< 2 Sarakuna 11 >

1 Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
When King Ahaziah’s mother Athaliah saw that her son had been killed, she commanded that all the members of Ahaziah’s family [who might become king] must be executed.
2 Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
So Ahaziah’s sons were all about to be murdered. But Jehosheba, who was King Jehoram’s daughter and Ahaziah’s half-sister, took Ahaziah’s [very young] son Joash and hid him and (his nursemaid/the woman who took care of him) in a bedroom [in the temple]. So he was not killed.
3 Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
He stayed with Jehosheba for six years. All during that time, he remained hidden in the temple, while Athaliah ruled [Judah].
4 A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
But during the next year, Jehoiada the Supreme Priest summoned the officers who supervised the royal bodyguards and the palace guards. He told them to come to the temple. There he required them to solemnly promise that they would do what he told them to do. And he showed King Ahaziah’s son Joash to them.
5 Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
He gave them these instructions: “There are three groups of you guards. When one group finishes their work on the Sabbath day, [divide yourselves into] three smaller groups. One group must guard the palace.
6 kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
Another group must guard at the Sur Gate. The other group must guard at the gate behind the other groups.
7 ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
The two groups that are not working on the Sabbath day must guard the temple [to protect little King Joash].
8 Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
You must stand around the king wherever he goes, with your weapons in your hands. You must kill anyone who comes near you.”
9 Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
The officers [who supervised the guards] did what Jehoiada told them to do. Each one brought to Jehoiada the guards that he supervised—the guards who were just finishing their work and those who were about to start their work on the Sabbath day.
10 Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
The priest distributed to the commanders of the guards the spears and shields that had belonged to King David, that were kept/stored in the temple.
11 Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
Then he commanded all the guards to stand in their positions, each one with his sword in his hand, all around the young king.
12 Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
Then he brought Joash out. He put the crown on his head and gave him a scroll on which were written the rules [that the kings needed to obey]. Then he poured some olive oil on Joash’s head and proclaimed that he was now the king. The people all clapped their hands and shouted, “We desire/hope that the king will live for many years!”
13 Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
When Athaliah heard the noise that was being made by the guards and the other people, she ran to the temple, where the people were gathered.
14 Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
She saw the new king standing there alongside one of the big pillars, which was the place at the temple where the kings usually stood. She saw that he was surrounded by the temple officers and men blowing trumpets, and that the people were shouting joyfully, and [some of] them were also blowing trumpets. She tore her clothes [to show her distress] and shouted, “You are traitors! You have tricked/deceived me!”
15 Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
Jehoiada [immediately] said, “Kill her, but do not kill her here at the temple of Yahweh! Take her away between two rows of guards. And kill anyone who tries to rescue her!”
16 Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
[She tried to flee, but] the guards seized her and took her to the palace, to the place where horses enter the courtyard. They killed her there.
17 Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
Then Jehoiada made a solemn agreement between the king and the people, that they would always (obey/be faithful to) Yahweh. He also made an agreement requiring the people to be loyal to Joash their king.
18 Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
Then all the people of Israel who were there went to the temple of Baal and tore it down. They smashed the altars and the statues of Baal. They also killed Mattan, the priest of Baal, in front of the altars. Jehoiada stationed/put guards at the temple of Yahweh.
19 Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
Then he and the officers of the temple, the officers who supervised the royal bodyguards, and the king’s bodyguards brought the king from the temple to the palace. All the people [followed them]. Joash entered the palace at the Guard Gate and sat down on the throne, [which showed that he was the new king].
20 dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
All the people of Judah rejoiced. And because Athaliah had been killed, the city was quiet/calm.
21 Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.
Joash was seven years old when he became the king [of Judah].

< 2 Sarakuna 11 >