< 2 Sarakuna 12 >
1 A shekara ta bakwai ta Yehu, Yowash ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima na tsawon shekaru arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; daga Beyersheba.
In the seventh year of Jehu became Jehoash king; and forty years did he reign in Jerusalem; and the name of his mother was Zibyah of Beer-sheba'.
2 Yowash ya aikata abin da yake daidai a idon Ubangiji domin Yehohiyada firist ya koya masa.
And Jehoash did what is right in the eyes of the Lord all his days, that Yehoyada' the priest instructed him.
3 Amma fa ba a kawar da masujadan kan tuddai ba; mutane suka ci gaba da miƙa hadayu da kuma ƙona turare a kan tuddai.
Only the high-places were not removed: the people as yet sacrificed and burnt incense on the high-places.
4 Yowash ya ce wa firistoci, “Ku tattara dukan kuɗin da ake kawo a matsayin hadayu masu tsarki na haikalin Ubangiji, kuɗin da aka tattara a ƙidaya, kuɗin da aka tattara daga wa’adin da mutum ya yi, da kuma kuɗin da aka kawo na yardan rai a haikali.
And Jehoash said to the priests, all the money of the dedicated things that may be brought into the house of the Lord, the money of every one that passeth the numbering, the money any man is valued at, and all the money that cometh into any man's heart to bring into the house of the Lord,
5 Bari kowane firist yă karɓi kuɗi daga masu ajiya, sa’an nan a yi amfani da su a gyara duk wani abin da ya lalace a haikali.”
The priests shall take to themselves, every man from his acquaintance; and they shall repair the breaches of the house, wheresoever any breach may be found.
6 Amma har zuwa shekara ta ashirin da uku ta mulkin Yowash, firistocin ba su yi gyara haikalin ba.
But it happened, that in the three and twentieth year of king Jehoash the priests had not repaired the breaches of the house.
7 Saboda haka Sarki Yowash ya kira Yehohiyada firist da sauran firistoci ya tambaye su ya ce, “Me ya sa ba kwa gyaran abubuwan da suka lalace a haikali? Kada ku sāke karɓan kuɗi daga masu ajiya, amma a miƙa su domin gyaran haikali.”
Then called king Jehoash for Yehoyada' the priest, and the [other] priests, and he said unto them, Wherefore do ye not repair the breaches of the house? and now ye shall take no more money from your acquaintances, but ye shall give it up [at once] for the breaches of the house.
8 Firistoci suka yarda cewa ba za su sāke karɓan kuɗi daga mutane ba, kuma ba za su yi gyaran haikalin da kansu ba.
And the priests consented neither to take any more money from the people, nor to repair the breaches of the house.
9 Yehohiyada firist ya ɗauki akwatin ya huda rami a murfinsa. Ya ajiye shi kusa da bagade a hannun dama na haikalin Ubangiji. Firistocin da suke tsaron ƙofar suka zuba dukan kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji a cikin akwatin.
But Yehoyada' the priest took a chest, and bored a hole in its lid, and he placed it beside the altar, on the right side as one cometh into the house of the Lord: and the priests that kept watch at the threshold put therein all the money, that was brought into the house of the Lord.
10 Duk sa’ad da suka ga kuɗin sun ƙaru a akwatin, sai marubucin fada da babban firist, su ƙirga kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji su sa a jakankuna.
And it happened, when they saw that there was much money in the chest, that the king's scribe and the high-priest came up, and they put up in bags, after having counted, the money that was found in the house of the Lord.
11 Sa’ad da suka ga kuɗin ya yi yawa, sai su ba wa waɗanda aka zaɓa su lura da aikin haikalin. Da shi suka biya waɗanda suka yi aiki a haikalin Ubangiji, su kafintoci, da magina,
And they gave the money, after it was counted, into the hands of those who overlooked the workmen, that had been appointed as overseers of the house of the Lord: and they laid it out to the carpenters and to the builders, that wrought on the house of the Lord,
12 masu gini, da masu fasa duwatsu. Suka sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu domin gyaran haikalin Ubangiji, suka kuma biya duk waɗansu kuɗin gyaran haikalin.
And to the masons, and the hewers of stone, and for the purchase of timber and hewn stones to repair the breaches of the house of the Lord, and for all that was laid out for the house to repair it.
13 Ba a yi amfani da kuɗin da aka kawo a haikali don yin manyan kwanonin azurfa, lagwani, abin yayyafa ruwa, kakaki ko wani abu na zinariya, ko na azurfa domin haikalin Ubangiji ba;
Nevertheless there were not made for the house of the Lord bowls of silver, knives, basins, trumpets, all kinds of vessels of gold, or vessels of silver, from the money that was brought into the house of the Lord;
14 an ba ma’aikatan da suka gyara haikalin ne.
But they gave it to those who overlooked the workmen, and they repaired therewith the house of the Lord.
15 Ba su bukaci wani bayani daga waɗanda aka ba wa kuɗin don su biya ma’aikatan ba, domin sun yi aikinsu da aminci.
And they reckoned not with the men, into whose hand they delivered the money to give it to those who overlooked the workmen; for they acted in good faith.
16 Ba a kawo kuɗi daga hadayun laifi da na hadayun zunubi a haikalin Ubangiji ba, waɗannan na firistoci ne.
The money for trespass-offerings and the money for sin-offerings was not brought into the house of the Lord: it belonged to the priests.
17 A wannan lokaci, Hazayel sarkin Aram ya haura, ya kai wa Gat hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Sa’an nan ya juya don yă yaƙi Urushalima.
At that time Chazael the king of Syria went up, and fought against Gath, and captured it: and Chazael directed his face to go up against Jerusalem.
18 Amma Yowash sarkin Yahuda ya kwashe tsarkakan kayan da kakanninsa, Yehoshafat, Yehoram da Ahaziya, sarakunan Yahuda suka keɓe, da kyautai da shi kansa ya keɓe, da kuma dukan azurfan da aka samu a ɗakunan ajiya haikalin Ubangiji da na fada, ya aika da su wa Hazayel sarkin Aram, shi kuma ya janye daga Urushalima.
Then took Jehoash the king of Judah all the hallowed things that Jehoshaphat, Jehoram, and Achazyahu, his fathers, the kings of Judah, had dedicated, and his own hallowed things, and all the gold that was found in the treasures of the house of the Lord, and in the king's house, and sent it to Chazael the king of Syria: and he withdrew from Jerusalem.
19 Game da sauran ayyukan mulkin Yowash da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
And the rest of the acts of Joash, and all that he did, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Judah.
20 Hafsoshinsa suka yi masa maƙarƙashiya suka kashe shi a Bet Millo, a kan hanyar da ta gangara zuwa Silla.
And his servants arose, and formed a conspiracy, and smote Joash in Beth-millo, which [lieth on the road] that goeth down to Silla.
21 Hafsoshin da suka kashe shi kuwa su ne Yozabad ɗan Shimeyat da Yehozabad ɗan Shomer. Ya mutu, aka kuma binne shi tare da kakanninsa a Birnin Dawuda. Sai Amaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
And Yozachar the son of Shim'ath, and Yehozabad the son of Shomer, his servants, smote him, and he died; and they buried him with his fathers in the city of David: and Amazyah his son became king in his stead.