< 2 Sarakuna 13 >
1 A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
В лето двадесять третие Иоаса сына Охозиина царя Иудина царствова Иоахаз сын Ииуев над Израилем в Самарии седмьнадесять лет,
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
и сотвори лукавое пред очима Господнима, и иде вслед грехов Иеровоама сына Наватова, иже в грех введе Израиля и не остася злобы тоя.
3 Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
И разгневася Господь гневом на Израиля, и вдаде их в руце Азаилу царю Сирску и в руце сына Адера, сына Азаилева, во вся дни.
4 Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
И помолися Иоахаз лицу Господню, и услыша его Господь, яко виде скорбь Израилеву, понеже оскорби их царь Сирский.
5 Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
И даде Господь спасение Израилю, и избыша от руку Сирску: и вселишася и сынове Израилевы в селения своя якоже и вчера и третияго дне:
6 Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
обаче не отступиша от грехов дому Иеровоама сына Наватова, иже и в грех введе Израиля, в нем ходяху: и дубрава стояше в Самарии.
7 Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
Яко не осташася Иоахазу людие, но токмо пятьдесят конник, и десять колесниц, и десять тысящ пешцев, яко изгубил их царь Сирский, и положи я яко прах на попрание.
8 Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
И прочая словес Иоахазовых, и вся елика сотвори, и силы его, не сия ли писана в книзе словес дний царей Израилевых?
9 Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
И успе Иоахаз со отцы своими, и погребоша его в Самарии: и воцарися Иоас сын его вместо его.
10 A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
В лето тридесять седмое Иоаса царя Иудина царствова Иоас сын Иоахазов над Израилем в Самарии шестьнадесять лет,
11 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
и сотвори лукавое пред очима Господнима: и отступи от всех грехов Иеровоама сына Наватова, иже в грех введе Израиля, в том хождаше.
12 Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
И прочая словес Иоасовых и вся елика сотвори, и силы его, яже сотвори со Амессием царем Иудиным, не сия ли писана в книзе словес дний царей Израилевых?
13 Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
И успе Иоас со отцы своими, Иеровоам же седе на престоле его: и погребен бысть Иоас в Самарии с царми Израилевыми.
14 To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
И Елиссей разболеся болезнию своею, от неяже умре. И прииде к нему Иоас царь Израилев, и плакася над лицем его, и рече: отче, отче, колесница Израилева и кони его.
15 Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
И рече ему Елиссей возми лук и стрелы. И взя к себе лук и стрелы.
16 Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
И рече царю: возложи руку свою на лук. И возложи Иоас руку свою на лук, и Елиссей возложи руки своя на руки царевы,
17 Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
и рече: отверзи окно еже на восток. И отверзе. И рече Елиссей: стрели. И стрели (царь). И рече Елиссей: стрела спасения Господня и стрела спасения на Сирию, и победиши Сирию во Афеке даже до скончания.
18 Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
И рече ему Елиссей: возми лук. И взя. И рече царю Израилеву: удари на землю. И удари царь трижды, и ста.
19 Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
И оскорбе человек Божий о нем и рече: аще бы ударил еси пятищи или шестищи, тогда бы еси поразил Сирию до скончания, ныне же победиши Сирию трижды.
20 Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
И умре Елиссей, и погребоша его. Воини же Моавли приидоша в землю наставающу лету тому.
21 Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
И бысть им погребающим мужа, и се, видеша воинов, и повергоша мужа во гробе Елиссеове: (и впаде тело человека мертва, ) и прикоснуся костем Елиссеовым, и оживе и воста на ноги своя.
22 Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
Азаил же оскорбляше Израиля во вся дни Иоахазовы.
23 Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
И помилова и Господь, и ущедри я, и призре на ня завета ради Своего, иже со Авраамом и Исааком и Иаковом, и не восхоте Господь потребити их, ниже отверже их от лица Своего.
24 Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
И умре Азаил царь Сирский, и воцарися Адер сын его вместо его.
25 Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.
И возвратися Иоас сын Иоахазов, и взя грады от руки Адера сына Азаилева, ихже взя от руку Иоахаза отца его в брани: трижды победи его Иоас, и возврати грады Израилевы.