< 2 Korintiyawa 6 >

1 A matsayinmu na abokan aikin Allah, muna roƙonku kada ku karɓi alherin Allah a banza.
But, as a help to you, we exhort you not to receive the grace of God in vain.
2 Gama ya ce, “A lokacin samun alherina, na ji ka, a ranar samun ceto kuma, na taimake ka.” Ina gaya muku, yanzu ne lokacin samun alherin Allah, yanzu ne ranar samun ceto.
For he says: “In a favorable time, I heeded you; and on the day of salvation, I helped you.” Behold, now is the favorable time; behold, now is the day of salvation.
3 Ba ma sa abin tuntuɓe wa kowa, domin kada hidimarmu ta zama abin zargi.
May we never give offense to anyone, so that our ministry may not be disparaged.
4 A maimakon haka, duk abin da muke yi, muna yin shi ne don mu nuna cewa mu masu hidimar Allah ne. Muna yin haka cikin jimrewa, da shan wahala, da shan wuya, har da shan masifu.
But in all things, let us exhibit ourselves as ministers of God with great patience: through tribulation, difficulties, and distress;
5 Da shan dūka, da shan dauri, da yawan hargitsi, da yawan fama, da rashin barci, da kuma yunwa.
despite wounds, imprisonment, and rebellion; with hard work, vigilance, and fasting;
6 Da cikin tsarki, da fahimta, da haƙuri, da kirki, da cikin Ruhu Mai Tsarki, da cikin ƙauna mai gaskiya,
by chastity, knowledge, and longsuffering; in pleasantness, in the Holy Spirit, and in unfeigned charity;
7 da cikin magana mai gaskiya, da kuma cikin ikon Allah. Muna riƙe da makaman adalci dama da hagu,
with the Word of truth, with the power of God, and with the armor of justice to the right and to the left;
8 ta wurin ɗaukaka da ƙasƙanci, da cikin ɓata suna, da kuma cikin yabo. Cikin faɗin gaskiya, an ɗauke mu masu ƙarya,
through honor and dishonor, despite good reports and bad, whether seen as deceivers or truth-tellers, whether ignored or acknowledged;
9 mu sanannu ne, duk da haka an ɗauke mu kamar ba a san mu ba, muna mutuwa, duk da haka a raye muke, an ba mu horo, duk da haka ba a kashe mu ba,
as if dying and yet truly alive; as if chastised and yet not subdued;
10 cikin baƙin ciki, duk da haka kullum cikin murna muke. Cikin matalauta, duk da haka muna azurtar da mutane da yawa. Ba mu da kome, alhali kuwa kome namu ne.
as if sorrowful and yet always rejoicing; as if needy and yet enriching many; as if having nothing and possessing everything.
11 Ya ku Korintiyawa, mun yi muku magana a sake, muka kuma saki zuciya da ku ƙwarai.
Our mouth is open to you, O Corinthians; our heart is enlarged.
12 Ba mu ƙi nuna muku ƙaunarmu ba, sai dai ku kuka ƙi nuna mana.
You are not narrowed by us, but it is by your own inner selves that you are narrowed.
13 A wannan zance kam, ina magana da ku kamar’ya’yana, ku ma ku saki zuciya da mu.
But since we have the same recompense, (I am speaking as if to my own sons), you, too, should be enlarged.
14 Kada ku haɗa kai da marasa bi. Gama me ya haɗa adalci da mugunta? Ko kuwa me ya haɗa haske da duhu?
Do not choose to bear the yoke with unbelievers. For how can justice be a participant with iniquity? Or how can the fellowship of light be a participant with darkness?
15 Wace daidaituwa ce tsakanin Kiristi da Iblis? Me ya haɗa mai bi da marar bi?
And how can Christ join together with Belial? Or what part do the faithful have with the unfaithful?
16 Wane alkawari ne tsakanin haikalin Allah da na gumaka? Gama mu haikalin Allah mai rai ne. Kamar yadda Allah ya ce, “Zan zauna tare da su, in yi tafiya a cikinsu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena.”
And what consensus does the temple of God have with idols? For you are the temple of the living God, just as God says: “I will dwell with them, and I will walk among them. And I will be their God, and they shall be my people.
17 Saboda haka, “Sai ku fito daga cikinsu, ku keɓe kanku, in ji Ubangiji. Kada ku taɓa wani abu marar tsabta, zan kuma karɓe ku.”
Because of this, you must depart from their midst and be separate, says the Lord. And do not touch what is unclean.
18 Kuma, “Zan zama Uba a gare ku, ku kuma za ku zama’ya’yana, maza da mata, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Then I will accept you. And I will be a Father to you, and you shall be sons and daughters to me, says the Lord Almighty.”

< 2 Korintiyawa 6 >