< 2 Sarakuna 11 >
1 Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
Da Akasjas mor Atalja fikk vite at hennes sønn var død, tok hun sig for å utrydde hele den kongelige ætt.
2 Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
Men Akasjas søster Joseba, kong Jorams datter, tok Joas, Akasjas sønn, og førte ham hemmelig bort fra kongesønnene som skulde drepes, og førte ham og hans amme inn i sengekammeret. Således skjulte de ham for Atalja, så han ikke blev drept.
3 Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
Siden var han hos henne i Herrens hus og blev holdt skjult i seks år, mens Atalja regjerte i landet.
4 A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
Men i det syvende år sendte Jojada bud efter livvaktens høvedsmenn og lot dem komme inn til sig i Herrens hus og gjorde en pakt med dem og tok dem i ed der i Herrens hus og viste dem kongens sønn.
5 Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
Og han bød dem og sa: Hør nu hvad I skal gjøre: Den ene tredjedel av eder skal tiltrede vakten på sabbaten og holde vakt ved kongens hus,
6 kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
og den annen tredjedel i Surporten og den tredje tredjedel i porten bak drabantene; således skal I holde vakt ved huset og avstenge det;
7 ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
men de to deler av eder, de som treder av på sabbaten, de skal holde vakt i Herrens hus hos kongen.
8 Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
I skal stille eder rundt omkring kongen, hver mann med våben i hånd, og den som vil trenge inn i rekkene, skal drepes; I skal være om kongen, bade når han går ut, og når han går inn.
9 Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
Høvedsmennene gjorde aldeles som presten Jojada bød dem; de tok hver sine menn, både dem som tiltrådte på sabbaten, og dem som trådte av på sabbaten, og kom til presten Jojada.
10 Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
Og presten gav høvedsmennene de spyd og skjold som hadde tilhørt kong David, og som var i Herrens hus.
11 Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
Og drabantene stod opstilt, hver mann med våben i hånd, fra husets høire side til husets venstre side bortimot alteret og bortimot huset rundt omkring kongen.
12 Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
Så førte han kongesønnen ut og satte kronen på ham og overgav ham vidnesbyrdet, og de gjorde ham til konge og salvet ham; og de klappet i hendene og ropte: Kongen leve!
13 Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
Da Atalja hørte drabantenes og folkets rop, gikk hun inn i Herrens hus til folket.
14 Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
Der fikk hun se at kongen stod på forhøiningen, som skikk var, og høvedsmennene og trompetblåserne stod hos ham, og hele folkemengden gledet sig og støtte i trompetene; da sønderrev Atalja sine klær og ropte: Oprør, oprør!
15 Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
Men presten Jojada bød høvedsmennene, dem som var satt over hæren, og sa til dem: Før henne ut mellem rekkene, og om nogen følger henne, så drep ham med sverd! For presten hadde sagt: Hun må ikke drepes i Herrens hus!
16 Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
Så gjorde de plass for henne til begge sider, og hun gikk den vei som hestene pleier å kjøre inn til kongens hus; og der blev hun drept.
17 Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
Og Jojada gjorde en pakt mellem Herren og kongen og folket at de skulde være Herrens folk, og en pakt mellem kongen og folket.
18 Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
Og hele folkemengden gikk inn i Ba'als hus og rev det ned; hans altere og hans billeder knuste de aldeles, og Ba'als prest Mattan drepte de foran alterne. Og presten satte folk til å ha tilsyn med Herrens hus.
19 Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
Så tok han med sig høvedsmennene og livvakten og drabantene og hele folkemengden, og de førte kongen ned fra Herrens hus og gikk inn i kongens hus gjennem drabantenes port; og han satte sig på kongetronen.
20 dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
Og hele folkemengden gledet sig, og byen var rolig; men Atalja hadde de drept med sverd i kongens hus.
21 Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.
Joas var syv år gammel da han blev konge.