< 2 Sarakuna 14 >

1 A shekara ta biyu ta mulkin Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila, Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya fara mulki.
Druge godine carovanja Joasa sina Joahazova nad Izrailjem zacari se Amasija sin Joasov nad Judom.
2 Ya zama sarki yana da shekaru ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin, mutuniyar Urushalima.
Bijaše mu dvadeset i pet godina kad poèe carovati, i carova dvadeset i devet godina u Jerusalimu. Materi mu bješe ime Joadana, iz Jerusalima.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, sai dai ba kamar kakansa Dawuda ba. A kome dai ya bi gurbin mahaifinsa Yowash.
I èinjaše što je pravo pred Gospodom, ali ne kao David otac njegov; sasvijem èinjaše onako kako je èinio otac njegov Joas.
4 Ba a dai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙone turare a can.
Jer visine ne biše oborene: narod još prinošaše žrtve i kaðaše na visinama.
5 Bayan masarauta ta kahu a hannunsa, sai ya kashe fadawan da suka kashe mahaifinsa sarki.
A kad se utvrdi carstvo u ruci njegovoj, on pobi sluge svoje koje su ubile cara oca njegova.
6 Duk da haka bai kashe’ya’yan masu kisan ba, bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda laifin’ya’ya ba, ko kuma’ya’ya saboda laifin iyayensu ba, kowa zai mutu don zunubansa.”
Ali sinova tijeh krvnika ne pobi, kao što piše u knjizi zakona Mojsijeva, gdje je zapovjedio Gospod govoreæi: ocevi da ne ginu za sinove niti sinovi za oceve, nego svaki za svoj grijeh neka gine.
7 Shi ne kuma wanda ya ci mutanen Edom dubu goma a yaƙi, a Kwarin Gishiri, ya kuma ci Sela da yaƙi, ya ba ta suna Yokteyel, sunan da ake kiranta har wa yau.
On pobi deset tisuæa Edomaca u slanoj dolini, i uze Selu ratom, i prozva je Jokteil, koje osta do danas.
8 Sai Amaziya ya aika’yan aika wurin Yehowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, yana tsokanarsa cewa, “Zo, mu sadu fuska da fuska.”
Tada posla Amasija poslanike k Joasu sinu Joahaza sina Jujeva, caru Izrailjevu, i reèe: doði da se ogledamo.
9 Amma Yehowash sarkin Isra’ila ya mai da martani wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata’yar ƙaya a kurmin Lebanon ta aika da saƙo wurin itacen al’ul a Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Amma wani naman jeji ya zo ya tattake ƙayar.
A Joas car Izrailjev posla k Amasiji caru Judinu i poruèi mu: trn na Livanu posla ka kedru na Livanu, i poruèi: daj svoju kæer sinu mojemu za ženu; ali naiðe zvijerje Livansko, i izgazi trn.
10 Tabbatacce ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana ɗaga kai. To, ka gode da darajar da ka samu, amma ka zauna a gida! Don me kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da kuma ta Yahuda?”
Pobio si Edomce, pa se ponese srce tvoje; hvali se, i sjedi kod kuæe svoje; zašto bi se zapletao u zlo da padneš i ti i Juda s tobom?
11 Amma Amaziya bai saurara ba, saboda haka Yehowash sarkin Isra’ila ya kai masa hari. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh.
Ali ne posluša Amasija; i podiže se Joas car Izrailjev, i ogledaše se, on i Amasija car Judin, u Vetsemesu Judinu.
12 Isra’ila suka fatattaki Yahuda, kowa kuwa ya tsere zuwa gidansa.
Ali Judu razbi Izrailj, te pobjegoše svaki k svojemu šatoru.
13 Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya, a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya tafi Urushalima ya rushe katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, ratarta ta kai wajen ƙafa ɗari shida.
A Amasiju cara Judina, sina Joasa sina Ohozijina, uhvati Joas car Izrailjev u Vetsemesu; potom doðe u Jerusalim i obori zid Jerusalimski od vrata Jefremovijeh do vrata na uglu, èetiri stotine lakata.
14 Ya kwashi ɗaukan zinariya da azurfa da duk kayan da aka samu a haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan. Ya kuma kwashi bayi sa’an nan ya koma Samariya.
I uze sve zlato i srebro i sve posuðe što se naðe u domu Gospodnjem i u riznicama doma careva, i taoce, pa se vrati u Samariju.
15 Game da sauran ayyukan mulkin Yehowash, abin da ya yi da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙinsa da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
A ostala djela Joasova, što je uèinio, i junaštva njegova, i kako je vojevao s Amasijom carem Judinijem, nije li to zapisano u dnevniku careva Izrailjevijeh?
16 Ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Samariya tare da sarakunan Isra’ila. Yerobowam ɗansa, ya kuma gāje shi.
I poèinu Joas kod otaca svojih, i bi pogreben u Samariji kod careva Izrailjevijeh, a na njegovo se mjesto zacari Jerovoam sin njegov.
17 Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya yi shekaru goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
Amasija pak sin Joasov car Judin poživje petnaest godina po smrti Joasa sina Joahazova, cara Izrailjeva.
18 Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
A ostala djela Amasijina nijesu li zapisana u dnevniku careva Judinijeh?
19 Suka ƙulla masa maƙarƙashiya a Urushalima, ya gudu zuwa Lakish, amma suka aika har Lakish aka kashe shi a can.
I digoše bunu na nj u Jerusalimu, te pobježe u Lahis, a oni poslaše za njim u Lahis i ubiše ga ondje.
20 Aka ɗauko shi a kan doki aka kawo shi Urushalima, aka kuwa binne shi tare da kakanninsa, a Birnin Dawuda.
A odande ga donesoše na konjma, i bi pogreben u Jerusalimu kod otaca svojih u gradu Davidovu.
21 Sa’an nan dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda yake ɗan shekaru goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
Tada sav narod Judin uze Azariju, kome bijaše šesnaest godina, i zacariše ga na mjesto oca njegova Amasije.
22 Shi ne ya sāke gina Elat, ya kuma maido da ita a hannun Yahuda bayan Amaziya ya huta da kakanninsa.
On sazida Elat povrativ ga Judi pošto car poèinu kod otaca svojih.
23 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehowash sarkin Isra’ila ya zama sarki a Samariya, ya kuma yi mulki na shekaru arba’in da ɗaya.
Godine petnaeste carovanja Amasije sina Joasova nad Judom zacari se Jerovoam sin Joasov nad Izrailjem u Samariji, i carova èetrdeset i jednu godinu.
24 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji bai kuwa kauce wa duk zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
I èinjaše što je zlo pred Gospodom i ne otstupi ni od jednoga grijeha Jerovoama sina Navatova kojima navede na grijeh Izrailja.
25 Shi ne ya maido da iyakokin Isra’ila daga Lebo Hamat zuwa Tekun Araba, bisa ga maganar Ubangiji, Allah na Isra’ila, da ya yi ta bakin bawansa Yunana ɗan Amittai, annabi daga Gat-Hefer.
On povrati meðe Izrailjeve od Emata do mora uz polje, po rijeèi Gospoda Boga Izrailjeva, koju reèe preko sluge svojega Jone sina Amatijina, proroka iz Gatefera.
26 Ubangiji ya ga irin muguwar wahalar da ta shafi kowa a Isra’ila, ko bawa ko’yantacce, babu mai taimakonsu.
Jer Gospod vidje da je u ljutoj nevolji Izrailj, i da nema ništa ni od uhvaæenoga ni od ostavljenoga, i da nema nikoga da pomože Izrailju.
27 Da yake kuma Ubangiji bai ce zai shafe sunan Isra’ila daga fuskar duniya ba, sai ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yowash.
I ne bješe rekao Gospod da zatre ime Izrailjevo pod nebom; zato ih izbavi preko Jerovoama sina Joasova.
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yerobowam, da dukan abin da ya yi, da yaƙe-yaƙen da ya yi, haɗe da sāke ƙwato wa Isra’ila Damaskus da Hamat waɗanda suke a hannun Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
A ostala djela Jerovoamova, i sve što je èinio, i junaštva njegova, kako je vojevao i kako je povratio Damasak i Emat od Jude Izrailju, nije li to zapisano u dnevniku careva Izrailjevijeh?
29 Yerobowam ya huta da kakanninsa, sarakunan Isra’ila. Zakariya ɗansa kuwa ya gāje shi.
Potom poèinu Jerovoam kod otaca svojih, careva Izrailjevijeh, a na njegovo se mjesto zacari Zaharija sin njegov.

< 2 Sarakuna 14 >