< 2 Korintiyawa 6 >

1 A matsayinmu na abokan aikin Allah, muna roƙonku kada ku karɓi alherin Allah a banza.
And you also we, as God's fellow workers, entreat not to be found to have received His grace to no purpose.
2 Gama ya ce, “A lokacin samun alherina, na ji ka, a ranar samun ceto kuma, na taimake ka.” Ina gaya muku, yanzu ne lokacin samun alherin Allah, yanzu ne ranar samun ceto.
For He says, "At a time of welcome I have listened to you, and on a day of salvation I have succoured you." Now is the time of loving welcome! Now is the day of salvation!
3 Ba ma sa abin tuntuɓe wa kowa, domin kada hidimarmu ta zama abin zargi.
We endeavour to give people no cause for stumbling in anything, lest the work we are doing should fall into discredit.
4 A maimakon haka, duk abin da muke yi, muna yin shi ne don mu nuna cewa mu masu hidimar Allah ne. Muna yin haka cikin jimrewa, da shan wahala, da shan wuya, har da shan masifu.
On the contrary, as God's servants, we seek their full approval--by unwearied endurance, by afflictions, by distress, by helplessness;
5 Da shan dūka, da shan dauri, da yawan hargitsi, da yawan fama, da rashin barci, da kuma yunwa.
by floggings, by imprisonments; by facing riots, by toil, by sleepless watching, by hunger and thirst;
6 Da cikin tsarki, da fahimta, da haƙuri, da kirki, da cikin Ruhu Mai Tsarki, da cikin ƙauna mai gaskiya,
by purity of life, by knowledge, by patience, by kindness, by the Holy Spirit, by sincere love;
7 da cikin magana mai gaskiya, da kuma cikin ikon Allah. Muna riƙe da makaman adalci dama da hagu,
by the proclamation of the truth, by the power of God; by the weapons of righteousness, wielded in both hands;
8 ta wurin ɗaukaka da ƙasƙanci, da cikin ɓata suna, da kuma cikin yabo. Cikin faɗin gaskiya, an ɗauke mu masu ƙarya,
through honour and ignominy, through calumny and praise. We are looked upon as impostors and yet are true men;
9 mu sanannu ne, duk da haka an ɗauke mu kamar ba a san mu ba, muna mutuwa, duk da haka a raye muke, an ba mu horo, duk da haka ba a kashe mu ba,
as obscure persons, and yet are well known; as on the point of death, and yet, strange to tell, we live; as under God's discipline, and yet we are not deprived of life;
10 cikin baƙin ciki, duk da haka kullum cikin murna muke. Cikin matalauta, duk da haka muna azurtar da mutane da yawa. Ba mu da kome, alhali kuwa kome namu ne.
as sad, but we are always joyful; as poor, but we bestow wealth on many; as having nothing, and yet we securely possess all things.
11 Ya ku Korintiyawa, mun yi muku magana a sake, muka kuma saki zuciya da ku ƙwarai.
O Corinthians, our lips are unsealed to you: our heart is expanded.
12 Ba mu ƙi nuna muku ƙaunarmu ba, sai dai ku kuka ƙi nuna mana.
There is no narrowness in our love to you: the narrowness is in your own feelings.
13 A wannan zance kam, ina magana da ku kamar’ya’yana, ku ma ku saki zuciya da mu.
And in just requital--I speak as to my children--let your hearts expand also.
14 Kada ku haɗa kai da marasa bi. Gama me ya haɗa adalci da mugunta? Ko kuwa me ya haɗa haske da duhu?
Do not come into close association with unbelievers, like oxen yoked with asses. For what is there in common between righteousness and lawlessness? Or what partnership has light with darkness?
15 Wace daidaituwa ce tsakanin Kiristi da Iblis? Me ya haɗa mai bi da marar bi?
Where can harmony between Christ and Belial be found? Or what participation has a believer with an unbeliever?
16 Wane alkawari ne tsakanin haikalin Allah da na gumaka? Gama mu haikalin Allah mai rai ne. Kamar yadda Allah ya ce, “Zan zauna tare da su, in yi tafiya a cikinsu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena.”
And what compact has the Temple of God with idols? For we are the Temple of the ever-living God; as God has said, "I will dwell among them, and walk about among them; and will be their God, and it is they who shall be My people."
17 Saboda haka, “Sai ku fito daga cikinsu, ku keɓe kanku, in ji Ubangiji. Kada ku taɓa wani abu marar tsabta, zan kuma karɓe ku.”
Therefore, "'Come out from among them and separate yourselves,' says the Lord, 'and touch nothing impure; and I will receive you, and will be a Father to you,
18 Kuma, “Zan zama Uba a gare ku, ku kuma za ku zama’ya’yana, maza da mata, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
and you shall be My sons and daughters,' says the Lord the Ruler of all."

< 2 Korintiyawa 6 >