< 2 Korintiyawa 4 >

1 Saboda haka, da yake ta wurin jinƙan Allah ne muke da wannan hidima, ba za mu fid da zuciya ba.
Linu, mukuti twina ili ikolo, ni sina mutu va tambwiri chisemo, katuzwafi.
2 Ba ruwanmu da ɓoye-ɓoye na munafuncin da suke abubuwan kunya. Ba ruwanmu da ruɗu, ko yin ƙarya da kalmar Allah. Sai dai muna faɗin gaskiya a fili. Ta haka ne kowa zai yi shaidar gaskiyarmu a gaban Allah cikin zuciyarsa.
Ni hakwina vulyo, tuve zivahazi inzila ziswavisisa ni zili wungwile. Katuhali cha ku chengelela, tuwonda inzwi lye Ireeza hande. Chaku zimanina initi, tulileta havusu bwa zumwi ni zumwi cha kuya che zwalo lyakwe mu menso e Ireeza.
3 Ko da bishararmu a rufe take, tana a rufe ne ga waɗanda suke hallaka.
Haiva i evangeli yetu i umbitwe, i umbitwe feela kwabo basinyeha.
4 Allahn zamanin nan ya makanta hankulan marasa ba da gaskiya, yadda har ba za su iya ganin hasken bishara ta ɗaukakar Kiristi ba, wanda yake kamannin Allah. (aiōn g165)
Imi kuvali, mulimu we inu inkanda ava hofuhazi kusa zumina kwa mihupulo yavo. Chelo ivaka, kava woli kuvona mumuni wa linzwi we kanya ya Kresite, iye chiswaniso che Ireeza. (aiōn g165)
5 Gama ba wa’azin kanmu muke yi ba, sai dai na Yesu Kiristi, a kan shi ne Ubangiji, mu kuma bayinku saboda Yesu.
Katuli zivahazi iswe tuvene, kono Kresite Jesu neli Simwine, mi iswe tuvahikana venu kuchitila Jesu.
6 Domin shi Allah wanda ya ce, “Bari haske yă haskaka daga duhu,” ya sa haskensa ya haskaka a cikin zukatanmu, don yă ba mu hasken sanin ɗaukakar Allah a fuskar Kiristi.
Mukuti Ireeza nja va wambi kuti, “mumuni kauvenye mwi fifi.” Ava veñyisi mwi inkulo zetu, kuha iseri lyo kwiziva ikanya ye Ireeza mukuva kwa Jesu Kresite.
7 Amma muna da wannan dukiya a cikin tulunan yumɓu, don a nuna wannan mafificin ikon nan daga Allah ne, ba daga gare mu ba.
Kono twina ichi chifumu tuhamwe twe rongo, nji kuta kuti ziho zonse kuhitiliza njiza Ireza mi isinyi zetu.
8 A matse muke a kowane gefe, sai dai ba a gurgunta mu ba. An rikitar da mu, amma ba mu fid da zuciya ba.
Tuwina muvukavo mwinkalulo zonse, kono katu pwachuki, katwizi cha ku panga kono katwizuli kuswava.
9 An tsananta mana, amma ba a yashe mu ba, an fyaɗe mu da ƙasa, amma ba a hallaka mu ba.
Tunyandiswa kono katukanwa. Tu wisikizwa hansi kono katusinyehi.
10 Kullum muna ɗauke da mutuwar Yesu a jikinmu, domin ran Yesu yă bayyana a jikinmu.
Tuhindite ifu lya Jesu mu mi viri yetu inako yonse, jo kuti vuhalo bwa Jesu vuvoneke mumivili yetu.
11 Muddin muna a raye, kullum zaman mutuwa muke yi saboda Yesu, don a bayyana ran Yesu ta wurin jikin nan namu mai mutuwa.
Iswe tuhala tuhindite mumivili yetu inako yonse ifu lya Jesu, njokuti vuhalo bwa Jesu vuvoniswe mumivili yetu ya vuntu.
12 Ta haka, mutuwa tana aiki a cikinmu, ku kuwa rai a cikinku.
Njokuti ifu likwete kuveleka mwetu, kono vuhalo vukwete kuveleka mwenu.
13 A rubuce yake cewa, “Na gaskata; saboda haka na yi magana.” Da wannan ruhun bangaskiya ne mu ma muka gaskata, saboda haka muke magana.
Kono twina luhulo luswana lwe ntumelo kakuya ka chiva ñoletwe: “Niva zumini, mi linu niva wambi.” Naswe tuzumina mi hape tuwamba.
14 Domin mun san cewa shi da ya tā da Ubangiji Yesu daga matattu, zai tashe mu mu ma tare da Kiristi, yă kuma miƙa mu a gabansa tare da ku.
Twizi kuti iyemwine yava vusi simwene Jesu, katu vuse naswe ni Jesu. Twizi kuti kaatu hinde nanwe kuya mwena iye.
15 Duk wannan fa don amfaninku ne, domin alherin nan da yake bazuwa zuwa ga mutane masu yawa, yă zama dalilin godiya mai yawa ga ɗaukakar Allah.
Zintu zonse zichitilwe inwe kuchila kuti, sina chisemo hachi hasene kuvantu vangi. Kutambika vuitumelo kwi njihe kwi kanya ya Ireeza.
16 Saboda haka, ba mu fid da zuciya ba. Ko da yake a waje, jikinmu mai mutuwa yana lalacewa, amma can ciki, ana sabunta mu kowace rana.
Linu katuzwafi. Nihakuva vulyo, hanze tukwete ku sinyeha, mukati tukwete kuvumbwa chihya izuva ni zuva.
17 Don wannan’yar wahalar tamu mai saurin wucewa, ita take tanadar mana madawwamiyar ɗaukaka mai yawa, fiye da kwatanci. (aiōnios g166)
Mweyi inako zana, manyandozana anu a kwete atuvakanyeza kulema kwe kanya kulikanyezwa kusamani. (aiōnios g166)
18 Domin ba abubuwan da ido yake gani ne muke dubawa ba, sai dai marasa ganuwa. Gama abubuwan da ake gani masu saurin wucewa ne, marasa ganuwa kuwa, madawwama ne. (aiōnios g166)
Katu lolete zintu zivoneka, kono zintu zisa voneki. zintu zivoneka zenakozana, kono zintu zisa voneki za kuya kusamani. (aiōnios g166)

< 2 Korintiyawa 4 >