< 2 Sarakuna 12 >

1 A shekara ta bakwai ta Yehu, Yowash ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima na tsawon shekaru arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; daga Beyersheba.
In the seventh year of Jehu's rule, Jehoash became king; and he was ruling for forty years in Jerusalem; his mother's name was Zibiah of Beer-sheba.
2 Yowash ya aikata abin da yake daidai a idon Ubangiji domin Yehohiyada firist ya koya masa.
Jehoash did what was right in the eyes of the Lord all his days, because he was guided by the teaching of Jehoiada the priest.
3 Amma fa ba a kawar da masujadan kan tuddai ba; mutane suka ci gaba da miƙa hadayu da kuma ƙona turare a kan tuddai.
But the high places were not taken away; the people went on making offerings and burning them in the high places.
4 Yowash ya ce wa firistoci, “Ku tattara dukan kuɗin da ake kawo a matsayin hadayu masu tsarki na haikalin Ubangiji, kuɗin da aka tattara a ƙidaya, kuɗin da aka tattara daga wa’adin da mutum ya yi, da kuma kuɗin da aka kawo na yardan rai a haikali.
And Jehoash said to the priests, All the money of the holy things, which comes into the house of the Lord, (the amount fixed for every man's payment, ) and all the money given by any man freely from the impulse of his heart,
5 Bari kowane firist yă karɓi kuɗi daga masu ajiya, sa’an nan a yi amfani da su a gyara duk wani abin da ya lalace a haikali.”
Let the priests take, every man from his friends and neighbours, to make good what is damaged in the house, wherever it is to be seen.
6 Amma har zuwa shekara ta ashirin da uku ta mulkin Yowash, firistocin ba su yi gyara haikalin ba.
But in the twenty-third year of King Jehoash, the priests had not made good the damaged parts of the house.
7 Saboda haka Sarki Yowash ya kira Yehohiyada firist da sauran firistoci ya tambaye su ya ce, “Me ya sa ba kwa gyaran abubuwan da suka lalace a haikali? Kada ku sāke karɓan kuɗi daga masu ajiya, amma a miƙa su domin gyaran haikali.”
Then King Jehoash sent for Jehoiada the priest, and the other priests, and said to them, Why have you not made good what is damaged in the house? now take no more money from your neighbours, but give it for the building up of the house.
8 Firistoci suka yarda cewa ba za su sāke karɓan kuɗi daga mutane ba, kuma ba za su yi gyaran haikalin da kansu ba.
So the priests made an agreement to take no more money from the people, and not to make good what was damaged in the house.
9 Yehohiyada firist ya ɗauki akwatin ya huda rami a murfinsa. Ya ajiye shi kusa da bagade a hannun dama na haikalin Ubangiji. Firistocin da suke tsaron ƙofar suka zuba dukan kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji a cikin akwatin.
But Jehoiada the priest took a chest, and making a hole in the cover of it, put it by the altar, on the right side when one comes into the house of the Lord; and the priests who kept the door put in it regularly all the money which was taken into the house of the Lord.
10 Duk sa’ad da suka ga kuɗin sun ƙaru a akwatin, sai marubucin fada da babban firist, su ƙirga kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji su sa a jakankuna.
And when they saw that there was much money in the chest, the king's scribe and the high priest came and put it in bags, noting the amount of all the money there was in the house of the Lord.
11 Sa’ad da suka ga kuɗin ya yi yawa, sai su ba wa waɗanda aka zaɓa su lura da aikin haikalin. Da shi suka biya waɗanda suka yi aiki a haikalin Ubangiji, su kafintoci, da magina,
And the money which was measured out they gave regularly to those who were responsible for overseeing the work, and these gave it in payment to the woodworkers and the builders who were working on the house of the Lord,
12 masu gini, da masu fasa duwatsu. Suka sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu domin gyaran haikalin Ubangiji, suka kuma biya duk waɗansu kuɗin gyaran haikalin.
And to the wall-builders and the stone-cutters, and to get wood and cut stone for building up the broken parts of the house of the Lord, and for everything needed to put the house in good order.
13 Ba a yi amfani da kuɗin da aka kawo a haikali don yin manyan kwanonin azurfa, lagwani, abin yayyafa ruwa, kakaki ko wani abu na zinariya, ko na azurfa domin haikalin Ubangiji ba;
But the money was not used for making silver cups or scissors or basins or wind-instruments or any vessels of gold or silver for the house of the Lord;
14 an ba ma’aikatan da suka gyara haikalin ne.
But it was all given to the workmen who were building up the house.
15 Ba su bukaci wani bayani daga waɗanda aka ba wa kuɗin don su biya ma’aikatan ba, domin sun yi aikinsu da aminci.
And they did not get any statement of accounts from the men to whom the money was given for the workmen, for they made use of it with good faith.
16 Ba a kawo kuɗi daga hadayun laifi da na hadayun zunubi a haikalin Ubangiji ba, waɗannan na firistoci ne.
The money of the offerings for error and the sin-offerings was not taken into the house of the Lord; it was the priests'.
17 A wannan lokaci, Hazayel sarkin Aram ya haura, ya kai wa Gat hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Sa’an nan ya juya don yă yaƙi Urushalima.
Then Hazael, king of Aram, went up against Gath and took it; and his purpose was to go up to Jerusalem.
18 Amma Yowash sarkin Yahuda ya kwashe tsarkakan kayan da kakanninsa, Yehoshafat, Yehoram da Ahaziya, sarakunan Yahuda suka keɓe, da kyautai da shi kansa ya keɓe, da kuma dukan azurfan da aka samu a ɗakunan ajiya haikalin Ubangiji da na fada, ya aika da su wa Hazayel sarkin Aram, shi kuma ya janye daga Urushalima.
Then Jehoash, king of Judah, took all the holy things which Jehoshaphat and Jehoram and Ahaziah his fathers, the kings of Judah, had given to the Lord, together with the things he himself had given, and all the gold in the Temple store and in the king's house, and sent it to Hazael, king of Aram; and he went away from Jerusalem.
19 Game da sauran ayyukan mulkin Yowash da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Now the rest of the acts of Joash, and all he did, are they not recorded in the book of the history of the kings of Israel?
20 Hafsoshinsa suka yi masa maƙarƙashiya suka kashe shi a Bet Millo, a kan hanyar da ta gangara zuwa Silla.
And his servants made a secret design and put Joash to death at the house of Millo on the way down to Silla.
21 Hafsoshin da suka kashe shi kuwa su ne Yozabad ɗan Shimeyat da Yehozabad ɗan Shomer. Ya mutu, aka kuma binne shi tare da kakanninsa a Birnin Dawuda. Sai Amaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
And Jozacar, the son of Shimeath, and Jehozabad, the son of Shomer, his servants, came to him and put him to death; and they put him into the earth with his fathers in the town of David; and Amaziah his son became king in his place.

< 2 Sarakuna 12 >