< 2 Sarakuna 14 >

1 A shekara ta biyu ta mulkin Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila, Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya fara mulki.
V drugem letu Jehoáša, Joaházovega sina, Izraelovega kralja, je zakraljeval Amacjá, sin Judovega kralja Joáša.
2 Ya zama sarki yana da shekaru ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin, mutuniyar Urushalima.
Petindvajset let je bil star, ko je začel kraljevati in v Jeruzalemu je kraljeval devetindvajset let. Ime njegove matere je bilo Joadána iz Jeruzalema.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, sai dai ba kamar kakansa Dawuda ba. A kome dai ya bi gurbin mahaifinsa Yowash.
Delal je to, kar je bilo pravilno v Gospodovih očeh, vendar ne tako kakor njegov oče David. Delal je glede na vse stvari, kakor jih je delal njegov oče Joáš.
4 Ba a dai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙone turare a can.
Vendar visoki kraji niso bili odstranjeni. Ljudstvo je na visokih krajih še vedno žrtvovalo in zažigalo kadilo.
5 Bayan masarauta ta kahu a hannunsa, sai ya kashe fadawan da suka kashe mahaifinsa sarki.
Takoj, ko je bilo kraljestvo v njegovi roki potrjeno, se je pripetilo, da je umoril svoja služabnika, ki sta umorila kralja, njegovega očeta.
6 Duk da haka bai kashe’ya’yan masu kisan ba, bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda laifin’ya’ya ba, ko kuma’ya’ya saboda laifin iyayensu ba, kowa zai mutu don zunubansa.”
Toda otrok morilcev ni usmrtil, glede na to, kakor je pisano v knjigi Mojzesove postave, v kateri je Gospod zapovedal, rekoč: »Očetje ne bodo usmrčeni zaradi otrok niti ne bodo otroci usmrčeni zaradi očetov, temveč bo vsak človek usmrčen zaradi svojega lastnega greha.«
7 Shi ne kuma wanda ya ci mutanen Edom dubu goma a yaƙi, a Kwarin Gishiri, ya kuma ci Sela da yaƙi, ya ba ta suna Yokteyel, sunan da ake kiranta har wa yau.
Izmed Edóma jih je v solni dolini usmrtil deset tisoč in v vojni zavzel Selo in njeno ime imenoval Jokteél do današnjega dne.
8 Sai Amaziya ya aika’yan aika wurin Yehowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, yana tsokanarsa cewa, “Zo, mu sadu fuska da fuska.”
Potem je Amacjá poslal poslance k Jehoášu, sinu Joaháza, sinu Jehúja, Izraelovega kralja, rekoč: »Pridite, drug drugemu poglejmo v obraz.«
9 Amma Yehowash sarkin Isra’ila ya mai da martani wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata’yar ƙaya a kurmin Lebanon ta aika da saƙo wurin itacen al’ul a Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Amma wani naman jeji ya zo ya tattake ƙayar.
Izraelov kralj Jehoáš je poslal k Judovemu kralju Amacjáju, rekoč: »Osat, ki je bil na Libanonu, je poslal k cedri, ki je bila na Libanonu, rekoč: ›Daj svojo hčer mojemu sinu za ženo, ‹ pa je tam mimo šla divja zver, ki je bila na Libanonu in pomendrala osat.
10 Tabbatacce ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana ɗaga kai. To, ka gode da darajar da ka samu, amma ka zauna a gida! Don me kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da kuma ta Yahuda?”
Zares si udaril Edóma in tvoje srce te je povzdignilo. Uživaj v tem in ostani doma, kajti zakaj bi se vmešaval v svojo bolečino, da bi padel ti in Juda s teboj?«
11 Amma Amaziya bai saurara ba, saboda haka Yehowash sarkin Isra’ila ya kai masa hari. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh.
Toda Amacjá ni hotel poslušati. Zato je Izraelov kralj Jehoáš odšel gor in on in Judov kralj Amacjá sta si drug drugemu pogledala v obraz pri Bet Šemešu, ki pripada Judu.
12 Isra’ila suka fatattaki Yahuda, kowa kuwa ya tsere zuwa gidansa.
Juda je bil premagan pred Izraelom in pobegnili so vsak mož k svojim šotorom.
13 Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya, a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya tafi Urushalima ya rushe katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, ratarta ta kai wajen ƙafa ɗari shida.
Izraelov kralj Jehoáš je ujel Judovega kralja Amacjája, sina Joáša, sina Ahazjája, pri Bet Šemešu, prišel v Jeruzalem in porušil jeruzalemsko obzidje od Efrájimskih velikih vrat do Vogalnih velikih vrat, štiristo komolcev.
14 Ya kwashi ɗaukan zinariya da azurfa da duk kayan da aka samu a haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan. Ya kuma kwashi bayi sa’an nan ya koma Samariya.
Vzel je vse zlato, srebro in vse posode, ki so se našle v Gospodovi hiši, v zakladnicah kraljeve hiše in talce ter se vrnil v Samarijo.
15 Game da sauran ayyukan mulkin Yehowash, abin da ya yi da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙinsa da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Torej ostala izmed Jehoáševih dejanj, ki jih je storil, njegova moč in kako se je boril z Judovim kraljem Amacjájem, mar niso zapisana v kroniški knjigi Izraelovih kraljev?
16 Ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Samariya tare da sarakunan Isra’ila. Yerobowam ɗansa, ya kuma gāje shi.
Jehoáš je zaspal s svojimi očeti in z Izraelovimi kralji je bil pokopan v Samariji in namesto njega je zakraljeval njegov sin Jerobeám.
17 Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya yi shekaru goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
Judov kralj Amacjá, Joášev sin, je po smrti Jehoáša, Izraelovega kralja, Joaházovega sina, živel petnajst let.
18 Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Ostala Amacjájeva dela, mar niso zapisana v kroniški knjigi Judovih kraljev?
19 Suka ƙulla masa maƙarƙashiya a Urushalima, ya gudu zuwa Lakish, amma suka aika har Lakish aka kashe shi a can.
Torej zoper njega so v Jeruzalemu skovali zaroto in pobegnil je v Lahíš, toda za njim so poslali v Lahíš in ga tam usmrtili.
20 Aka ɗauko shi a kan doki aka kawo shi Urushalima, aka kuwa binne shi tare da kakanninsa, a Birnin Dawuda.
Prinesli so ga na konjih in pokopan je bil s svojimi očeti v Jeruzalemu, v Davidovem mestu.
21 Sa’an nan dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda yake ɗan shekaru goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
Vse Judovo ljudstvo je vzelo Azarjája, ki je bil star šestnajst let in ga postavilo [za] kralja namesto njegovega očeta Amacjája.
22 Shi ne ya sāke gina Elat, ya kuma maido da ita a hannun Yahuda bayan Amaziya ya huta da kakanninsa.
Zgradil je Elát in ga povrnil Judu, potem je kralj zaspal s svojimi očeti.
23 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehowash sarkin Isra’ila ya zama sarki a Samariya, ya kuma yi mulki na shekaru arba’in da ɗaya.
V petnajstem letu Judovega kralja Amacjája, Joáševega sina, je v Samariji začel kraljevati Jerobeám, Jehoášev sin, Izraelov kralj in kraljeval je enainštirideset let.
24 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji bai kuwa kauce wa duk zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
Počel je to, kar je bilo zlo v Gospodovih očeh. Ni se oddvojil od vseh grehov Nebátovega sina Jerobeáma, ki je Izraela pripravil, da greši.
25 Shi ne ya maido da iyakokin Isra’ila daga Lebo Hamat zuwa Tekun Araba, bisa ga maganar Ubangiji, Allah na Isra’ila, da ya yi ta bakin bawansa Yunana ɗan Amittai, annabi daga Gat-Hefer.
Povrnil je Izraelovo pokrajino od vstopa v Hamát do morja ravnine, glede na besedo od Gospoda, Izraelovega Boga, ki jo je govoril po roki svojega služabnika Jona, Amitájevega sina, preroka, ki je bil iz Gat Heferja.
26 Ubangiji ya ga irin muguwar wahalar da ta shafi kowa a Isra’ila, ko bawa ko’yantacce, babu mai taimakonsu.
Kajti Gospod je videl Izraelovo stisko, da je bila ta zelo grenka, kajti tam ni bilo nobenega zaprtega, niti nobeden ni ostal, niti ni bilo pomočnika za Izrael.
27 Da yake kuma Ubangiji bai ce zai shafe sunan Isra’ila daga fuskar duniya ba, sai ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yowash.
Gospod ni rekel, da bo Izraelovo ime izbrisal izpod neba, temveč jih je rešil po roki Jehoáševega sina Jerobeáma.
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yerobowam, da dukan abin da ya yi, da yaƙe-yaƙen da ya yi, haɗe da sāke ƙwato wa Isra’ila Damaskus da Hamat waɗanda suke a hannun Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Torej preostala izmed Jerobeámovih dejanj in vse, kar je storil in njegova moč, kako se je bojeval in kako je za Izrael obnovil Damask in Hamát, ki je pripadal Judu, mar niso zapisana v kroniški knjigi Izraelovih kraljev?
29 Yerobowam ya huta da kakanninsa, sarakunan Isra’ila. Zakariya ɗansa kuwa ya gāje shi.
Jerobeám je zaspal s svojimi očeti, z Izraelovimi kralji in namesto njega je zakraljeval njegov sin Zaharija.

< 2 Sarakuna 14 >