< 2 Sarakuna 14 >

1 A shekara ta biyu ta mulkin Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila, Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya fara mulki.
Ngomnyaka wesibili kaJowashi indodana kaJehowazi, inkosi yakoIsrayeli, uAmaziya indodana kaJowashi inkosi yakoJuda waba yinkosi.
2 Ya zama sarki yana da shekaru ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin, mutuniyar Urushalima.
Wayeleminyaka engamatshumi amabili lanhlanu lapho esiba yinkosi; wabusa iminyaka engamatshumi amabili lesificamunwemunye eJerusalema. Lebizo likanina lalinguJehowadani weJerusalema.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, sai dai ba kamar kakansa Dawuda ba. A kome dai ya bi gurbin mahaifinsa Yowash.
Wasesenza okulungileyo emehlweni eNkosi, kodwa kungenjengoDavida uyise; wenza njengakho konke uJowashi uyise akwenzayo.
4 Ba a dai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙone turare a can.
Loba kunjalo indawo eziphakemeyo kazisuswanga; abantu babelokhu benikela imihlatshelo betshisa impepha endaweni eziphakemeyo.
5 Bayan masarauta ta kahu a hannunsa, sai ya kashe fadawan da suka kashe mahaifinsa sarki.
Kwasekusithi umbuso wakhe usuqinisiwe esandleni sakhe, watshaya inceku zakhe ezazitshaye inkosi uyise.
6 Duk da haka bai kashe’ya’yan masu kisan ba, bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda laifin’ya’ya ba, ko kuma’ya’ya saboda laifin iyayensu ba, kowa zai mutu don zunubansa.”
Kodwa abantwana bababulali kababulalanga, njengokubhaliweyo ogwalweni lomlayo kaMozisi lapho iNkosi eyalaya khona isithi: Oyise kabayikubulawa ngenxa yabantwana, labantwana kabayikubulawa ngenxa yaboyise, kodwa wonke umuntu uzabulawelwa isono sakhe.
7 Shi ne kuma wanda ya ci mutanen Edom dubu goma a yaƙi, a Kwarin Gishiri, ya kuma ci Sela da yaƙi, ya ba ta suna Yokteyel, sunan da ake kiranta har wa yau.
Yena wasetshaya amaEdoma azinkulungwane ezilitshumi esihotsheni setshwayi, wathumba iSela ngempi, wabiza ibizo layo ngokuthi yiJokhitheyeli, kuze kube lamuhla.
8 Sai Amaziya ya aika’yan aika wurin Yehowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, yana tsokanarsa cewa, “Zo, mu sadu fuska da fuska.”
Khona uAmaziya wathuma izithunywa kuJehowashi indodana kaJehowahazi indodana kaJehu, inkosi yakoIsrayeli, esithi: Woza sikhangelane ubuso ngobuso.
9 Amma Yehowash sarkin Isra’ila ya mai da martani wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata’yar ƙaya a kurmin Lebanon ta aika da saƙo wurin itacen al’ul a Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Amma wani naman jeji ya zo ya tattake ƙayar.
UJehowashi inkosi yakoIsrayeli wasethumela kuAmaziya inkosi yakoJuda esithi: Ukhula oluhlabayo oluseLebhanoni lwathumela emsedarini oseLebhanoni lusithi: Nika indodakazi yakho endodaneni yami ibe ngumkayo; kwasekusedlula isilo seganga esiseLebhanoni, salugxoba ukhula oluhlabayo.
10 Tabbatacce ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana ɗaga kai. To, ka gode da darajar da ka samu, amma ka zauna a gida! Don me kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da kuma ta Yahuda?”
Uyitshayile lokuyitshaya iEdoma, inhliziyo yakho isikuphakamisile; dumiseka, uhlale endlini yakho; ngoba kungani uzivusela ububi ukuze uwe wena loJuda kanye lawe?
11 Amma Amaziya bai saurara ba, saboda haka Yehowash sarkin Isra’ila ya kai masa hari. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh.
Kodwa uAmaziya kezwanga. Ngakho uJehowashi inkosi yakoIsrayeli wenyuka, yena-ke loAmaziya inkosi yakoJuda bakhangelana ubuso ngobuso eBeti-Shemeshi eyakoJuda.
12 Isra’ila suka fatattaki Yahuda, kowa kuwa ya tsere zuwa gidansa.
UJuda wasetshaywa phambi kukaIsrayeli; basebebaleka, ngulowo lalowo waya ethenteni lakhe.
13 Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya, a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya tafi Urushalima ya rushe katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, ratarta ta kai wajen ƙafa ɗari shida.
UJehowashi inkosi yakoIsrayeli wasembamba uAmaziya inkosi yakoJuda, indodana kaJehowashi indodana kaAhaziya, eBeti-Shemeshi; wafika eJerusalema, wadilizela phansi umduli weJerusalema, kusukela esangweni lakoEfrayimi kusiya esangweni lengonsi, ingalo ezingamakhulu amane.
14 Ya kwashi ɗaukan zinariya da azurfa da duk kayan da aka samu a haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan. Ya kuma kwashi bayi sa’an nan ya koma Samariya.
Wasethatha lonke igolide lesiliva, lezitsha zonke ezatholakala endlini kaJehova lezendlini zenotho zendlu yenkosi, kanye labayisibambiso, wasebuyela eSamariya.
15 Game da sauran ayyukan mulkin Yehowash, abin da ya yi da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙinsa da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Ezinye-ke zezindaba zikaJehowashi azenzayo, lamandla akhe, lokuthi walwa njani loAmaziya inkosi yakoJuda, kakubhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoIsrayeli?
16 Ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Samariya tare da sarakunan Isra’ila. Yerobowam ɗansa, ya kuma gāje shi.
UJehowashi waselala laboyise, wangcwatshelwa eSamariya emakhosini akoIsrayeli. UJerobhowamu indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.
17 Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya yi shekaru goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
UAmaziya indodana kaJowashi, inkosi yakoJuda, wasephila iminyaka elitshumi lanhlanu emva kokufa kukaJehowashi indodana kaJehowahazi inkosi yakoIsrayeli.
18 Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Ezinye-ke zezindaba zikaAmaziya, kazibhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoJuda?
19 Suka ƙulla masa maƙarƙashiya a Urushalima, ya gudu zuwa Lakish, amma suka aika har Lakish aka kashe shi a can.
Basebemenzela ugobe eJerusalema, wabalekela eLakishi; kodwa bathuma bamlandela eLakishi, bambulalela khona.
20 Aka ɗauko shi a kan doki aka kawo shi Urushalima, aka kuwa binne shi tare da kakanninsa, a Birnin Dawuda.
Basebemthwala ngamabhiza, wangcwatshelwa eJerusalema kuboyise emzini kaDavida.
21 Sa’an nan dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda yake ɗan shekaru goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
Bonke abantu bakoJuda basebethatha uAzariya, owayeleminyaka elitshumi lesithupha, bambeka waba yinkosi esikhundleni sikayise uAmaziya.
22 Shi ne ya sāke gina Elat, ya kuma maido da ita a hannun Yahuda bayan Amaziya ya huta da kakanninsa.
Yena wakha iElathi, wayibuyisela koJuda emva kokulala kwenkosi laboyise.
23 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehowash sarkin Isra’ila ya zama sarki a Samariya, ya kuma yi mulki na shekaru arba’in da ɗaya.
Ngomnyaka wetshumi lanhlanu kaAmaziya indodana kaJowashi inkosi yakoJuda uJerobhowamu indodana kaJowashi inkosi yakoIsrayeli waba yinkosi eSamariya; wabusa iminyaka engamatshumi amane lanye.
24 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji bai kuwa kauce wa duk zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
Wasesenza okubi emehlweni eNkosi; kasukanga ezonweni zonke zikaJerobhowamu indodana kaNebati owenza uIsrayeli one.
25 Shi ne ya maido da iyakokin Isra’ila daga Lebo Hamat zuwa Tekun Araba, bisa ga maganar Ubangiji, Allah na Isra’ila, da ya yi ta bakin bawansa Yunana ɗan Amittai, annabi daga Gat-Hefer.
Yena wabuyisela umngcele wakoIsrayeli kusukela ekungeneni kweHamathi kuze kufike elwandle lwamagceke, njengokwelizwi leNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli, eyalikhuluma ngesandla senceku yayo uJona indodana kaAmithayi umprofethi, owayevela eGathi-Heferi.
26 Ubangiji ya ga irin muguwar wahalar da ta shafi kowa a Isra’ila, ko bawa ko’yantacce, babu mai taimakonsu.
Ngoba iNkosi yabona ukuhlupheka kukaIsrayeli, kwakubaba kakhulu, ngoba kwakungekho ovalelweyo, njalo engekho okhululekileyo, njalo kungelamsizi kaIsrayeli.
27 Da yake kuma Ubangiji bai ce zai shafe sunan Isra’ila daga fuskar duniya ba, sai ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yowash.
INkosi yayingatshongo-ke ukuthi izalesula ibizo likaIsrayeli ngaphansi kwamazulu; kodwa yabasindisa ngesandla sikaJerobhowamu indodana kaJowashi.
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yerobowam, da dukan abin da ya yi, da yaƙe-yaƙen da ya yi, haɗe da sāke ƙwato wa Isra’ila Damaskus da Hamat waɗanda suke a hannun Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Ezinye-ke zezindaba zikaJerobhowamu, lakho konke akwenzayo, lamandla akhe, ukuthi walwa njani, lokuthi wayibuyisela njani koIsrayeli iDamaseko leHamathi, engeyeJuda, kakubhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoIsrayeli?
29 Yerobowam ya huta da kakanninsa, sarakunan Isra’ila. Zakariya ɗansa kuwa ya gāje shi.
UJerobhowamu waselala laboyise, emakhosini akoIsrayeli. UZekhariya indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.

< 2 Sarakuna 14 >