< 2 Sarakuna 1 >

1 Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
Efter Akabs død falt Moab fra Israel.
2 Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
Akasja falt ut gjennem gitteret i sin sal i Samaria og blev syk. Da skikket han nogen sendebud avsted og sa til dem: Gå og spør Ba'al-Sebub, Ekrons gud, om jeg skal komme mig av denne sykdom!
3 Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
Men Herrens engel sa til tisbitten Elias: Gjør dig rede og gå sendebudene fra Samarias konge i møte og si til dem: Er det fordi det ingen Gud er i Israel, at I går avsted og spør Ba'al-Sebub, Ekrons gud?
4 Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
Derfor sier Herren så: Du skal ikke stige ned fra den seng du er steget op i; du skal dø. Dermed gikk Elias.
5 Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
Da sendebudene vendte tilbake til ham, spurte han dem: Hvorfor er I vendt tilbake?
6 Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
De svarte: En mann kom oss i møte og sa til oss: Gå tilbake til kongen som har sendt eder, og si til ham: Så sier Herren: Er det fordi det ingen Gud er i Israel, at du sender bud for å spørre Ba'al-Sebub, Ekrons gud? Derfor skal du ikke stige ned fra den seng du er steget op i; du skal dø.
7 Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
Han spurte dem: Hvorledes så den mann ut som kom eder i møte og talte således til eder?
8 Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
De svarte: Det var en mann i en lodden kjortel, med et lærbelte bundet om lendene. Da sa han: Det var tisbitten Elias.
9 Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
Og han sendte til ham en høvedsmann over femti med sine menn; og han gikk op til ham, der han satt på toppen av fjellet, og han sa til ham: Du Guds mann! Kongen sier: Kom ned!
10 Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
Men Elias svarte høvedsmannen over femti: Er jeg en Guds mann, så fare ild ned fra himmelen og fortære dig og dine femti mann! Da fór det ild ned fra himmelen og fortærte ham og hans femti mann.
11 Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
Så sendte han til ham en annen høvedsmann over femti med sine menn; og han tok til orde og sa til ham: Du Guds mann! Så sier kongen: Kom straks ned!
12 Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
Men Elias svarte dem: Er jeg en Guds mann, så fare ild ned fra himmelen og fortære dig og dine femti mann! Da fór Guds ild ned fra himmelen og fortærte ham og hans femti mann.
13 Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
Så sendte han igjen en tredje høvedsmann over femti med sine menn; og denne tredje høvedsmann gikk op til Elias og falt på kne for ham og bønnfalt ham og sa til ham: Du Guds mann! La mitt liv og disse dine femti tjeneres liv være dyrt i dine øine!
14 Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
Ild fór ned fra himmelen og fortærte begge de første høvedsmenn over femti med sine menn; men la nu mitt liv være dyrt i dine øine!
15 Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
Da sa Herrens engel til Elias: Gå ned med ham, og vær ikke redd ham! Så stod han op og gikk med ham ned til kongen.
16 Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
Og han sa til ham: Så sier Herren: Fordi du skikket sendebud og vilde spørre Ba'al-Sebub, Ekrons gud, som om det ingen Gud var i Israel som du kunde spørre derom - derfor skal du ikke stige ned fra den seng du er steget op i; du skal dø.
17 Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
Og han døde efter det Herrens ord som Elias hadde talt, og Joram blev konge i hans sted i Judas konge Jorams, Josafats sønns annet år; for han hadde ikke nogen sønn.
18 Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?
Hvad som ellers er å fortelle om Akasja og det han gjorde, det er opskrevet i Israels kongers krønike.

< 2 Sarakuna 1 >