< 2 Sarakuna 10 >

1 To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
There were seventy descendants of King Ahab who were living there in Samaria. Jehu wrote a letter [and made copies of it] and sent them to the rulers of the city, to the elders, and to those who raised and tutored Ahab’s children.
2 “Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
[This is what he wrote]: “You are the ones who are [taking care of] the king’s descendants. You have chariots and horses and weapons, and you live in cities that have walls around them. So as soon as you receive this letter,
3 sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
choose one of the king’s sons, the one who is the best qualified, and appoint him to be your king. Then [prepare to] fight to defend him.”
4 Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
But [when they got those letters from Jehu and read them], they became very afraid. They said, “King Joram and King Ahaziah could not resist him; (how can we resist him?/we cannot possibly resist him!)” [RHQ]
5 Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
So the officer who was in charge of the palace and the mayor of the city sent a message to Jehu saying, “We want to serve you, and we are ready to do whatever you tell us to do. We will not appoint anyone to become our king. You do whatever you think is best.”
6 Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
So Jehu sent a second letter to them, writing this: “If you (are on my side/want to help me), and if you are ready to obey me, [kill] King Ahab’s descendants [and cut off their heads and] bring their heads to me here in Jezreel at this time tomorrow.” The seventy descendants of King Ahab were being brought up and supervised by the leaders of [Samaria] city.
7 Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
When they received the letter from Jehu, they killed all seventy of Ahab’s descendants and [cut off their heads]. They put their heads in baskets and sent them to Jehu at Jezreel.
8 Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
A messenger came to Jehu and told him, “They have brought the heads of Ahab’s descendants.” So Jehu commanded that the heads should be put in two piles at the city gate and that the heads should stay there until the next morning.
9 Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
The next morning he went out [to the city gate] and said to all the people, “I am the one who plotted against King Joram and killed him. You are not guilty of doing that. But [it was Yahweh, not I] [RHQ] who [commanded that] all these [descendants of Ahab should be] killed.
10 Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
So you need to know that everything that Yahweh said would happen has happened. He has caused to happen what he told the prophet Elijah would happen.”
11 Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
Then Jehu executed all the other relatives of Ahab in Jezreel, and all Ahab’s officers, and close friends, and his priests. He did not allow any of them to remain alive.
12 Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
Then Jehu left [Jezreel] and went toward Samaria. While he was going there, at a place called ‘Shepherds’ Camp’,
13 sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
he met some relatives of King Ahaziah of Judah. He asked them, “Who are you?” They replied, “We are relatives of King Ahaziah. We are going to Jezreel to visit the children of Queen Jezebel and the other members of King [Joram’s] family.”
14 Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
Jehu said to his men, “Seize them!” So they seized them and killed all of them at the pit named Beth-Eked. There were 42 people whom they killed; they did not allow any of them to remain alive.
15 Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
Then Jehu [continued to travel toward Samaria]. Along the road, he was met by Jonadab, a leader of the Rechab clan. Jehu greeted him and said to him, “Are you as devoted to me [IDM] as I am devoted to you?” Jonadab replied, “Yes, I am.” Jehu said, “If you are, shake hands with me.” So Jonadab shook hands with him, and Jehu helped him to get into his chariot.
16 Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
Jehu said to him, “Come with me, and you will see that I am very devoted to Yahweh.” So they rode together to Samaria.
17 Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
When they arrived in Samaria, Jehu killed all of Ahab’s relatives who were still alive. He did not (spare any of them/allow any of them to remain alive). That was what Yahweh told Elijah would happen.
18 Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
Then Jehu summoned all the people [of Samaria], and said to them, “King Ahab was devoted to [your god] Baal a little bit, but I will serve him much more.
19 Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
So now summon all the prophets of Baal, all of Baal’s priests, and all the others who worship Baal. I am going to make a great sacrifice to Baal. I want all of them to be there. Any of them who is not there will be executed.” But Jehu was planning to trick them; he was planning to kill all those who worshiped Baal.
20 Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
Then Jehu commanded, “Announce that we are going to set aside a day to honor Baal.” So they did that.
21 Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
Jehu [decided what day they would gather and] sent messages throughout Israel [telling everyone what day to gather on], and on that day, everyone who worshiped Baal came. No one stayed at home. They all went into the huge temple of Baal and filled it from one end to the other.
22 Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
Jehu told the priest who took care of the sacred robes to bring them out and give them to the people who worshiped Baal. So the priest did that.
23 Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
Then Jehu went into the temple of Baal with Jonadab, and he said to the people who were there to worship Baal, “Be sure that only those who worship Baal are here. Be sure that no one who worships Yahweh has come in.”
24 Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
Then he and Jonadab prepared to offer sacrifices and other offerings to Baal that would be completely burned [on the altar that was there in Samaria]. But Jehu had stationed eighty of his men outside the temple, and had said to them, “I want you to kill all the people [who are in the temple]. Anyone who allows one of them to escape will be executed!”
25 Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
As soon as Jehu [and Jonadab] had finished killing the animals that would be completely burned to be an offering to Baal, they [went outside and] said to the guards and officers, “Go in and kill all of them! Do not allow any of them to escape!” So the guards and officers went in and killed them all with their swords. Then they dragged their corpses outside the temple. Then they went into the inner room of the temple,
26 suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
and they carried out the sacred pillar of Baal that was there, and they burned it.
27 Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
So they destroyed that pillar that honored Baal, and then they burned down the temple, and made it a public toilet. And it is still a toilet!
28 Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
That is how Jehu got rid of the worship of Baal in Israel.
29 Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
But Jehu did not quit committing the kinds of sins that Jeroboam had committed, sins that led the people of Israel to sin by worshiping the gold [statues of] calves in Bethel and Dan [cities].
30 Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
Then Yahweh said to Jehu, “You have done what pleased me by getting rid of all of Ahab’s descendants. So I promise you that your son and grandson and great-grandson and great-great-grandson will all be kings of Israel.”
31 Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
But Jehu did not obey all the laws of Yahweh, the God of the Israeli people. He did not stop committing the sins that Jeroboam had committed, sins that led the Israeli people to sin.
32 A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
At that time, Yahweh began to cause the territory controlled by Israel to become smaller. [The army of] King Hazael [of Syria] conquered much of the Israeli territory.
33 gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
He conquered the parts east of the Jordan [River], as far south as Aroer [town] on the Arnon [River]. That included [the] Gilead and Bashan [regions], where the tribes of Gad, Reuben, and half of the tribe of Manasseh lived.
34 Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
[If you want to read more] about all the other things that Jehu did [RHQ], they are written in the scroll called ‘The History of the Kings of Israel’.
35 Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
Jehu died [EUP], and was buried in Samaria. His son Jehoahaz became the king in place of his father.
36 Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.
Jehu had ruled in Samaria as the king of Israel for twenty-eight years.

< 2 Sarakuna 10 >