< 2 Yohanna 1 >
1 Dattijon nan, Zuwa ga uwargida zaɓaɓɓiya da kuma’ya’yanta, waɗanda nake ƙauna ƙwarai da gaske kuma ba ni kaɗai ba, amma har da dukan waɗanda suka san gaskiya.
The elder, to Electa Cyria, and her children, whom I love sincerely; and not I only, but also all who have known the truth;
2 Muna ƙaunarku saboda gaskiyan nan, wadda take cikinmu za tă kuma kasance tare da mu har abada. (aiōn )
for the truth's sake, which is in us, and shall be with us forever: (aiōn )
3 Alheri, jinƙai da kuma salama daga Allah Uba da kuma Yesu Kiristi, Ɗan Uba, su kasance tare da mu cikin gaskiya da ƙauna.
Favor, mercy, and peace, be with you, from God the Father, and from the Lord Jesus Christ, the Son of the Father, with truth and love.
4 Na yi farin ciki ƙwarai, da na sami waɗansu’ya’yanki suna tafiya cikin gaskiya, kamar yadda Uba ya umarce mu.
I rejoiced greatly, when I found some of your children walking in truth, as we received commandment from the Father.
5 Yanzu kuma, uwargida ƙaunatacciya, ba sabon umarni nake rubuta miki ba sai dai wanda muke da shi tun farko. Ina roƙo cewa mu ƙaunaci juna.
And now I beseech you, Cyria, not as writing to you a new commandment, but that which we had from the beginning, that we love one another.
6 Ƙauna, ita ce mu yi biyayya ga umarnansa. Kamar yadda kuka ji tun da fari, umarninsa shi ne ku yi zaman ƙauna.
And this is the love that we walk according to his commandments. This is the commandment, even as you have heard from the beginning, that you may walk in it;
7 Masu ruɗi da yawa, waɗanda ba su yarda da zuwan Yesu Kiristi cikin jiki ba, sun riga sun fito a duniya. Duk irin mutumin nan mai ruɗi ne kuma magabcin Kiristi.
for many deceivers are entered into the world, who do not confess Jesus Christ did come in the flesh. This is the deceiver, and the antichrist.
8 Ku lura don kada ku yi hasarar aikin da kuka yi, sai dai ku sami cikakken lada.
Look to yourselves, that we may not lose the things which we have wrought, but may receive a full reward.
9 Duk mutumin da bai tsaya a kan koyarwar Kiristi ba, amma ya yi ƙari a kanta, mutumin nan ba shi da Allah. Amma wanda ya tsaya a kan koyarwar Kiristi, yana da Uban da kuma Ɗan.
Whoever transgresses, and does not abide in the doctrine of Christ, has not God: he who abides in the doctrine of Christ, has both the Father and the Son.
10 Duk wanda ya zo wurinku bai kuma kawo koyarwan nan ba, kada ku karɓe shi a gidanku ko ku marabce shi.
If any one come to you, and bring not this doctrine; receive him not into your house, nor wish him success:
11 Duk wanda ya karɓe shi yana tarayya da mugun aikinsa ke nan.
for he who wishes him success, partakes in his evil deeds.
12 Ina da abubuwa da dama da zan rubuta muku, sai dai ba na so in yi amfani da takarda da inki in rubuta. A maimako, ina fata in ziyarce ku in kuma yi magana da ku fuska da fuska, domin farin cikinmu yă zama cikakke.
Having many things to write to you, I did not incline to communicate them by paper and ink; because I hope to come to you, and speak face to face, that our joy may be complete.
13 ’Ya’yan’yar’uwarki wadda Allah ya keɓe, suna gaishe ku.
The children of your beloved sister, salute you.