< 2 Sarakuna 10 >

1 To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
И Ахааву беша седмьдесят сынове во Самарии. И написа писание Ииуй и посла в Самарию ко князем Самарийским и к старейшинам и ко кормителем сынов Ахаавлих, глаголя:
2 “Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
и ныне егда приидет писание сие к вам, и с вами сынове господина вашего, и с вами колесницы и кони, и грады тверды и оружия:
3 sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
и узрите благаго и праваго в сынех господина вашего, и поставите его на престоле отца его, и да воюете о доме господина вашего.
4 Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
И убояшася зело и реша: се, два царя не возмогоста стати противу лицу его, и како мы станем?
5 Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
И послаша иже над домом и иже над градом, и старейшины, и кормителе ко Ииую, глаголголюще: отроцы мы твои, и елика аще речеши к нам, сотворим: не воцарим мужа, благое пред очима твоима сотворим.
6 Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
И написа к ним Ииуй писание второе, глаголя: аще вы мои и гласа моего вы послушаете, возмите главы мужей сынов господина вашего и принесите ко мне, якоже час утро, во Иезраель. И бе сынов царевых седмьдесят мужей, сии началницы града вскормиша их.
7 Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
И бысть егда прииде к ним писание, и взяша сыны царевы и заклаша их седмьдесят мужей, и возложиша главы их в кошницы и послаша их к нему во Иезраель.
8 Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
И прииде вестник, и возвести ему, глаголя: принесоша главы сынов царевых. И рече: положите я в два холма при вратех града до заутра.
9 Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
И бысть заутра, и изыде и ста во вратех града, и рече ко всем людем: праведни вы: се, аз есмь, обратихся на господина моего и убих его: и кто порази всех сих?
10 Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
Видите убо, яко не падет от глагола Господня на землю, егоже глагола Господь на дом Ахаавль: и Господь сотвори, елика глагола рукою раба Своего Илии.
11 Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
И изби Ииуй всех оставшихся в дому Ахаавли во Иезраели, и вся вельможы его, и знаемыя его, и жерцы его, яко не остатися его останку.
12 Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
И воста и иде в Самарию сам, в Вефакад пастырский при пути.
13 sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
И Ииуй обрете братию Охозии царя Иудина и рече: кто вы? И реша: братия Охозиины мы, и снидохом поздравити сыны царевы и сыны обладающия.
14 Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
И рече: поимите я живы. И взяша их живых, и заклаша их в Вефакаде, четыредесять два мужа: и не остави мужа от них.
15 Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
И иде оттуду, и обрете Ионадава сына Рихавля на пути во сретение себе, и благослови его. И рече к нему Ииуй: аще есть сердце твое с сердцем моим право, якоже сердце мое с сердцем твоим? И рече Ионадав: есть. И рече Ииуй: и аще есть, даждь руку твою. И даде руку свою. И возведе его к себе на колесницу
16 Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
и рече к нему: гряди со мною и виждь, внегда ревновати мне по Господе саваофе. И посади его на колесницу свою.
17 Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
И вниде в Самарию, и изби всех оставшихся Ахаавлих в Самарии, дондеже истребити ему по глаголу Господню, егоже глагола ко Илии.
18 Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
И собра Ииуй вся люди и рече к ним: Ахаав поработа Ваалу мало, Ииуй же поработает ему много:
19 Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
и ныне вся пророки Вааловы, вся рабы его и жерцы его призовите ко мне, муж да не потаится, яко жертва велика Ваалу: и всяк иже потаится, не будет жив. И Ииуй сотвори лестию, да погубит рабы Вааловы.
20 Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
И рече Ииуй: освятите жертву Ваалу и служение. И проповедаша.
21 Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
И посла Ииуй во весь Израиль и рече, глаголя: и ныне вси раби Вааловы, и вси жерцы его, и вси пророцы его, да никтоже останется, яко жертву велику творю: иже останется, не будет жив и приидоша вси раби Вааловы, и вси жерцы его, и вси пророцы его: не остася муж, иже не прииде: и внидоша во храм Ваалов, и наполнися храм Ваалов от края да края.
22 Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
И рече Ииуй к сущым над домом одежд: изнесите одежды всем рабом Вааловым. И изнесе им ризохранитель.
23 Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
И вниде Ииуй и Ионадав сын Рихавль в храмину Ваалову и рече рабом Вааловым: испытайте и видите, аще есть с вами от рабов Господних, и вышлите всех рабов Господних обретшихся тамо. И бысть якоже глагола Ииуй, яко не бе от рабов Господних, но токмо едини раби Вааловы.
24 Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
И вниде сотворити жертвы и всесожжения и Ииуй постави себе вне осмьдесят мужей и рече: муж иже аще угонзет от мужей, ихже аз извожду в руки вашя, душа его вместо души его.
25 Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
И бысть егда сконча творяй всесожжения, и рече Ииуй предтекущым и тристатом: вшедше избийте их, да не изыдет от них муж. И избиша их острием меча и повергоша предтекущии и тристаты, и идоша даже до града храма Ваалова:
26 suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
и изнесоша кумир Ваалов и сожгоша его:
27 Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
и разбиша кумиры Вааловы, и низвергоша дом Ваалов, и определиша его на афедрон даже до дне сего.
28 Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
И погуби Ииуй храм Ваалов от Израиля.
29 Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
Обаче от грехов Иеровоама сына Наватова, иже введе в грех Израиля, не отступи Ииуй от последования их: юницы златыя, яже в Вефили и в Дане.
30 Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
И рече Господь ко Ииую: за сия, елика ублажил еси сотворити правое пред очима Моима, и вся елика по сердцу Моему сотворил еси дому Ахаавлю, сынове твои до четвертаго рода сядут на престоле во Израили.
31 Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
И Ииуй не сохрани ходити в законе Господни всем сердцем своим: не отступи от грехов Иеровоама сына Наватова, иже в грех введе Израиля.
32 A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
Во дни оны нача Господь посецати во Израили: и порази их Азаил во всех пределех Израилевых,
33 gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
от Иордана на восток солнца, всю землю Галаадску и Гаддииску, и Рувимову и Манассиину, от Ароира, иже есть при устии потока Арнонска, и Галаад и Васан.
34 Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
И прочая словес Ииуевых, и вся яже сотвори, и вся сила его, и совещания, яже совеща, не се ли, сия написана в книзе словес дний царей Израилевых?
35 Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
И успе Ииуй со отцы своими, и погребоша его в Самарии. И воцарися Иоахаз сын его вместо его.
36 Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.
И дний бяше, в няже Ииуй царствова над Израилем в Самарии, двадесять осмь лет.

< 2 Sarakuna 10 >