< 2 Sarakuna 13 >
1 A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
Idet tre og tyvende Joas's, Ahasias Søns, Judas Konges, Aar blev Joahas, Jehus Søn, Konge over Israel i Samaria i sytten Aar.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
Og han gjorde det onde for Herrens Øjne og vandrede efter Jeroboams, Nebats Søns, Synder, med hvilke han kom Israel til at synde, han veg ikke derfra.
3 Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
Derfor optændtes Herrens Vrede over Israel, og han gav dem i Hasaels, Syriens Konges, Haand og i Benhadads, Hasaels Søns, Haand alle Dage.
4 Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
Men Joahas bad ydmygeligt til Herren, og Herren hørte ham; thi han saa til Israels Trængsel, thi Kongen af Syrien trængte dem.
5 Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
Og Herren gav Israel en Frelser, og de slap fri for at være under Syrernes Magt; og Israels Børn boede i deres Telte som tilforn.
6 Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
Dog vege de ikke fra Jeroboams Hus's Synder, som han kom Israel til at synde med, men man vandrede derudi, og Astartebilledet blev ogsaa staaende i Samaria.
7 Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
Men Joahas beholdt ikke flere Folk tilovers end halvtredsindstyve Ryttere og ti Vogne og ti Tusinde Fodfolk; thi Kongen af Syrien havde ødelagt dem og gjort dem til Støv at træde paa.
8 Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Men det øvrige af Joahas's Handeler og alt, hvad han gjorde, og hans Vælde, ere de Ting ikke skrevne i Israels Kongers Krønikers Bog?
9 Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
Og Joahas laa med sine Fædre, og de begravede ham i Samaria, og hans Søn, Joas blev Konge i hans Sted.
10 A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
I det syv og tredivte Joas's, Judas Konges, Aar blev Joas, Joahas's Søn, Konge over Israel i Samaria i seksten Aar.
11 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
Og han gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne; han veg ikke fra nogen af Jeroboams, Nebats Søns, Synder, som han kom Israel til at synde med, men han vandrede deri.
12 Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Men det øvrige af Joas's Handeler og alt, hvad han gjorde og hans Vælde, hvorledes han stred med Amazia, Judas Konge, ere de Ting ikke skrevne i Israels Kongers Krønikers Bog?
13 Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
Og Joas laa med sine Fædre, og Jeroboam sad paa hans Trone; og Joas blev begraven i Samaria hos Israels Konger.
14 To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
Og Elisa blev syg af sin Sygdom, af hvilken han døde; og Joas, Israels Konge, kom ned til ham og græd for hans Ansigt og sagde: Min Fader, min Fader! Israels Vogne og hans Ryttere!
15 Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
Da sagde Elisa til ham: Tag Bue og Pile; og han tog Bue og Pile til ham.
16 Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
Da sagde han til Israels Konge: Læg din Haand paa Buen; og han lagde sin Haand paa den, og Elisa lagde sine Hænder paa Kongens Hænder.
17 Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
Og han sagde: Luk det Vindue op imod Østen! og han lukkede det op; og Elisa sagde: Skyd! og han skød. Og han sagde: En Frelses Pil fra Herren og en Frelses Pil imod Syrerne, og du skal slaa Syrerne i Afek, indtil du gør Ende paa dem.
18 Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
Og han sagde: Tag Pilene; og han tog dem; og han sagde til Kongen af Israel: Slaa imod Jorden; og han slog tre Gange, og saa holdt han op.
19 Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
Da blev den Guds Mand vred paa ham og sagde: Havde du slaget fem eller seks Gange, da skulde du have slaget Syrerne, indtil du havde gjort Ende paa dem; men nu skal du slaa Syrerne tre Gange.
20 Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
Og Elisa døde, og de begravede ham; og Moabs Tropper kom i Landet først paa Aaret.
21 Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
Og det skete, at de begravede en Mand, og se, da de saa Troppen, da kastede de Manden i Elisas Grav; og der Manden kom ned og rørte ved Elisas Ben, da blev han levende og stod op paa sine Fødder.
22 Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
Og Hasael, Kongen af Syrien, havde trængt Israel alle Joahas's Dage.
23 Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
Men Herren var dem naadig og forbarmede sig over dem og vendte sig til dem for sin Pagts Skyld med Abraham, Isak og Jakob og vilde ikke ødelægge dem og bortkastede dem endnu ikke fra sit Ansigt.
24 Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
Og Hasael, Kongen af Syrien, døde, og hans Søn Benhadad blev Konge i hans Sted.
25 Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.
Og Joas, Joahas's Søn, tog de Stæder igen fra Benhadads, Hasaels Søns, Haand, som han havde taget fra Joahas's, hans Faders, Haand i Krigen; tre Gange slog Joas ham og fik Israels Stæder igen.