< 2 Korintiyawa 5 >
1 Yanzu mun san cewa in an hallaka tentin duniyan nan da muke ciki, muna da wani gini daga Allah, madawwamin gida a sama, wanda ba da hannuwan mutum ne suka gina shi ba. (aiōnios )
PWE kitail asaer, impwal atail sappa a lao ola, kitail pan id imaneki im eu sang ren Kot, im eu me kaidin wiaui kida pa, pwe a me soutuk nanlang. (aiōnios )
2 Kafin nan muna nishi, da marmari a yi mana sutura da gidanmu na sama,
I me kitail kin sangesang o inong iong im sang nanlang en kalikau kitail da.
3 don sa’ad da aka yi mana sutura, ba za a same mu tsirara ba.
Pwe ma kitail likaudar, kitail solar pan kiliso.
4 Sa’ad da muke zaune a cikin jikin nan na duniya, nishi muke domin matsuwar da muke sha, ba domin muna so mu rabu da jikinmu na wannan duniya ba ne, sai dai don so muke yi a suturta mu da na Sama, domin mai rai ya shafe mai mutuwa.
Pwe ni atail deula impwal wet kitail kin sangesang o patau, pwe kitail sota men pure sang atail likau, a se men kadupaledi, pwe maur en katalala mela.
5 Allah ne ya yi mu domin wannan, ya kuma ba mu Ruhu a matsayin abin ajiya, yana kuma tabbatar da abin da zai zo nan gaba.
A me wia kin kitail ong mepukat, i Kot me pil kotiki ong kitail er komoan Ngen.
6 Saboda haka, kullum muna da tabbaci mun kuma san cewa, muddin muna a duniya cikin jikin nan, ana raba mu da Ubangiji.
Kitail ari insenemau ansau karos o asaer, ni atail kauson ki war, kitail kin doo wei sang Kaun.
7 Rayuwa bangaskiya muke, ba ta ganin ido ba.
Pwe kitail kin weweid ni poson a kaidin ni kilang.
8 Ina cewa muna da tabbaci, za mu fi so mu rabu da jikin nan, mu kuma kasance a sama tare da Ubangiji.
Ari so, kitail kin insenemau o inong iong muei sang war atail, ap mimi nan deu atail ren Kaun o.
9 Saboda haka, niyyarmu ita ce, mu gamshe shi, ko muna a duniya cikin jikin nan, ko ba mu nan.
Nan i me kitail kin nantiong kaperen i, ma ni deu’tail de ni at doo wei sang.
10 Gama dole dukanmu mu bayyana a gaban kujerar shari’ar Kiristi, domin kowannenmu yă karɓi ladan aikin da ya yi a wannan jiki, ko mai kyau ne ko marar kyau.
Pwe kitail karos pan sansal mon mol en kadeik en Kristus, pwe amen amen en ale pwain en a wiawia arain a maur ni pali war, ma me mau de me sued.
11 To, da yake mun san ko mene tsoron Ubangiji yake, muna ƙoƙari mu rinjaye mutane. Yadda muke kuwa, yana sane a sarari ga Allah, ina kuma fata yana nan a sarari a lamirinku.
Kit asaer, me sen masak Kaun o, i me se kin kanekanai ong at dodok ong aramas akan, ap kin sansal ong Kot. A i pil kaporoporeki me se pil sansal ong nan insen omail.
12 Ba ƙoƙari muke mu yabe kanmu a gare ku ba ne, sai dai muna ba ku damar yin taƙama da mu ne, don ku sami amsar da za ku ba wa waɗanda suke taƙama da abin da ake gani ne, a maimakon abin da yake cikin zuciya.
Pwe kit sota sapal suaiki pein kit ong komail, a se pang ong komail, en kaping pat, pwe peikite pamail en mia ong irail, me kin suaiki mas arail, a so mongiong arail.
13 In hankalinmu a taɓe yake, ai, saboda Allah ne, in kuwa cikin hankalinmu muke, ai, saboda ku ne.
Pwe ni at mi likin war at, a kin wiaui ong Kot, a ma so, se kin dodok ong komail.
14 Ƙaunar Kiristi a gare mu, ita take mallakarmu, saboda haka mun tabbata, da yake wani ya mutu saboda dukan mutane, ashe kuwa, mutuwarsu ce dukansu.
Pwe iduen limpok en Kristus kangong kin kit, pwe se kasauiadar, me amen mata kila karos, i me irail karos mekilar.
15 Ya kuwa mutu ne saboda dukan mutane, domin kada waɗanda suke rayuwa kada su yi zaman ganin dama a nan gaba, sai dai su yi zaman wannan da ya mutu saboda su, aka kuma tashe shi saboda su.
A i mata kilang karos, pwe irail me memaur, der memaur ong pein irail, a ong i, me mata kin irail lar o me kaiasadar.
16 Saboda haka, daga yanzu zuwa nan gaba, ba mu ƙara ɗaukan wani mutum bisa ga ganin duniya ba. Ko da yake a dā, mun ɗauki Kiristi haka, amma yanzu mun daina yin haka.
I me se solar asa amen ni pali uduk. Ei, mas o se asaer Kristus ni pali uduk eta, a met se solar asa i due.
17 Saboda haka, duk wanda yake cikin Kiristi, sabuwar halitta ce, tsohon al’amari ya shuɗe, sabon ya zo!
Ari ma amen mi ren Kristus, nan a wilikapadar; men mas momelar, kilang, karos wilikapada.
18 Duk wannan kuwa daga Allah ne, wanda ya sulhunta mu da kansa ta wurin Kiristi, ya kuma ba mu hidimar sulhu,
A meakan karos sang ren Kot, me kotin kalolamaui ong pein i kitail ki Iesus Kristus, me kotiki ong kit at koa dodok, duen padak en kalolmau.
19 wato, Allah ya sulhunta duniya zuwa kansa ta wurin Kiristi, ba ya lissafta zunuban mutane a kansu. Ya kuma danƙa mana saƙon sulhu.
Pwe Kot kotikot ren Kristus o kotin kalokalolamau ong pein i sappa, o solar kapokon ong irail dip arail akan, o kotiki ong kitail masan en kalolamau.
20 Saboda haka, mu jakadu ne na Kiristi, sai ka ce Allah kansa yake magana ta wurinmu. Muna roƙonku a madadin Kiristi. Ku sulhuntu da Allah.
Ari, kit men en kadar en Kristus, pwe Kot kin panaui ki kit. Kit wiliandi Kristus ap poekipoeki kin komail: Komail kalolamau pein komail ong Kot!
21 Shi da bai san zunubi ba, Allah ya mai da shi kamar hadayar zunubi saboda mu, domin mu sami adalcin Allah ta wurinsa.
Pwe Kot kotin kapokonki ong, me so dip a, dip atail, pwe kitail en pung kila pa ren Kot.