< 2 Korintiyawa 1 >

1 Bulus, manzon Kiristi Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu, Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, tare da dukan tsarkaka a ko’ina a Akayya.
[I], Paul, who [write this letter to you], became an apostle of Christ Jesus because God chose me for that. [Timothy, our] fellow believer, [is with me. I am sending this letter] to you who are God’s people in the congregations in Corinth [city. I want] the believers who live in [other places] in Achaia [province to also read this letter].
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
[We(exc) desire] that you will [experience] God our Father and our Lord Jesus Christ [acting] kindly toward you and causing you to have [inner] peace.
3 Yabo ya tabbata ga Allah, da Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba mai tausayi, da kuma Allah na dukan ta’aziyya,
[We should] praise God, who is the father of our [(inc)] Lord Jesus Christ. He always pities us and helps us [because he is like] [MET] a father to us [and we are like his children]. He always encourages us [(inc)].
4 wanda yakan yi mana ta’aziyya a cikin dukan wahalolinmu, domin mu kuma mu iya ta’azantar da waɗanda suke cikin kowace irin wahala, da ta’aziyyar da mu kanmu muka samu daga Allah.
He has encouraged us [(exc)] whenever we suffered hardships. As a result, we [(exc)] are able to encourage others whenever they suffer hardships, just as/just like God has encouraged us [(exc)].
5 Gama kamar yadda wahalar Kiristi ta cika har tana zuba a cikin rayuwarmu, haka nan kuma ta wurin Kiristi ta’aziyyarmu ta cika har tana zuba.
It is true that just like Christ suffered, we [who serve him] also continually suffer [because we belong to him]. But also, because we [belong to] Christ, God greatly strengthens us (just as/just like) [God strengthened him].
6 In muna shan wahala, ai, muna shanta domin ta’aziyyarku, da cetonku ne, in mun sami ta’aziyya, ai, mun same ta domin ta’aziyyarku ce, wadda take sa ku jure wa irin wahalan nan, da muke sha.
So, whenever we [(exc)] experience sufferings, we [learn how to encourage] you [when you experience sufferings. As a result, you will become more and more the kind of people God] wants you to be. Whenever [God] strengthens us [(exc) when we are suffering, he] does that in order that you [may see how he makes us strong when we are suffering. Then, as God] encourages [you in that way], you will learn to continue patiently [trusting him] when you suffer as we do.
7 Begen da muke da shi dominku kuwa, tabbatacce ne, domin mun san cewa kamar yadda kuke tarayya da mu a cikin wahalolinmu, haka kuma kuke tarayya da mu a cikin ta’aziyyarmu.
As a result, we [(exc)] strongly expect that because you suffer just as/just like we do, [God] will encourage you (just as/just like) [he] encourages us.
8 ’Yan’uwa, ba ma so ku zama da rashin sani, a kan wahalolin da muka sha a lardin Asiya. Mun sha wahaloli sosai, har abin ya fi ƙarfinmu, ya sa muka fid da tsammanin rayuwa.
[Our] fellow believers, we [(exc)] want you to know [LIT] about the trouble that we suffered in Asia [province]. That trouble was so very great that it was much more than we were able to endure. As a result, we [(exc)] thought that we would certainly die.
9 Ba shakka, a zuciyarmu mun ji kamar hukuncin kisa ne aka yi mana. Wannan kuwa ya faru ne domin kada mu dogara da kanmu, sai dai ga Allah, wanda yake tā da matattu.
Indeed, we felt [like a person feels when he has heard a judge say], “I condemn you to die/be executed [MET].” But [God allowed us to think that we were going to die] so that we would not (rely on/trust in) our own [strength. He wanted us] instead [to rely] only on his [strength, because he] is the one who [has power even to make] those who have died live [again].
10 Shi ya cece mu daga irin wannan hatsari na mutuwa, zai kuwa cece mu. A kansa muka kafa bege cewa zai ci gaba da cetonmu,
And [even though] we [(exc)] were [in terrible danger and were] about to die, God rescued us. And he will continue to rescue us [whenever we are in trouble]. We confidently expect that he will continue to rescue us [time after time].
11 yayinda kuke taimakonmu ta wurin addu’o’inku. Mutane da yawa kuwa za su yi godiya ta dalilinmu, saboda albarkar da aka yi mana, ta amsa addu’o’i masu yawa.
[And we are also relying on] you to help us by praying for us [(exc)]. [If many people pray for us], many people will also thank [God] when [he] kindly answers those many prayers [and delivers us from danger].
12 Wannan shi ne taƙamarmu. Lamirinmu yana ba da shaida cewa mun yi zamanmu a duniya, musamman a dangantakarmu da ku cikin tsarki, tsakani da Allah. Mun yi haka ta wurin bishewar alherin Allah, ba bisa ga hikimar duniya ba.
I am happy [to say] that I have behaved toward all people [MTY] in an honest and sincere way. My conscience assures me [that this is true]. Especially, I have behaved toward you [honestly and sincerely because that is what] God wants us to do. As I have done that, [my thoughts] have not been the thoughts that unbelieving people [MTY] [think are] wise. Instead, [I have behaved toward people only as God wants me to, depending on] God to help me in ways that I do not deserve.
13 Gama ba mu rubuta muku abin da ba za ku iya karatu ko ku kāsa fahimta ba. Ina kuma fata cewa,
[I say that] because [in all my letters to you] I have always written [LIT] clearly in a way that you can easily and completely understand [when you] read them.
14 kamar yadda kuka ɗan fahimce mu, za ku kai ga cikakkiyar fahimta cewa za ku iya yin taƙama da mu, kamar yadda mu ma za mu yi taƙama da ku a ranar da Ubangiji Yesu zai dawo.
[Previously some of] you, but not all of you, have completely understood [that I am always honest and sincere with you]. But I confidently expect that [soon] you will all be fully convinced [about that]. Then when the Lord Jesus [MTY] [returns, you will all be able to say that] you are pleased with me, just like I will [be able to say that] I am pleased with you.
15 Saboda na amince da haka, shi ya sa na so zuwa wurinku da fari, domin ku sami albarka riɓi biyu.
It was because I felt sure [that all of you were pleased with me] that I was planning to visit you on my way from [here] to Macedonia [province]. I also planned to visit you again on my way back from there, so that I could [spend time with you] twice, and be able to help you more, and I was hoping that you would [give me things that I needed] [EUP] for my journey to Judea [province].
16 Na yi shiri in ziyarce ku a kan hanyata zuwa Makidoniya, in kuma sāke dawo wurinku a kan hanyata daga Makidoniya, sa’an nan ku yi mini rakiya a hanyata zuwa Yahudiya.
17 Kuna gani na yi wannan shirin ba da sanin abin da nake yi ba ne? Ko kuwa, kuna gani na yi shirin nan da halin mutuntaka ne, don in ce, “I” in koma in ce, “A’a”?
So then, even though I [changed my mind later and did not do what] I [first] planned to do, [it was not because I did not have an important reason for changing my plans]. Surely you do not [really think] that I decide what I am going to do like people who do not know God do! [RHQ] I am [not like that]. I am not [a person who] says [to people], “Yes, [certainly I will do that],” and then [for no good reason changes his mind and says], “No, [I will not do it].”
18 Kamar dai yadda ba shakka Allah yake mai aminci, haka ma maganar da muka yi muku, ba “I” da kuma “A’a” ba ce.
Just as surely as God always does what he says [he will do, it is true that I have never said], “Yes, [I will do this]” when I [really meant] “No.”
19 Gama Ɗan Allah, Yesu Kiristi, wanda ni da Sila da Timoti muka yi muku wa’azinsa, ai, ba “I” da “A’a” ba ne, amma a cikin Kiristi, “I” ne kullum.
[I follow the example of] God’s Son, Jesus Christ. When I, along with Silas and Timothy, taught you [about Christ], we told you that he was not [someone who said that he] would do [something] and [then] did not [do it]. Jesus Christ never [said to anyone], “Yes, [I will do what you desire],” and [then did] not [do it].
20 Domin dukan alkawaran Allah cikarsu a gare shi suke, ta wurinsa ne kuma muke faɗar “Amin”, domin a ɗaukaka Allah.
[We(inc) know that is true], because everything that God promised to do [for his people], he has done completely by [sending] Christ [to save us]. That is why we say, “Yes, it is true! [God has done everything that he promised to do]!” And we praise him for that!
21 Allah ne fa yake sa mu da ku mu tsaya daram cikin Kiristi. Shi ne ya shafe mu,
Now it is only God himself who causes us [(exc)], as well as you, to keep on [believing] strongly in Christ. God is the one who chose us [(inc) to belong to him and to have a close relationship] with Christ.
22 ya buga mana hatiminsa a kan mu nasa ne, ya kuma sa mana Ruhunsa a cikin zukatanmu, domin yă tabbatar da abin da yake zuwa nan gaba.
He also sent his Holy Spirit into our [(inc)] lives to mark us as belonging to himself [MET]. Also, since he has sent his Spirit to live in us [(inc)], [he wants us to know by this that] he guarantees [MET] [to give us every other] ([blessing/good thing]) [that he has promised].
23 Labudda, Allah shi ne shaidata cewa don kada in ƙara muku wahala ne ya sa ban koma Korint ba.
So now [I will tell you why I changed my mind and did not visit you as I intended to do]: God himself knows [that what I am telling you is true]. The reason that I did not return to Corinth was so that I might not have to [speak to you severely about the wrong that you had done].
24 Ba nuna muku iko a kan bangaskiyarku muke yi ba, sai dai muna aiki tare da ku ne saboda farin cikinku, domin bisa ga bangaskiya ce kuke tsaye da ƙarfi.
It is not that Silas, Timothy and I want to boss you [and tell you that you must] believe only what we say. [Not at all]! On the contrary, we [(exc)] are working as partners [with you] in order to make you happy. [We do not try to force you to believe everything that we believe, because we are sure that you are continuing to] trust [the Lord Jesus Christ] and that you are remaining firmly committed to him.

< 2 Korintiyawa 1 >