< 2 Sarakuna 14 >

1 A shekara ta biyu ta mulkin Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila, Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya fara mulki.
Amasías, hijo de Joás, llegó a ser rey de Judá en el segundo año del reinado de Joás, hijo de Joacaz, rey de Israel.
2 Ya zama sarki yana da shekaru ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin, mutuniyar Urushalima.
Tenía veinticinco años cuando llegó a ser rey, y reinó en Jerusalén durante veintinueve años. Su madre se llamaba Joadán de Jerusalén.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, sai dai ba kamar kakansa Dawuda ba. A kome dai ya bi gurbin mahaifinsa Yowash.
Hizo lo que era correcto a los ojos del Señor, pero no de la misma manera que su antepasado David. Hizo todo como lo había hecho su padre Joás.
4 Ba a dai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙone turare a can.
Pero los altares paganos no fueron destruidos. El pueblo seguía sacrificando y presentando holocaustos en esos lugares.
5 Bayan masarauta ta kahu a hannunsa, sai ya kashe fadawan da suka kashe mahaifinsa sarki.
Una vez que estuvo seguro en el trono, ejecutó a los funcionarios que habían asesinado a su padre el rey.
6 Duk da haka bai kashe’ya’yan masu kisan ba, bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda laifin’ya’ya ba, ko kuma’ya’ya saboda laifin iyayensu ba, kowa zai mutu don zunubansa.”
Pero no ejecutó a los hijos de los asesinos, siguiendo el mandato del Señor en la ley de Moisés: “Los padres no deben morir por los pecados de sus hijos, ni los hijos deben morir por los pecados de sus padres. Cada uno debe morir por su propio pecado”.
7 Shi ne kuma wanda ya ci mutanen Edom dubu goma a yaƙi, a Kwarin Gishiri, ya kuma ci Sela da yaƙi, ya ba ta suna Yokteyel, sunan da ake kiranta har wa yau.
Amasías mató a diez mil edomitas en el Valle de la Sal. Atacó y capturó Sela y la rebautizó como Joktheel, que es como se llama hasta hoy.
8 Sai Amaziya ya aika’yan aika wurin Yehowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, yana tsokanarsa cewa, “Zo, mu sadu fuska da fuska.”
Amasías envió mensajeros al rey de Israel, Joás, hijo de Joacaz, hijo de Jehú, diciéndole: “Luchemos, cara a cara!”
9 Amma Yehowash sarkin Isra’ila ya mai da martani wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata’yar ƙaya a kurmin Lebanon ta aika da saƙo wurin itacen al’ul a Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Amma wani naman jeji ya zo ya tattake ƙayar.
Joás, rey de Israel, respondió a Amasías, rey de Judá: “En el Líbano, un cardo envió un mensaje a un cedro, diciendo: ‘Dale tu hija como esposa a mi hijo’. Pero pasó un animal salvaje del Líbano y pisoteó el cardo.
10 Tabbatacce ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana ɗaga kai. To, ka gode da darajar da ka samu, amma ka zauna a gida! Don me kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da kuma ta Yahuda?”
Puede que hayas derrotado a Edom. Ahora te has vuelto arrogante. Quédate en casa y disfruta de tu victoria. ¿Por qué provocar problemas que te harán caer a ti, y a Judá contigo?”
11 Amma Amaziya bai saurara ba, saboda haka Yehowash sarkin Isra’ila ya kai masa hari. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh.
Pero Amasías se negó a escuchar, así que Joás, rey de Israel, vino a atacarlo. Él y Amasías, rey de Judá, se encontraron cara a cara en Bet Semes, en Judá.
12 Isra’ila suka fatattaki Yahuda, kowa kuwa ya tsere zuwa gidansa.
El ejército de Judá fue derrotado por Israel y huyó a su casa.
13 Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya, a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya tafi Urushalima ya rushe katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, ratarta ta kai wajen ƙafa ɗari shida.
Joás, rey de Israel, capturó a Amasías, rey de Judá, hijo de Joás, hijo de Ocozías, en Bet Semes. Entonces Joás atacó Jerusalén y derribó la muralla de la ciudad desde la puerta de Efraín hasta la puerta de la Esquina, de unos cuatrocientos codos de longitud.
14 Ya kwashi ɗaukan zinariya da azurfa da duk kayan da aka samu a haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan. Ya kuma kwashi bayi sa’an nan ya koma Samariya.
Se llevó todo el oro y la plata, y todos los objetos que se encontraban en el Templo del Señor y en los tesoros del palacio real, y también algunos rehenes. Luego regresó a Samaria.
15 Game da sauran ayyukan mulkin Yehowash, abin da ya yi da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙinsa da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
El resto de lo que sucedió en el reinado de Joás, todo lo que hizo y sus grandes logros y su guerra con Amasías, rey de Judá, están registrados en el Libro de las Crónicas de los Reyes de Israel.
16 Ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Samariya tare da sarakunan Isra’ila. Yerobowam ɗansa, ya kuma gāje shi.
Joás murió y fue enterrado en Samaria con los reyes de Israel. Su hijo Jeroboam le sucedió como rey.
17 Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya yi shekaru goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
Amasías, hijo de Joás, rey de Judá, vivió quince años más después de la muerte de Joás, hijo de Joacaz, rey de Israel.
18 Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
El resto de los acontecimientos que ocurrieron en el reinado de Amasías están registrados en el Libro de las Crónicas de los Reyes de Judá.
19 Suka ƙulla masa maƙarƙashiya a Urushalima, ya gudu zuwa Lakish, amma suka aika har Lakish aka kashe shi a can.
Una conspiración contra Amasías tuvo lugar en Jerusalén, y él huyó a Laquis. Pero se enviaron hombres tras él y lo asesinaron allí.
20 Aka ɗauko shi a kan doki aka kawo shi Urushalima, aka kuwa binne shi tare da kakanninsa, a Birnin Dawuda.
Lo trajeron de vuelta a caballo y lo enterraron en Jerusalén con sus antepasados en la Ciudad de David.
21 Sa’an nan dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda yake ɗan shekaru goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
Entonces todo el pueblo de Judá nombró rey al hijo de Amasías, Azarías, para que reemplazara a su padre. Azarías tenía dieciséis años.
22 Shi ne ya sāke gina Elat, ya kuma maido da ita a hannun Yahuda bayan Amaziya ya huta da kakanninsa.
Azarías reconquistó Elat para Judá y la reconstruyó después de la muerte de su padre.
23 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehowash sarkin Isra’ila ya zama sarki a Samariya, ya kuma yi mulki na shekaru arba’in da ɗaya.
Jeroboam, hijo de Joás, llegó a ser rey de Israel en el año quince del reinado de Amasías, hijo de Joás, rey de Judá. Reinó en Samaria durante cuarenta y un años.
24 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji bai kuwa kauce wa duk zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
Hizo lo malo a los ojos del Señor y no puso fin a todos los pecados que Jeroboam, hijo de Nabat, había hecho cometer a Israel.
25 Shi ne ya maido da iyakokin Isra’ila daga Lebo Hamat zuwa Tekun Araba, bisa ga maganar Ubangiji, Allah na Isra’ila, da ya yi ta bakin bawansa Yunana ɗan Amittai, annabi daga Gat-Hefer.
Restituyó la frontera de Israel a donde estaba, desde Lebó-Jamat hasta el Mar de la Arabá, como el Señor, el Dios de Israel, había dicho por medio de su siervo Jonás, hijo de Amitai, el profeta, que venía de Gat-Jefer.
26 Ubangiji ya ga irin muguwar wahalar da ta shafi kowa a Isra’ila, ko bawa ko’yantacce, babu mai taimakonsu.
El Señor había visto lo mucho que estaban sufriendo los israelitas, tanto los esclavos como los libres. Nadie estaba allí para ayudar a Israel.
27 Da yake kuma Ubangiji bai ce zai shafe sunan Isra’ila daga fuskar duniya ba, sai ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yowash.
Sin embargo, como el Señor había dicho que no eliminaría a Israel, lo salvó por medio de Jeroboam, hijo de Joás.
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yerobowam, da dukan abin da ya yi, da yaƙe-yaƙen da ya yi, haɗe da sāke ƙwato wa Isra’ila Damaskus da Hamat waɗanda suke a hannun Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
El resto de lo que sucedió en el reinado de Jeroboam, todo lo que hizo, sus grandes logros y las batallas que libró, y cómo recuperó para Israel tanto Damasco como Jamat, están registrados en el Libro de las Crónicas de los Reyes de Israel.
29 Yerobowam ya huta da kakanninsa, sarakunan Isra’ila. Zakariya ɗansa kuwa ya gāje shi.
Jeroboam murió y fue enterrado con los reyes de Israel. Su hijo Zacarías le sucedió como rey.

< 2 Sarakuna 14 >