< 2 Sarakuna 14 >
1 A shekara ta biyu ta mulkin Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila, Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya fara mulki.
Druge godine kraljevanja Joaša, sina Joahazova, nad Izraelom, postade judejskim kraljem Amasja, sin Joašev.
2 Ya zama sarki yana da shekaru ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin, mutuniyar Urushalima.
Bilo mu je dvadeset i pet godina kad se zakraljio, a kraljevao je dvadeset i devet godina u Jeruzalemu. Mati mu se zvala Joadana i bila je iz Jeruzalema.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, sai dai ba kamar kakansa Dawuda ba. A kome dai ya bi gurbin mahaifinsa Yowash.
Činio je što je pravo u Jahvinim očima, ali ne sasvim kao praotac njegov David. U svemu je slijedio Joaša, svoga oca.
4 Ba a dai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙone turare a can.
Ali uzvišica nije razrušio i narod je svejednako prinosio žrtve i kad na uzvišicama.
5 Bayan masarauta ta kahu a hannunsa, sai ya kashe fadawan da suka kashe mahaifinsa sarki.
Kad je učvrstio kraljevstvo, smakao je one časnike koji su mu ubili oca.
6 Duk da haka bai kashe’ya’yan masu kisan ba, bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda laifin’ya’ya ba, ko kuma’ya’ya saboda laifin iyayensu ba, kowa zai mutu don zunubansa.”
Ali nije pogubio sinova onih ubojica, prema onome što je napisano u knjizi Zakona Mojsijeva, gdje Jahve zapovijeda: “Neka se očevi ne pogubljuju za sinove ni sinovi za očeve, nego svatko neka gine za svoj grijeh.”
7 Shi ne kuma wanda ya ci mutanen Edom dubu goma a yaƙi, a Kwarin Gishiri, ya kuma ci Sela da yaƙi, ya ba ta suna Yokteyel, sunan da ake kiranta har wa yau.
On je potukao Edomce u Slanoj dolini, deset tisuća njih, i u bitki je zauzeo Selu; dao joj je ime Jokteel, koje nosi do današnjega dana.
8 Sai Amaziya ya aika’yan aika wurin Yehowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, yana tsokanarsa cewa, “Zo, mu sadu fuska da fuska.”
Tada Amasja posla glasnike izraelskom kralju Joašu, sinu Jehuova sina Joahaza, i poruči mu: “Dođi da se ogledamo!”
9 Amma Yehowash sarkin Isra’ila ya mai da martani wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata’yar ƙaya a kurmin Lebanon ta aika da saƙo wurin itacen al’ul a Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Amma wani naman jeji ya zo ya tattake ƙayar.
A izraelski kralj Joaš odvrati judejskom kralju Amasji: “Libanonski je trn jedanput poslao glasnike k libanonskom cedru: 'Daj kćer mome sinu za ženu', ali su divlje zvijeri libanonske prošle i trn izgazile.
10 Tabbatacce ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana ɗaga kai. To, ka gode da darajar da ka samu, amma ka zauna a gida! Don me kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da kuma ta Yahuda?”
Potukao si Edomce, pa ti se srce uzobijestilo i tražiš slavu! Radije ostani kod kuće. Zašto izazivaš zlo i hoćeš da propadneš ti i svi Judejci s tobom?”
11 Amma Amaziya bai saurara ba, saboda haka Yehowash sarkin Isra’ila ya kai masa hari. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh.
Ali Amasja ne posluša. Izađe izraelski kralj Joaš te se ogledaše u boju on i judejski kralj Amasja u Bet Šemešu u Judeji.
12 Isra’ila suka fatattaki Yahuda, kowa kuwa ya tsere zuwa gidansa.
Izraelci poraziše Judejce i oni pobjegoše svaki pod svoj šator.
13 Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya, a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya tafi Urushalima ya rushe katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, ratarta ta kai wajen ƙafa ɗari shida.
Izraelski kralj Joaš uhvati u Bet Šemešu judejskoga kralja Amasju, sina Joaševa, sina Ahazjina, i odvede ga u Jeruzalem. Tada sruši jeruzalemski zid od Efrajimovih vrata do Ugaonih vrata, u dužini od četiri stotine lakata.
14 Ya kwashi ɗaukan zinariya da azurfa da duk kayan da aka samu a haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan. Ya kuma kwashi bayi sa’an nan ya koma Samariya.
Uzevši sve zlato, srebro i posuđe što se nalazilo u Domu Jahvinu i u riznici kraljevskog dvora, povrh toga i taoce, vrati se u Samariju.
15 Game da sauran ayyukan mulkin Yehowash, abin da ya yi da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙinsa da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Ostala povijest Joaševa, sve što je činio i poduzimao i kako je ratovao s Amasjom, judejskim kraljem, zar sve to nije zapisano u knjizi Ljetopisa izraelskih kraljeva?
16 Ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Samariya tare da sarakunan Isra’ila. Yerobowam ɗansa, ya kuma gāje shi.
Joaš je počinuo sa svojim ocima i pokopan je u Samariji uz kraljeve izraelske. Sin njegov Jeroboam zakralji se mjesto njega.
17 Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya yi shekaru goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
Amasja, sin Joašev, judejski kralj, živio je još petnaest godina poslije smrti izraelskog kralja Joaša, sina Joahazova.
18 Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
A ostala povijest Amasjina zar nije zapisana u knjizi Ljetopisa kraljeva judejskih?
19 Suka ƙulla masa maƙarƙashiya a Urushalima, ya gudu zuwa Lakish, amma suka aika har Lakish aka kashe shi a can.
Protiv njega je skovana urota u Jeruzalemu. Iako je on pobjegao u Lakiš, poslaše za njim u Lakiš ljude koji ga ondje ubiše.
20 Aka ɗauko shi a kan doki aka kawo shi Urushalima, aka kuwa binne shi tare da kakanninsa, a Birnin Dawuda.
Odande su ga prenijeli na konjima i sahranili u Jeruzalemu kraj njegovih otaca, u Davidovu gradu.
21 Sa’an nan dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda yake ɗan shekaru goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
Tada sav judejski narod uze Azahju, komu bijaše šesnaest godina, i zakralji ga namjesto njegova oca Amasje.
22 Shi ne ya sāke gina Elat, ya kuma maido da ita a hannun Yahuda bayan Amaziya ya huta da kakanninsa.
On opet sagradi Elat povrativši ga Judeji, pošto je kralj počinuo kod svojih otaca.
23 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehowash sarkin Isra’ila ya zama sarki a Samariya, ya kuma yi mulki na shekaru arba’in da ɗaya.
Petnaeste godine kraljevanja judejskog kralja Amasje, sina Joaševa, postade izraelskim kraljem u Samariji Jeroboam, sin Joašev. On je kraljevao četrdeset i jednu godinu.
24 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji bai kuwa kauce wa duk zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
Činio je što je zlo u očima Jahvinim, nije se ostavio nijednoga grijeha Jeroboama, sina Nebatova, koji je zaveo Izraela.
25 Shi ne ya maido da iyakokin Isra’ila daga Lebo Hamat zuwa Tekun Araba, bisa ga maganar Ubangiji, Allah na Isra’ila, da ya yi ta bakin bawansa Yunana ɗan Amittai, annabi daga Gat-Hefer.
On je dobio natrag izraelsko područje od Ulaza u Hamat do Mrtvoga mora, prema riječi koju je Jahve, Bog Izraelov, rekao preko sluge svoga Jone, sina Amitajeva, proroka iz Gat Hahefera.
26 Ubangiji ya ga irin muguwar wahalar da ta shafi kowa a Isra’ila, ko bawa ko’yantacce, babu mai taimakonsu.
Jer je Jahve vidio ljutu nevolju Izraelovu da više nema ni slobodnih ni robova i nikoga da pomogne Izraelu.
27 Da yake kuma Ubangiji bai ce zai shafe sunan Isra’ila daga fuskar duniya ba, sai ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yowash.
Ali Jahve nije odlučio izbrisati ispod neba ime Izraelovo: spasio ga je rukom Jeroboama, sina Joaševa.
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yerobowam, da dukan abin da ya yi, da yaƙe-yaƙen da ya yi, haɗe da sāke ƙwato wa Isra’ila Damaskus da Hamat waɗanda suke a hannun Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Ostala povijest Jeroboama, sve što je učinio i sve što je poduzimao, kako je ratovao i kako je vratio Damask Judi i Izraelu, zar sve to nije zapisano u knjizi Ljetopisa kraljeva izraelskih?
29 Yerobowam ya huta da kakanninsa, sarakunan Isra’ila. Zakariya ɗansa kuwa ya gāje shi.
Jeroboam je počinuo sa svojim ocima. Pokopali su ga u Samariji uz kraljeve izraelske, a njegov sin Zaharija zakralji se mjesto njega.