< 2 Korintiyawa 5 >

1 Yanzu mun san cewa in an hallaka tentin duniyan nan da muke ciki, muna da wani gini daga Allah, madawwamin gida a sama, wanda ba da hannuwan mutum ne suka gina shi ba. (aiōnios g166)
For we knowe that if our earthly house of this tabernacle be destroyed, we haue a building giuen of God, that is, an house not made with handes, but eternall in the heauens. (aiōnios g166)
2 Kafin nan muna nishi, da marmari a yi mana sutura da gidanmu na sama,
For therefore we sighe, desiring to be clothed with our house, which is from heauen.
3 don sa’ad da aka yi mana sutura, ba za a same mu tsirara ba.
Because that if we be clothed, we shall not be found naked.
4 Sa’ad da muke zaune a cikin jikin nan na duniya, nishi muke domin matsuwar da muke sha, ba domin muna so mu rabu da jikinmu na wannan duniya ba ne, sai dai don so muke yi a suturta mu da na Sama, domin mai rai ya shafe mai mutuwa.
For in deede we that are in this tabernacle, sigh and are burdened, because we would not be vnclothed, but would be clothed vpon, that mortalitie might be swalowed vp of life.
5 Allah ne ya yi mu domin wannan, ya kuma ba mu Ruhu a matsayin abin ajiya, yana kuma tabbatar da abin da zai zo nan gaba.
And he that hath created vs for this thing, is God, who also hath giuen vnto vs the earnest of the Spirit.
6 Saboda haka, kullum muna da tabbaci mun kuma san cewa, muddin muna a duniya cikin jikin nan, ana raba mu da Ubangiji.
Therefore we are alway bolde, though we knowe that whiles we are at home in the bodie, we are absent from the Lord.
7 Rayuwa bangaskiya muke, ba ta ganin ido ba.
(For we walke by faith, and not by sight.)
8 Ina cewa muna da tabbaci, za mu fi so mu rabu da jikin nan, mu kuma kasance a sama tare da Ubangiji.
Neuerthelesse, we are bolde, and loue rather to remoue out of the body, and to dwell with the Lord.
9 Saboda haka, niyyarmu ita ce, mu gamshe shi, ko muna a duniya cikin jikin nan, ko ba mu nan.
Wherefore also we couet, that both dwelling at home, and remouing from home, we may be acceptable to him.
10 Gama dole dukanmu mu bayyana a gaban kujerar shari’ar Kiristi, domin kowannenmu yă karɓi ladan aikin da ya yi a wannan jiki, ko mai kyau ne ko marar kyau.
For we must all appeare before the iudgement seate of Christ, that euery man may receiue the things which are done in his body, according to that he hath done, whether it be good or euill.
11 To, da yake mun san ko mene tsoron Ubangiji yake, muna ƙoƙari mu rinjaye mutane. Yadda muke kuwa, yana sane a sarari ga Allah, ina kuma fata yana nan a sarari a lamirinku.
Knowing therefore that terrour of the Lord, we persuade men, and we are made manifest vnto God, and I trust also that we are made manifest in your consciences.
12 Ba ƙoƙari muke mu yabe kanmu a gare ku ba ne, sai dai muna ba ku damar yin taƙama da mu ne, don ku sami amsar da za ku ba wa waɗanda suke taƙama da abin da ake gani ne, a maimakon abin da yake cikin zuciya.
For we prayse not our selues againe vnto you, but giue you an occasion to reioyce of vs, that ye may haue to answere against them, which reioyce in the face, and not in the heart.
13 In hankalinmu a taɓe yake, ai, saboda Allah ne, in kuwa cikin hankalinmu muke, ai, saboda ku ne.
For whether we be out of our wit, we are it to God: or whether we be in our right minde, we are it vnto you.
14 Ƙaunar Kiristi a gare mu, ita take mallakarmu, saboda haka mun tabbata, da yake wani ya mutu saboda dukan mutane, ashe kuwa, mutuwarsu ce dukansu.
For that loue of Christ constraineth vs,
15 Ya kuwa mutu ne saboda dukan mutane, domin kada waɗanda suke rayuwa kada su yi zaman ganin dama a nan gaba, sai dai su yi zaman wannan da ya mutu saboda su, aka kuma tashe shi saboda su.
Because we thus iudge, that if one be dead for all, then were all dead, and he died for all, that they which liue, shoulde not henceforth liue vnto themselues, but vnto him which died for them, and rose againe.
16 Saboda haka, daga yanzu zuwa nan gaba, ba mu ƙara ɗaukan wani mutum bisa ga ganin duniya ba. Ko da yake a dā, mun ɗauki Kiristi haka, amma yanzu mun daina yin haka.
Wherefore, henceforth know we no man after the flesh, yea though wee had knowen Christ after the flesh, yet nowe henceforth know we him no more.
17 Saboda haka, duk wanda yake cikin Kiristi, sabuwar halitta ce, tsohon al’amari ya shuɗe, sabon ya zo!
Therefore if any man be in Christ, let him be a newe creature. Olde things are passed away: beholde, all things are become newe.
18 Duk wannan kuwa daga Allah ne, wanda ya sulhunta mu da kansa ta wurin Kiristi, ya kuma ba mu hidimar sulhu,
And all things are of God, which hath reconciled vs vnto himselfe by Iesus Christ, and hath giuen vnto vs the ministerie of reconciliation.
19 wato, Allah ya sulhunta duniya zuwa kansa ta wurin Kiristi, ba ya lissafta zunuban mutane a kansu. Ya kuma danƙa mana saƙon sulhu.
For God was in Christ, and reconciled the world to himselfe, not imputing their sinnes vnto them, and hath committed to vs the word of reconciliation.
20 Saboda haka, mu jakadu ne na Kiristi, sai ka ce Allah kansa yake magana ta wurinmu. Muna roƙonku a madadin Kiristi. Ku sulhuntu da Allah.
Now then are we ambassadours for Christ: as though God did beseeche you through vs, we pray you in Christes steade, that ye be reconciled to God.
21 Shi da bai san zunubi ba, Allah ya mai da shi kamar hadayar zunubi saboda mu, domin mu sami adalcin Allah ta wurinsa.
For he hath made him to be sinne for vs, which knewe no sinne, that we should be made the righteousnesse of God in him.

< 2 Korintiyawa 5 >