< 2 Sarakuna 12 >

1 A shekara ta bakwai ta Yehu, Yowash ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima na tsawon shekaru arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; daga Beyersheba.
Jeūs septītā gadā Joas palika par ķēniņu un valdīja četrdesmit gadus Jeruzālemē. Un viņa mātei bija vārds Cibea no Bēršebas.
2 Yowash ya aikata abin da yake daidai a idon Ubangiji domin Yehohiyada firist ya koya masa.
Un Joas darīja, kas Tam Kungam labi patika, visu savu mūžu, kamēr priesteris Jojada viņu mācīja.
3 Amma fa ba a kawar da masujadan kan tuddai ba; mutane suka ci gaba da miƙa hadayu da kuma ƙona turare a kan tuddai.
Tikai kalnu altāri netapa nopostīti; jo tie ļaudis upurēja un kvēpināja vēl uz tiem kalnu altāriem.
4 Yowash ya ce wa firistoci, “Ku tattara dukan kuɗin da ake kawo a matsayin hadayu masu tsarki na haikalin Ubangiji, kuɗin da aka tattara a ƙidaya, kuɗin da aka tattara daga wa’adin da mutum ya yi, da kuma kuɗin da aka kawo na yardan rai a haikali.
Un Joas sacīja uz tiem priesteriem: visu naudu, kas top dota Dievam par godu un nāk Tā Kunga namā, naudu, kas iet uz galvām, visu naudu, ko spriež par dvēseli, un visu naudu, ko dod no labprātības Tā Kunga namā,
5 Bari kowane firist yă karɓi kuɗi daga masu ajiya, sa’an nan a yi amfani da su a gyara duk wani abin da ya lalace a haikali.”
To priesteriem būs ņemt, ikkatram no sava pazīstama, un tiem būs izlabot tā nama plīsumus visur, kur tie plīsumus atrod.
6 Amma har zuwa shekara ta ashirin da uku ta mulkin Yowash, firistocin ba su yi gyara haikalin ba.
Un notikās ķēniņa Joasa divdesmit un trešā gadā, ka tie priesteri nebija labojuši tā nama plīsumus,
7 Saboda haka Sarki Yowash ya kira Yehohiyada firist da sauran firistoci ya tambaye su ya ce, “Me ya sa ba kwa gyaran abubuwan da suka lalace a haikali? Kada ku sāke karɓan kuɗi daga masu ajiya, amma a miƙa su domin gyaran haikali.”
Tad ķēniņš Joas aicināja priesteri Jojadu un tos citus priesterus un uz tiem sacīja: kāpēc jūs nelabojiet tā nama plīsumus. Un nu jums vairs nebūs ņemt naudu no saviem pazīstamiem, bet to dot priekš tā nama plīsumiem.
8 Firistoci suka yarda cewa ba za su sāke karɓan kuɗi daga mutane ba, kuma ba za su yi gyaran haikalin da kansu ba.
Tad tie priesteri bija mierā, naudas no ļaudīm vairs neņemt, nedz nama plīsumus izlabot.
9 Yehohiyada firist ya ɗauki akwatin ya huda rami a murfinsa. Ya ajiye shi kusa da bagade a hannun dama na haikalin Ubangiji. Firistocin da suke tsaron ƙofar suka zuba dukan kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji a cikin akwatin.
Un priesteris Jojada ņēma šķirstu un ieurba tā vākā caurumu, un to lika sānis altārim pa labo roku; kad kāds nāca Tā Kunga namā, tad tie priesteri, kas slieksni sargāja, tur ielika to naudu, ko ienesa Tā Kunga namā.
10 Duk sa’ad da suka ga kuɗin sun ƙaru a akwatin, sai marubucin fada da babban firist, su ƙirga kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji su sa a jakankuna.
Kad nu redzēja daudz naudas šķirstā esam, tad ķēniņa skrīveris un augstais priesteris nāca un sasēja un skaitīja to naudu, ko atrada Tā Kunga namā.
11 Sa’ad da suka ga kuɗin ya yi yawa, sai su ba wa waɗanda aka zaɓa su lura da aikin haikalin. Da shi suka biya waɗanda suka yi aiki a haikalin Ubangiji, su kafintoci, da magina,
Un tie to naudu ieskaitīja rokā darba uzraugiem, kas bija iecelti pār Tā Kunga namu. Un tie to izdeva amatniekiem un nama būvētājiem, kas pie Tā Kunga nama strādāja,
12 masu gini, da masu fasa duwatsu. Suka sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu domin gyaran haikalin Ubangiji, suka kuma biya duk waɗansu kuɗin gyaran haikalin.
Un mūrniekiem un akmeņu cirtējiem, pirkt kokus un cirstus akmeņus, izlabot Tā Kunga nama plīsumus un izdot par visu, kas bija vajadzīgs, izlabot Tā Kunga namu.
13 Ba a yi amfani da kuɗin da aka kawo a haikali don yin manyan kwanonin azurfa, lagwani, abin yayyafa ruwa, kakaki ko wani abu na zinariya, ko na azurfa domin haikalin Ubangiji ba;
Bet sudraba kausus, nažus, bļodas, trumetes un visādas zelta un sudraba lietas priekš Tā Kunga nama netaisīja no tās naudas, ko sanesa Tā Kunga namā,
14 an ba ma’aikatan da suka gyara haikalin ne.
Bet tie to deva strādniekiem, izlabot ar to Tā Kunga namu.
15 Ba su bukaci wani bayani daga waɗanda aka ba wa kuɗin don su biya ma’aikatan ba, domin sun yi aikinsu da aminci.
Un atbildēšanu neprasīja no tiem vīriem, kam tā nauda bija dota, to dot strādniekiem, bet tie to darīja uz ticību.
16 Ba a kawo kuɗi daga hadayun laifi da na hadayun zunubi a haikalin Ubangiji ba, waɗannan na firistoci ne.
Nauda no noziegumu upuriem un nauda no grēku upuriem netapa nesta Tā Kunga namā, tā nācās priesteriem.
17 A wannan lokaci, Hazayel sarkin Aram ya haura, ya kai wa Gat hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Sa’an nan ya juya don yă yaƙi Urushalima.
To brīdi Azaēls, Sīriešu ķēniņš, cēlās un karoja pret Gatu un to uzņēma. Un Azaēls griezās iet pret Jeruzālemi.
18 Amma Yowash sarkin Yahuda ya kwashe tsarkakan kayan da kakanninsa, Yehoshafat, Yehoram da Ahaziya, sarakunan Yahuda suka keɓe, da kyautai da shi kansa ya keɓe, da kuma dukan azurfan da aka samu a ɗakunan ajiya haikalin Ubangiji da na fada, ya aika da su wa Hazayel sarkin Aram, shi kuma ya janye daga Urushalima.
Tad Joas, Jūda ķēniņš, ņēma visas svētās dāvanas, ko viņa tēvi Jehošafats un Jehorams un Ahazija, Jūda ķēniņi, Dievam bija dāvinājuši, ir tās dāvanas, ko viņš pats bija devis, un visu zeltu, kas atradās Tā Kunga namā un pie ķēniņa nama mantām, un to sūtīja Azaēlim, Sīriešu ķēniņam. Tad šis aizgāja no Jeruzālemes.
19 Game da sauran ayyukan mulkin Yowash da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Un kas vēl par Joasu stāstāms, un viss, ko viņš darījis, tas ir rakstīts Jūda ķēniņu laiku grāmatā.
20 Hafsoshinsa suka yi masa maƙarƙashiya suka kashe shi a Bet Millo, a kan hanyar da ta gangara zuwa Silla.
Un viņa kalpi cēlās un derēja derību un nokāva Joasu Millus namā, kur iet uz Sillu.
21 Hafsoshin da suka kashe shi kuwa su ne Yozabad ɗan Shimeyat da Yehozabad ɗan Shomer. Ya mutu, aka kuma binne shi tare da kakanninsa a Birnin Dawuda. Sai Amaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Jo Jozakars, Šimeata dēls, un Jozabats, Šomera dēls, viņa kalpi, to nokāva, ka tas nomira; un viņu apraka pie viņa tēviem Dāvida pilī. Un viņa dēls Amacīja palika par ķēniņu viņa vietā.

< 2 Sarakuna 12 >