< 2 Korintiyawa 5 >
1 Yanzu mun san cewa in an hallaka tentin duniyan nan da muke ciki, muna da wani gini daga Allah, madawwamin gida a sama, wanda ba da hannuwan mutum ne suka gina shi ba. (aiōnios )
Mana twenga tuvimaa kuwera shisasa ashi shatulikala pasipanu, ndo nshimba zyetu, pazitupulwa, Mlungu hakatupanani numba ya mashaka goseri kumpindi, numba ya mashaka goseri yayinyawilwa ndiri kwa mawoku ga wantu. (aiōnios )
2 Kafin nan muna nishi, da marmari a yi mana sutura da gidanmu na sama,
Na vinu, twankulolera kwa mata nentu kupananwa nshimba ya kumpindi kwa Mlungu.
3 don sa’ad da aka yi mana sutura, ba za a same mu tsirara ba.
Toziya patupananwa nshimba zya kumpindi kwa Mlungu, hapeni tuwoneki twahera nshimba.
4 Sa’ad da muke zaune a cikin jikin nan na duniya, nishi muke domin matsuwar da muke sha, ba domin muna so mu rabu da jikinmu na wannan duniya ba ne, sai dai don so muke yi a suturta mu da na Sama, domin mai rai ya shafe mai mutuwa.
Twenga patuwera twankali twankulikala mushisasa ashi sha pasipanu, twankusapira na kufintirwa, tufira ndiri kuyivula nshimba ayi ya kuhowa, kumbiti tufira kuvalisiwa nshimba ilii yayihowa ndiri, su shilii shashihowa shigalambulwi na shilii shana ukomu.
5 Allah ne ya yi mu domin wannan, ya kuma ba mu Ruhu a matsayin abin ajiya, yana kuma tabbatar da abin da zai zo nan gaba.
Mlungu mweni katutandiriti shitwatira ashi, nayomberi katupanana Rohu gwakuwi kaweri ulanguziwu kwa goseri gakatutuliriti.
6 Saboda haka, kullum muna da tabbaci mun kuma san cewa, muddin muna a duniya cikin jikin nan, ana raba mu da Ubangiji.
Su, mashaka goseri tugangamala. Tuvimana handa kulikala munshimba ayi, twakutali mnumba yatwenga na Mtuwa.
7 Rayuwa bangaskiya muke, ba ta ganin ido ba.
Toziya tulikala ndiri kwa kuwona, kumbiti tulikala kwa njimiru.
8 Ina cewa muna da tabbaci, za mu fi so mu rabu da jikin nan, mu kuma kasance a sama tare da Ubangiji.
Twenga tugangamala na metufiri tulikali kutali na nshimba azi na tulikali pamuhera na Mtuwa.
9 Saboda haka, niyyarmu ita ce, mu gamshe shi, ko muna a duniya cikin jikin nan, ko ba mu nan.
Kumbiti shitwatila shikulu nentu, tufira kumfiriziya Mtuwa patulikala mnumba ya pasipanu ama mnumba ya kumpindi kwa Mlungu.
10 Gama dole dukanmu mu bayyana a gaban kujerar shari’ar Kiristi, domin kowannenmu yă karɓi ladan aikin da ya yi a wannan jiki, ko mai kyau ne ko marar kyau.
Toziya twenga twoseri hatugoloki kulongolu kwa Kristu na yomberi hakatutozi. Kila muntu hakanki shilii shakafiriziwitwi kwanka kwa galii gakatenditi pasipanu, gaweri gaherepa ama madoda.
11 To, da yake mun san ko mene tsoron Ubangiji yake, muna ƙoƙari mu rinjaye mutane. Yadda muke kuwa, yana sane a sarari ga Allah, ina kuma fata yana nan a sarari a lamirinku.
Toziya tuvimana nentu ntambu ya kumtira Mtuwa, su tujera kuwanika wantu wamonga. Mlungu katumana hweri na naneni nulitumbira mwenga mmana hweri myoyu yatwenga.
12 Ba ƙoƙari muke mu yabe kanmu a gare ku ba ne, sai dai muna ba ku damar yin taƙama da mu ne, don ku sami amsar da za ku ba wa waɗanda suke taƙama da abin da ake gani ne, a maimakon abin da yake cikin zuciya.
Tufira ndiri kayi kulijuma twaweni kulongolu kwa mwenga. Kumbiti tuwapanana toziya ziherepa zyetu zya kulitumbira, su mwezi kawawankula walii yawalitumbira wantu yawawoneka kuliku ntambu yawawera mumoyu mwawu.
13 In hankalinmu a taɓe yake, ai, saboda Allah ne, in kuwa cikin hankalinmu muke, ai, saboda ku ne.
Payiwera tuwoneka kuwera twanalukwali, twanalukwali kwajili ya Mlungu na mahala getu gaherepa, ayi ndo kwa mota yamwenga.
14 Ƙaunar Kiristi a gare mu, ita take mallakarmu, saboda haka mun tabbata, da yake wani ya mutu saboda dukan mutane, ashe kuwa, mutuwarsu ce dukansu.
Twenga tulonguziwa na ufiru wa Kristu, vinu tuwera tuvimana handa muntu yumu hera kahowiti kwajili ya wantu woseri, su twawoseri tuhowa pamuhera na yomberi.
15 Ya kuwa mutu ne saboda dukan mutane, domin kada waɗanda suke rayuwa kada su yi zaman ganin dama a nan gaba, sai dai su yi zaman wannan da ya mutu saboda su, aka kuma tashe shi saboda su.
Kahowiti kwajili ya woseri, su yawalikala walikali ndiri kwa toziya yawu weni, kumbiti kwajili yakuwi yomberi yakahowiti na kazyukisiyitwi kwajili yawu.
16 Saboda haka, daga yanzu zuwa nan gaba, ba mu ƙara ɗaukan wani mutum bisa ga ganin duniya ba. Ko da yake a dā, mun ɗauki Kiristi haka, amma yanzu mun daina yin haka.
Su, kwanjira vinu, twenga tumwalanga ndiri muntu yoseri shiuntu, ata handa tumwalangiti Kristu shiuntu, kumbiti vinu hapeni tutenda hangu kayi.
17 Saboda haka, duk wanda yake cikin Kiristi, sabuwar halitta ce, tsohon al’amari ya shuɗe, sabon ya zo!
Muntu yoseri pakalikolerana pamuhera na Kristu, muntu ayu kawera shiumbi sha syayi, ga makashu gapita, gawera ga syayi.
18 Duk wannan kuwa daga Allah ne, wanda ya sulhunta mu da kansa ta wurin Kiristi, ya kuma ba mu hidimar sulhu,
Goseri aga galawa kwa Mlungu, yakatugalambula twenga kulawa muungondu na kututenda tuweri waganja wakuwi kupitira Kristu na katupananiti lihengu kukolaniziya mawoku.
19 wato, Allah ya sulhunta duniya zuwa kansa ta wurin Kiristi, ba ya lissafta zunuban mutane a kansu. Ya kuma danƙa mana saƙon sulhu.
Mlungu kaweriti mngati mwa Kristu, kawatenda wantu waweri waganja wakuwi kupitira Kristu. Yomberi kawawalangiriti ndiri vidoda vyawu na yomberi katupananiti ujumbi wa kukolaniziya mawoku.
20 Saboda haka, mu jakadu ne na Kiristi, sai ka ce Allah kansa yake magana ta wurinmu. Muna roƙonku a madadin Kiristi. Ku sulhuntu da Allah.
Su twenga tutakula ntambu yakatakula Kristu yatutakula nayomberi Mlungu katutumiya twenga kuwaluwani. Tuwaluwani mwenga kwa ajili ya Kristu, mkolaniziwi mawoku na Mlungu.
21 Shi da bai san zunubi ba, Allah ya mai da shi kamar hadayar zunubi saboda mu, domin mu sami adalcin Allah ta wurinsa.
Kristu kaweriti ndiri na vidoda, kumbiti Mlungu kamtenda kapapi vidoda vyetu, su kwa kulikolerana pamuhera nayomberi, twenga tuweri wantu waheri wa Mlungu.