< 2 Sarakuna 10 >
1 To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
Or Achab avait soixante-dix fils à Samarie. Jéhu écrivit des lettres et les envoya à Samarie, aux chefs de Jizreel, aux anciens, et à ceux qui avaient élevé les fils d'Achab, en disant:
2 “Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
« Maintenant, dès que cette lettre vous parviendra, puisque les fils de votre maître sont avec vous, et que vous avez des chars et des chevaux, une ville fortifiée et des armes,
3 sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
choisissez le meilleur et le plus apte des fils de votre maître, mettez-le sur le trône de son père, et combattez pour la maison de votre maître. »
4 Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
Mais ils eurent très peur et dirent: « Voici, les deux rois ne se sont pas tenus devant lui! Comment allons-nous donc nous tenir debout? »
5 Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
Celui qui était à la tête de la maison, celui qui était à la tête de la ville, les anciens aussi, et ceux qui élevaient les enfants, envoyèrent dire à Jéhu: « Nous sommes tes serviteurs, et nous ferons tout ce que tu nous demanderas. Nous ne ferons pas de roi un autre homme. Fais ce qui est bon à tes yeux. »
6 Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
Puis il leur écrivit une seconde fois une lettre dans laquelle il disait: « Si vous êtes de mon côté, et si vous écoutez ma voix, prenez les têtes des hommes qui sont les fils de vos maîtres, et venez me voir à Jizreel demain à cette heure-ci. » Or les fils du roi, au nombre de soixante-dix personnes, étaient avec les grands de la ville, qui les firent monter.
7 Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
Lorsque la lettre leur parvint, ils prirent les fils du roi, les tuèrent, soit soixante-dix personnes, mirent leurs têtes dans des paniers, et les envoyèrent à Jizreel.
8 Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
Un messager vint lui dire: « On a apporté les têtes des fils du roi. » Il dit: « Disposez-les en deux tas à l'entrée de la porte jusqu'au matin. »
9 Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
Au matin, il sortit, se tint debout, et dit à tout le peuple: « Vous êtes justes. Voici, j'ai conspiré contre mon maître et je l'ai tué, mais qui a tué tous ceux-là?
10 Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
Sachez maintenant que rien ne tombera à terre de la parole de l'Éternel, que l'Éternel a prononcée sur la maison d'Achab. Car Yahvé a accompli ce qu'il avait annoncé par son serviteur Élie. »
11 Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
Et Jéhu frappa tout ce qui restait de la maison d'Achab à Jizreel, avec tous ses grands, ses familiers et ses prêtres, jusqu'à ce qu'il ne lui restât plus personne.
12 Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
Il se leva, partit, et se rendit à Samarie. Comme il se trouvait en chemin dans la bergerie des bergers,
13 sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
Jéhu rencontra les frères d'Achazia, roi de Juda, et dit: « Qui êtes-vous? » Ils répondirent: « Nous sommes les frères d'Achazia. Nous descendons saluer les enfants du roi et les enfants de la reine. »
14 Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
Il a dit: « Prenez-les vivants! » Ils les prirent vivants, et les tuèrent à la fosse de la tondeuse, même quarante-deux hommes. Il n'en a laissé aucun.
15 Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
Comme il était parti de là, il rencontra Jehonadab, fils de Rechab, qui venait à sa rencontre. Il le salua, et lui dit: « Ton cœur est-il droit, comme mon cœur est avec ton cœur? » Jehonadab a répondu: « C'est vrai. » « Si c'est le cas, donne-moi ta main. » Il lui donna sa main, et il le fit monter vers lui dans le char.
16 Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
Il dit: « Viens avec moi, et vois mon zèle pour Yahvé. » Et ils le firent monter dans son char.
17 Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
Lorsqu'il arriva à Samarie, il frappa tous ceux qui restaient à Achab à Samarie, jusqu'à ce qu'il les eût détruits, selon la parole de l'Éternel qu'il avait adressée à Élie.
18 Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
Jéhu rassembla tout le peuple et leur dit: « Achab a un peu servi Baal, mais Jéhu le servira beaucoup.
19 Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
Maintenant, appelez-moi tous les prophètes de Baal, tous ses adorateurs et tous ses prêtres. Que personne ne soit absent, car j'ai un grand sacrifice à offrir à Baal. Celui qui sera absent ne vivra pas. » Mais Jéhu agit de manière trompeuse, avec l'intention de détruire les adorateurs de Baal.
20 Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
Jéhu a dit: « Sanctifiez une assemblée solennelle pour Baal! » Et ils le proclamèrent.
21 Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
Jéhu envoya par tout Israël; et tous les adorateurs de Baal vinrent, de sorte qu'il ne resta pas un homme qui ne vint pas. Ils entrèrent dans la maison de Baal, et la maison de Baal fut remplie d'un bout à l'autre.
22 Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
Il dit à celui qui gardait l'armoire: « Sortez des robes pour tous les adorateurs de Baal! ». Il leur apporta donc des robes.
23 Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
Jéhu entra avec Jéhonadab, fils de Réchab, dans la maison de Baal. Il dit alors aux adorateurs de Baal: « Cherchez, et voyez qu'il n'y a ici avec vous aucun des serviteurs de Yahvé, mais seulement les adorateurs de Baal. »
24 Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
Et ils entrèrent pour offrir des sacrifices et des holocaustes. Or Jéhu s'était désigné quatre-vingts hommes à l'extérieur, et il avait dit: « Si l'un des hommes que je livre entre tes mains s'échappe, celui qui le laissera partir en aura pour sa vie. »
25 Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
Dès qu'il eut fini d'offrir l'holocauste, Jéhu dit à la garde et aux chefs: « Entrez et tuez-les! Que personne n'échappe. » Ils les frappèrent donc du tranchant de l'épée. La garde et les chefs jetèrent les cadavres dehors et allèrent dans le sanctuaire intérieur de la maison de Baal.
26 suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
Ils sortirent les colonnes qui étaient dans la maison de Baal et les brûlèrent.
27 Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
Ils démolirent la colonne de Baal, ils démolirent la maison de Baal, et ils en firent une latrine, jusqu'à ce jour.
28 Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
Ainsi Jéhu détruisit Baal hors d'Israël.
29 Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
Cependant, Jéhu ne se détourna pas des péchés de Jéroboam, fils de Nebat, par lesquels il avait fait pécher Israël, à savoir les veaux d'or qui étaient à Béthel et ceux qui étaient à Dan.
30 Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
Yahvé dit à Jéhu: « Parce que tu as bien exécuté ce qui est juste à mes yeux, et que tu as fait à la maison d'Achab tout ce qui était dans mon cœur, tes descendants s'assiéront sur le trône d'Israël jusqu'à la quatrième génération. »
31 Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
Mais Jéhu ne prit pas garde de marcher de tout son cœur dans la loi de Yahvé, le Dieu d'Israël. Il ne s'est pas détourné des péchés de Jéroboam, par lesquels il avait fait pécher Israël.
32 A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
En ces jours-là, l'Éternel commença à retrancher des parties d'Israël, et Hazaël les frappa dans tout le territoire d'Israël
33 gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
depuis le Jourdain vers l'orient, tout le pays de Galaad, les Gadites, les Rubénites et les Manassites, depuis Aroër, qui est près du torrent de l'Arnon, jusqu'à Galaad et Basan.
34 Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Et le reste des actes de Jéhu, et tout ce qu'il a fait, et toute sa puissance, n'est-ce pas écrit dans le livre des chroniques des rois d'Israël?
35 Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
Jéhu se coucha avec ses pères, et on l'enterra à Samarie. Joachaz, son fils, régna à sa place.
36 Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.
Le temps que Jéhu régna sur Israël à Samarie fut de vingt-huit ans.