< 2 Sarakuna 10 >

1 To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
Forsothe seuenti sones in Samarie weren to Achab. Therfor Hieu wroot lettris, and sente in to Samarie to the beste men of the citee, and to the gretter men in birthe, and to alle the nurschis of Achab, and seide,
2 “Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
Anoon as ye han take these lettris, ye that han the sones of youre lord, and the charis, and horsis, and stronge citees, and armeris,
3 sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
chese the beste, and hym that plesith to you of the sones of youre lord, and sette ye him on the trone of his fadir, and fiyte ye for the hows of youre lord.
4 Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
And thei dredden greetli, and seiden, Lo! twei kyngis myyten not stonde bifor hym, and how schulen we mowe ayenstonde hym?
5 Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
Therfor the souereyns of the hows, and the prefect of the citee, and the grettere men in birthe, and the nurchis senten to Hieu, and seiden, We ben thi seruauntis; what euer thingis thou comaundist, we schulen do, and we schulen not make a kyng to vs; do thou what euer thing plesith thee.
6 Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
Forsothe he wroot ayen to hem lettris the secunde tyme, and seide, If ye ben myne, and obeien to me, take ye the heedis of the sones of youre lord, and come ye to me in this same our to morewe in to Jezrael. Sotheli the sones of the kyng, seuenti men, weren nurschid at the beste men of the citee.
7 Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
And whanne the lettris hadden come to hem, thei token the sones of the kyng, and killiden seuenti men, and puttiden the heedis of hem in coffyns; and senten to hym in to Jezrael.
8 Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
Forsothe a messanger cam to hym, and schewide to hym, and seide, Thei han brouyt the heedis of the sones of the king. Which answeride, Putte ye tho heedis to tweyne hepis, bisidis the entring of the yate, til the morewtid.
9 Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
And whanne it was cleer dai, he yede out, and stood, and seide to al the puple, Ye ben iust men; if Y conspiride ayens my lord, and killide hym, who killide alle these?
10 Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
Therfor se ye now, that noon of the wordis of the Lord felde doun in to the erthe, whiche the Lord spak on the hows of Achab; and the Lord hath do that, that he spak in the hond of his seruaunt, Elie.
11 Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
Therfor Hieu smoot alle that weren residue of the hows of Achab in Jezrael, and alle the beste men of hym, and knowun men, and preestis, til no relikis of hym leften.
12 Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
And he roos, and cam in to Samarie; and whanne he hadde come to the chaumbir of schepherdis in the weie,
13 sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
he foond the britheren of Ocozie, kyng of Juda; and he seide to hem, Who ben ye? And thei answeriden, We ben the britheren of Ocozie, and we comen doun to grete the sones of the kyng and the sones of the queen.
14 Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
Which Hieu seide, Take ye hem quyke. And whanne thei hadden take hem quyke, thei strangliden hem in the cisterne, bisidis the chaumbre, two and fourti men; and he lefte not ony of hem.
15 Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
And whanne he hadde go fro thennus, he foond Jonadab, the sone of Rechab, in to meetyng of hym; and he blesside hym. And Hieu seide to hym, Whether thin herte is riytful with myn herte, as myn herte is with thin herte? And Jonadab seide, It is. Hieu seide, If `it is, yyue thin hond. Which yaf his hond to hym; and he reiside hym to hym silf in to the chare.
16 Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
And he seide to hym, Come thou with me, and se my feruent loue for the Lord.
17 Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
And he ledde hym, put in hys chare, in to Samarie. And he killide alle men that weren residue of Achab in Samarie `til to oon, bi the word of the Lord, which he spak bi Elie.
18 Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
Therfor Hieu gaderide to gidere alle the puple, and seide to hem, Achab worschipide Baal a litil, but Y schal worschipe hym more.
19 Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
Now therfor clepe ye to me alle the prophetis of Baal, and alle hise seruauntis, and alle hise preestis; `noon be that come not, for grete sacrifice is of me to Baal; who euer schal faile, he schal not lyue. Forsothe Hieu dide this bi tresoun, that he schulde distrie alle the worschipers of Baal.
20 Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
And he seide, Halewe ye a solempne day to Baal.
21 Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
And he clepide, and sente in to alle the termes of Israel; and alle the seruauntis of Baal camen, `noon was residue, and sotheli `not oon was that cam not. And thei entriden in to the temple of Baal; and the hows of Baal was fillid, fro oon ende `til to `the tothir.
22 Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
And he seide to hem that weren souereyns ouer the clothis, Bringe ye forth clothis to alle the seruauntis of Baal; and thei brouyten forth clothis to hem.
23 Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
And Hieu entride, and Jonadab, the sone of Rechab, in to the temple of Baal. And Hieu seide to the worschiperis of Baal, Enquere ye, and se, lest perauenture ony of the seruauntis of the Lord be with you; but that the seruauntis be aloone of Baal.
24 Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
Therfor thei entriden, to make slayn sacrifices, and brent sacrifices. Sotheli Hieu hadde maad redi to hym with outforth foure scoore men, and hadde seid to hem, Who euer schal fle of alle these, whiche Y schal brynge in to youre hondis, the lijf of hym schal be for the lijf of hym that ascapith.
25 Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
Forsothe it was don, whanne the brent sacrifice was fillid, Hieu comaundide to hise knyytis and duykis, Entre ye, and sle hem, that noon ascape. And the knyytis and duykis smytiden `hem bi the scharpnesse of swerd, and castiden forth. And `thei yeden into the citee of the temple of Baal,
26 suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
and thei brouyten forth the ymage fro the temple of Baal,
27 Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
and brenten it, and al to braken it. Also thei destrieden the hows of Baal, and maden priuyes for it `til in to this dai.
28 Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
Therfor Hieu dide awei Baal fro Israel;
29 Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
netheles he yede not awei fro the synnes of Jeroboam, sone of Nabath, that made Israel to do synne, nether he forsook the goldun caluys, that weren in Bethel and in Dan.
30 Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
Forsothe the Lord seide to Hieu, For thou didist bisili that that was riytful, and pleside in myn yyen, and hast do ayens the hows of Achab alle thingis that weren in myn herte, thi sones `til to the fourthe generacioun schulen sitte on the trone of Israel.
31 Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
Forsothe Hieu kepte not, that he yede in the lawe of the Lord God of Israel in al his herte; for he yede not awei fro the synnes of Jeroboam, that made Israel to do synne.
32 A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
In tho daies the Lord bigan to be anoyed on Israel; and Asahel smoot hem in alle the coostis of Israel,
33 gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
fro Jordan ayens the eest coost, al the lond of Galaad, and of Gad, and of Ruben, and of Manasses, fro Aroer which is on the stronde of Arnon, and Galaad, and Baasan.
34 Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
Forsothe the residue of wordis of Hieu, and alle thingis whiche he dide, and his strengthe, whether these ben not writun in the book of wordis of daies of the kyngis of Israel?
35 Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
And Hieu slepte with hise fadris; and thei birieden hym in Samarie; and Joachaz, his sone, regnyde for hym.
36 Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.
Forsothe the daies, in whiche Hieu regnede on Israel in Samarie, ben eiyte and twenti yeer.

< 2 Sarakuna 10 >