< 2 Sarakuna 12 >

1 A shekara ta bakwai ta Yehu, Yowash ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima na tsawon shekaru arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; daga Beyersheba.
Jehoash começou a reinar no sétimo ano de Jehu, e ele reinou quarenta anos em Jerusalém. O nome de sua mãe era Zíbia de Berseba.
2 Yowash ya aikata abin da yake daidai a idon Ubangiji domin Yehohiyada firist ya koya masa.
Jehoash fez o que estava certo aos olhos de Iavé todos os seus dias em que Jehoiada, o sacerdote, o instruiu.
3 Amma fa ba a kawar da masujadan kan tuddai ba; mutane suka ci gaba da miƙa hadayu da kuma ƙona turare a kan tuddai.
However, os lugares altos não lhe foram tirados. O povo ainda sacrificava e queimava incenso nos lugares altos.
4 Yowash ya ce wa firistoci, “Ku tattara dukan kuɗin da ake kawo a matsayin hadayu masu tsarki na haikalin Ubangiji, kuɗin da aka tattara a ƙidaya, kuɗin da aka tattara daga wa’adin da mutum ya yi, da kuma kuɗin da aka kawo na yardan rai a haikali.
Jehoash disse aos sacerdotes: “Todo o dinheiro das coisas sagradas que é trazido à casa de Iavé, em dinheiro corrente, o dinheiro do povo para quem cada homem é avaliado, e todo o dinheiro que entra no coração de qualquer homem para trazer à casa de Iavé,
5 Bari kowane firist yă karɓi kuɗi daga masu ajiya, sa’an nan a yi amfani da su a gyara duk wani abin da ya lalace a haikali.”
deixe os sacerdotes levá-lo a eles, cada homem de seu doador; e eles repararão os danos à casa, onde quer que se encontre algum dano”.
6 Amma har zuwa shekara ta ashirin da uku ta mulkin Yowash, firistocin ba su yi gyara haikalin ba.
Mas foi assim, que no vigésimo terceiro ano do rei Jehoash os padres não haviam reparado os danos da casa.
7 Saboda haka Sarki Yowash ya kira Yehohiyada firist da sauran firistoci ya tambaye su ya ce, “Me ya sa ba kwa gyaran abubuwan da suka lalace a haikali? Kada ku sāke karɓan kuɗi daga masu ajiya, amma a miƙa su domin gyaran haikali.”
Então o rei Jehoash chamou o sacerdote Jehoiada e os outros sacerdotes, e disse-lhes: “Por que vocês não estão reparando os danos da casa? Agora, portanto, não aceitem mais dinheiro de seus tesoureiros, mas entreguem-no para reparar os danos à casa”.
8 Firistoci suka yarda cewa ba za su sāke karɓan kuɗi daga mutane ba, kuma ba za su yi gyaran haikalin da kansu ba.
Os padres consentiram que não aceitassem mais dinheiro do povo, e que não reparassem os danos à casa.
9 Yehohiyada firist ya ɗauki akwatin ya huda rami a murfinsa. Ya ajiye shi kusa da bagade a hannun dama na haikalin Ubangiji. Firistocin da suke tsaron ƙofar suka zuba dukan kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji a cikin akwatin.
Mas Jehoiada o padre pegou uma arca e fez um buraco em sua tampa, e a colocou ao lado do altar, do lado direito, ao entrar na casa de Yahweh; e os padres que mantiveram o limiar colocaram todo o dinheiro que foi trazido para a casa de Yahweh dentro dela.
10 Duk sa’ad da suka ga kuɗin sun ƙaru a akwatin, sai marubucin fada da babban firist, su ƙirga kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji su sa a jakankuna.
Quando viram que havia muito dinheiro na arca, o escriba do rei e o sumo sacerdote subiram, colocaram-no em sacos e contaram o dinheiro que foi encontrado na casa de Yahweh.
11 Sa’ad da suka ga kuɗin ya yi yawa, sai su ba wa waɗanda aka zaɓa su lura da aikin haikalin. Da shi suka biya waɗanda suka yi aiki a haikalin Ubangiji, su kafintoci, da magina,
Eles deram o dinheiro que foi pesado nas mãos daqueles que fizeram o trabalho, que tinham a supervisão da casa de Iavé; e o pagaram aos carpinteiros e construtores que trabalharam na casa de Iavé,
12 masu gini, da masu fasa duwatsu. Suka sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu domin gyaran haikalin Ubangiji, suka kuma biya duk waɗansu kuɗin gyaran haikalin.
e aos pedreiros e cortadores de pedra, e para comprar madeira e pedra cortada para reparar os danos à casa de Iavé, e por tudo o que foi disposto para que a casa a reparasse.
13 Ba a yi amfani da kuɗin da aka kawo a haikali don yin manyan kwanonin azurfa, lagwani, abin yayyafa ruwa, kakaki ko wani abu na zinariya, ko na azurfa domin haikalin Ubangiji ba;
Mas não foram feitos para a casa de Iavé copos de prata, rapé, bacias, trombetas, quaisquer vasos de ouro ou vasos de prata, do dinheiro que foi trazido para a casa de Iavé;
14 an ba ma’aikatan da suka gyara haikalin ne.
pois eles deram isso para aqueles que fizeram o trabalho, e repararam a casa de Iavé com ele.
15 Ba su bukaci wani bayani daga waɗanda aka ba wa kuɗin don su biya ma’aikatan ba, domin sun yi aikinsu da aminci.
Moreover eles não exigiram uma contabilidade dos homens em cujas mãos entregaram o dinheiro para dar àqueles que fizeram o trabalho; pois eles lidaram fielmente.
16 Ba a kawo kuɗi daga hadayun laifi da na hadayun zunubi a haikalin Ubangiji ba, waɗannan na firistoci ne.
O dinheiro para as ofertas de transgressão e o dinheiro para as ofertas pelo pecado não foi trazido para a casa de Yahweh. Era dos sacerdotes.
17 A wannan lokaci, Hazayel sarkin Aram ya haura, ya kai wa Gat hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Sa’an nan ya juya don yă yaƙi Urushalima.
Então Hazael, rei da Síria, subiu e lutou contra Gate, e tomou-a; e Hazael preparou seu rosto para subir a Jerusalém.
18 Amma Yowash sarkin Yahuda ya kwashe tsarkakan kayan da kakanninsa, Yehoshafat, Yehoram da Ahaziya, sarakunan Yahuda suka keɓe, da kyautai da shi kansa ya keɓe, da kuma dukan azurfan da aka samu a ɗakunan ajiya haikalin Ubangiji da na fada, ya aika da su wa Hazayel sarkin Aram, shi kuma ya janye daga Urushalima.
Jehoash rei de Judá tomou todas as coisas sagradas que Jeosafá e Jeorão e Acazias, seus pais, reis de Judá, tinham dedicado, e suas próprias coisas sagradas, e todo o ouro que foi encontrado nos tesouros da casa de Javé, e da casa do rei, e o enviou a Hazael, rei da Síria; e ele foi embora de Jerusalém.
19 Game da sauran ayyukan mulkin Yowash da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Now o resto dos atos de Joás, e tudo o que ele fez, não estão escritos no livro das crônicas dos reis de Judá?
20 Hafsoshinsa suka yi masa maƙarƙashiya suka kashe shi a Bet Millo, a kan hanyar da ta gangara zuwa Silla.
seus servos se levantaram e fizeram uma conspiração, e atingiram Joás na casa de Millo, no caminho que desce até Silla.
21 Hafsoshin da suka kashe shi kuwa su ne Yozabad ɗan Shimeyat da Yehozabad ɗan Shomer. Ya mutu, aka kuma binne shi tare da kakanninsa a Birnin Dawuda. Sai Amaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Pois Jozacar, filho de Shimeath, e Jehozabad, filho de Shomer, seus servos, o atingiram e ele morreu; e o enterraram com seus pais na cidade de David; e Amaziah, seu filho, reinou em seu lugar.

< 2 Sarakuna 12 >