mulkin Yotam da aikin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Now the rest of the acts of Jotham, and all that he did, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Judah.
37 (A kwanakin nan Ubangiji ya fara aikan Rezin sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, su yi gāba da Yahuda.)
In those days began the Lord to send against Judah Rezin the king of Syria, and Pekach the son of Remalyahu.
38 Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda, birnin mahaifinsa. Ahaz ɗansa kuma ya gāje shi.
And Jotham slept with his fathers, and was buried with his fathers in the city of David his father: and Achaz his son became king in his stead.

< 2 Sarakuna 15 >