< 2 Korintiyawa 5 >

1 Yanzu mun san cewa in an hallaka tentin duniyan nan da muke ciki, muna da wani gini daga Allah, madawwamin gida a sama, wanda ba da hannuwan mutum ne suka gina shi ba. (aiōnios g166)
Tudjuk, hogyha ez a mi földi sátorunk összeomlik, van Istentől készített hajlékunk, nem kézzel csinált, hanem örökkévaló házunk a mennyben. (aiōnios g166)
2 Kafin nan muna nishi, da marmari a yi mana sutura da gidanmu na sama,
Azért is sóhajtozunk ebben, mert mennyei hajlékunkat szeretnénk erre felölteni,
3 don sa’ad da aka yi mana sutura, ba za a same mu tsirara ba.
hogy ezt felöltve, mezíteleneknek ne találtassunk.
4 Sa’ad da muke zaune a cikin jikin nan na duniya, nishi muke domin matsuwar da muke sha, ba domin muna so mu rabu da jikinmu na wannan duniya ba ne, sai dai don so muke yi a suturta mu da na Sama, domin mai rai ya shafe mai mutuwa.
Mert mi is, akik e sátorban vagyunk, megterhelten sóhajtozunk, mert nem kívánunk levetkőztetni, hanem felöltöztetni, hogy ami halandó, elnyelje azt az élet.
5 Allah ne ya yi mu domin wannan, ya kuma ba mu Ruhu a matsayin abin ajiya, yana kuma tabbatar da abin da zai zo nan gaba.
Aki pedig minket erre felkészített, az Isten az, aki a Lélek zálogát is adta nekünk.
6 Saboda haka, kullum muna da tabbaci mun kuma san cewa, muddin muna a duniya cikin jikin nan, ana raba mu da Ubangiji.
Ezért mindenkor bizakodunk, és tudjuk, hogy amíg e testben lakunk, távol vagyunk az Úrtól,
7 Rayuwa bangaskiya muke, ba ta ganin ido ba.
mert hitben járunk, nem látásban.
8 Ina cewa muna da tabbaci, za mu fi so mu rabu da jikin nan, mu kuma kasance a sama tare da Ubangiji.
De bizakodunk, és inkább szeretnénk kiköltözni e testből és elköltözni az Úrhoz.
9 Saboda haka, niyyarmu ita ce, mu gamshe shi, ko muna a duniya cikin jikin nan, ko ba mu nan.
Ezért arra igyekszünk, hogy akár itt lakunk, akár elköltözünk, neki kedvesek legyünk.
10 Gama dole dukanmu mu bayyana a gaban kujerar shari’ar Kiristi, domin kowannenmu yă karɓi ladan aikin da ya yi a wannan jiki, ko mai kyau ne ko marar kyau.
Mert nekünk mindnyájunknak meg kell jelennünk a Krisztus ítélőszéke előtt, hogy ki-ki elvegye jutalmát annak, amit e testben cselekedett, vagy jót, vagy gonoszt.
11 To, da yake mun san ko mene tsoron Ubangiji yake, muna ƙoƙari mu rinjaye mutane. Yadda muke kuwa, yana sane a sarari ga Allah, ina kuma fata yana nan a sarari a lamirinku.
Ismerve tehát az Úrnak félelmét, embereket térítünk. Isten előtt pedig nyíltan állunk és remélem, hogy a ti lelkiismeretetek előtt is nyíltan állunk.
12 Ba ƙoƙari muke mu yabe kanmu a gare ku ba ne, sai dai muna ba ku damar yin taƙama da mu ne, don ku sami amsar da za ku ba wa waɗanda suke taƙama da abin da ake gani ne, a maimakon abin da yake cikin zuciya.
Mert nem önmagunkat ajánljuk ismét, hanem alkalmat adunk nektek a velünk való dicsekedésre, hogy legyen mit felelnetek a színből és nem szívből dicsekedőknek.
13 In hankalinmu a taɓe yake, ai, saboda Allah ne, in kuwa cikin hankalinmu muke, ai, saboda ku ne.
Ha révületben vagyunk, Istenért vagyunk, ha pedig megfontoltak vagyunk, értetek van.
14 Ƙaunar Kiristi a gare mu, ita take mallakarmu, saboda haka mun tabbata, da yake wani ya mutu saboda dukan mutane, ashe kuwa, mutuwarsu ce dukansu.
Mert Krisztus szeretete szorongat minket, mivel úgy ítéljük,
15 Ya kuwa mutu ne saboda dukan mutane, domin kada waɗanda suke rayuwa kada su yi zaman ganin dama a nan gaba, sai dai su yi zaman wannan da ya mutu saboda su, aka kuma tashe shi saboda su.
hogy ha egy meghalt mindenkiért, azok tehát mind meghaltak, és azért halt meg mindenkiért, hogy akik élnek, ezután ne maguknak éljenek, hanem annak, aki értük meghalt és feltámadt.
16 Saboda haka, daga yanzu zuwa nan gaba, ba mu ƙara ɗaukan wani mutum bisa ga ganin duniya ba. Ko da yake a dā, mun ɗauki Kiristi haka, amma yanzu mun daina yin haka.
Ezért mi ezentúl senkit sem ismerünk test szerint. Ha Krisztust ismertük is test szerint, de többé már nem így ismerjük.
17 Saboda haka, duk wanda yake cikin Kiristi, sabuwar halitta ce, tsohon al’amari ya shuɗe, sabon ya zo!
Ezért, ha valaki Krisztusban van, új teremtés az, a régiek elmúltak, és íme ujjá lett minden.
18 Duk wannan kuwa daga Allah ne, wanda ya sulhunta mu da kansa ta wurin Kiristi, ya kuma ba mu hidimar sulhu,
Mindez pedig Istentől van, aki megbékéltetett minket magával Jézus Krisztus által és nekünk adta a békéltetés szolgálatát.
19 wato, Allah ya sulhunta duniya zuwa kansa ta wurin Kiristi, ba ya lissafta zunuban mutane a kansu. Ya kuma danƙa mana saƙon sulhu.
Mivel Isten volt az, aki Krisztusban magával megbékéltette a világot, nem tulajdonítva nekik az ő bűneiket és ránk bízta a békéltetés igéjét,
20 Saboda haka, mu jakadu ne na Kiristi, sai ka ce Allah kansa yake magana ta wurinmu. Muna roƙonku a madadin Kiristi. Ku sulhuntu da Allah.
Krisztusért járva követségben, mintha Isten kérne miáltalunk, Krisztusért kérünk, béküljetek meg az Istennel!
21 Shi da bai san zunubi ba, Allah ya mai da shi kamar hadayar zunubi saboda mu, domin mu sami adalcin Allah ta wurinsa.
Mert azt, aki bűnt nem ismert, bűnné tette értünk, hogy mi Isten igazsága legyünk őbenne.

< 2 Korintiyawa 5 >