< 2 Sarakuna 11 >

1 Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
Cependant Athalie, mère d'Achazia, voyant son fils mort, se leva et fit périr toute la race royale.
2 Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
Alors Joséba, fille du roi Joram, sœur d'Achazia, enleva Joas, fils d'Achazia, et le déroba du milieu des fils du roi qui recevaient la mort, et le recela lui et sa nourrice dans la salle des lits. Et elles le cachèrent aux regards d'Athalie en sorte qu'il ne fut pas mis à mort;
3 Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
et il fut caché six ans avec elle dans le temple de l'Éternel. Or Athalie régissait le pays.
4 A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
Et la septième année, Jehojada envoya chercher les centurions des satellites et des coureurs, et il les fit venir chez lui dans le temple de l'Éternel et conclut avec eux un accord, et les assermenta dans le temple de l'Éternel et leur montra le fils du roi.
5 Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
Et il leur donna ses ordres en ces termes: Voici ce que vous avez à faire: Un tiers d'entre vous qui entrez en service le jour du sabbat, gardera le palais royal,
6 kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
et un tiers occupera la porte Sur (latérale), et un tiers la porte derrière les coureurs, et vous garderez ainsi le palais, en arrêt.
7 ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
Et les deux sections que vous formez, vous tous qui êtes relevés le jour du sabbat [de la garde du palais], monteront la garde dans le temple de l'Éternel auprès du roi.
8 Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
Et entourez le roi de toutes parts, ayant chacun ses armes à la main; et mort à qui s'introduira entre les rangs! et accompagnez le roi à sa sortie et à son entrée.
9 Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
Et les centurions exécutèrent tous les ordres du Prêtre Jehojada, et ils prirent chacun son monde, savoir et ceux qui montaient et ceux qui descendaient la garde le jour du sabbat, et joignirent le Prêtre Jehojada.
10 Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
Et le Prêtre remit aux centurions les piques et les boucliers du roi David, qui étaient dans le temple de l'Éternel.
11 Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
Et les coureurs, chacun ses armes à la main, se portèrent depuis le côté droit au côté gauche du temple, et à l'autel vers le Temple à l'entour du roi.
12 Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
Et il produisit le fils du roi et il le couvrit de la couronne et lui remit la Loi; et ils le constituèrent roi et l'oignirent et frappèrent des mains et crièrent: Vive le Roi!
13 Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
Alors Athalie entendit les voix des coureurs et du peuple et elle se porta vers le peuple dans le temple de l'Éternel.
14 Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
Et elle regarda, et voilà que le roi se tenait sur le palier selon l'usage et aux côtés du roi les centurions et les trompettes et tout le peuple du pays joyeux et sonnant de la trompette.
15 Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
Alors Athalie déchira ses vêtements et s'écria: Complot! Complot! Mais le Prêtre Jehojada fit aux centurions, généraux de l'armée, ce commandement: Tirez-la jusqu'entre les rangs! et tuez avec l'épée quiconque la suivra! Car le Prêtre disait: Qu'elle ne reçoive pas la mort dans le temple de l'Éternel.
16 Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
Et pour lui faire place ils formèrent deux lignes, et elle arriva par la voie du passage des chevaux au palais royal, où elle reçut la mort.
17 Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
Et Jehojada solennisa l'alliance entre l'Éternel et le roi et le peuple, stipulant qu'il serait le peuple de l'Éternel, et entre le roi et le peuple.
18 Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
Alors toute la population du pays envahit le temple de Baal, et ils le démolirent et brisèrent ses autels et ses simulacres, à fond, et égorgèrent Mathan, prêtre de Baal, devant les autels. Et le Prêtre préposa des préfectures sur le temple de l'Éternel.
19 Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
Et il prit les centurions et les satellites et les coureurs et tout le peuple du pays, et ils firent descendre le roi du temple de l'Éternel, et passant par la porte des coureurs ils arrivèrent au palais royal, et le roi prit place sur le trône des rois.
20 dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
Et tout le peuple du pays était dans l'allégresse, et la ville était tranquille: quant à Athalie, ils lui avaient donné la mort avec l'épée au palais royal.
21 Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.
Joas avait sept ans à son avènement.

< 2 Sarakuna 11 >