< 2 Yohanna 1 >
1 Dattijon nan, Zuwa ga uwargida zaɓaɓɓiya da kuma’ya’yanta, waɗanda nake ƙauna ƙwarai da gaske kuma ba ni kaɗai ba, amma har da dukan waɗanda suka san gaskiya.
THE presbyter to the elect Kuria and to her sons, whom I love in truth, nor I only, but all they who know the truth,
2 Muna ƙaunarku saboda gaskiyan nan, wadda take cikinmu za tă kuma kasance tare da mu har abada. (aiōn )
on account of the truth which abideth in us, and is with us for ever; (aiōn )
3 Alheri, jinƙai da kuma salama daga Allah Uba da kuma Yesu Kiristi, Ɗan Uba, su kasance tare da mu cikin gaskiya da ƙauna.
Grace be with you and mercy and peace, from Aloha the Father, and from Jeshu Meshiha the Son of the Father, in truth and in love.
4 Na yi farin ciki ƙwarai, da na sami waɗansu’ya’yanki suna tafiya cikin gaskiya, kamar yadda Uba ya umarce mu.
I have rejoiced much to have found of thy sons who walk in the truth, after the commandment we have received from the Father.
5 Yanzu kuma, uwargida ƙaunatacciya, ba sabon umarni nake rubuta miki ba sai dai wanda muke da shi tun farko. Ina roƙo cewa mu ƙaunaci juna.
And now I entreat thee, Kuria, -no new commandment writing to thee, but that which we have had from the beginning, -that we love one another.
6 Ƙauna, ita ce mu yi biyayya ga umarnansa. Kamar yadda kuka ji tun da fari, umarninsa shi ne ku yi zaman ƙauna.
And this is love, that we walk according to the commandment; this commandment is according to that which you have heard from the beginning, that in it we should walk.
7 Masu ruɗi da yawa, waɗanda ba su yarda da zuwan Yesu Kiristi cikin jiki ba, sun riga sun fito a duniya. Duk irin mutumin nan mai ruɗi ne kuma magabcin Kiristi.
Because many deceivers are come out into the world who confess not that Jeshu Meshiha came in the flesh. This is the deceiver and antichrist.
8 Ku lura don kada ku yi hasarar aikin da kuka yi, sai dai ku sami cikakken lada.
Be watchful of yourselves, that not any thing perish which you have wrought; but (that with) a complete reward you may be recompensed.
9 Duk mutumin da bai tsaya a kan koyarwar Kiristi ba, amma ya yi ƙari a kanta, mutumin nan ba shi da Allah. Amma wanda ya tsaya a kan koyarwar Kiristi, yana da Uban da kuma Ɗan.
Every one who transgresseth, and abideth not in the doctrine of the Meshiha, hath not Aloha. He who abideth in his doctrine, this hath both the Father and the Son.
10 Duk wanda ya zo wurinku bai kuma kawo koyarwan nan ba, kada ku karɓe shi a gidanku ko ku marabce shi.
If any one come to you, and this doctrine bring not, receive him not into the house, and "Joy to you," and " Farewell," say not to him.
11 Duk wanda ya karɓe shi yana tarayya da mugun aikinsa ke nan.
For he who saith to him, " Farewell," becometh a participator of his evil deeds.
12 Ina da abubuwa da dama da zan rubuta muku, sai dai ba na so in yi amfani da takarda da inki in rubuta. A maimako, ina fata in ziyarce ku in kuma yi magana da ku fuska da fuska, domin farin cikinmu yă zama cikakke.
Though I have many things to write to you, I will not with parchment and ink; but I hope to come to you, and mouth with mouth to speak, that our joy may be complete.
13 ’Ya’yan’yar’uwarki wadda Allah ya keɓe, suna gaishe ku.
The sons of thy elect sister ask your peace. Grace be with you. Amen.