< 2 Korintiyawa 3 >
1 Yabon kanmu ne kuma muka fara yi? Ko kuwa muna bukatar wasiƙun yabo ne zuwa gare ku, ko daga gare ku, kamar yadda waɗansu suke yi?
১ৱযং কিম্ আত্মপ্ৰশংসনং পুনৰাৰভামহে? যুষ্মান্ প্ৰতি যুষ্মত্তো ৱা পৰেষাং কেষাঞ্চিদ্ ইৱাস্মাকমপি কিং প্ৰশংসাপত্ৰেষু প্ৰযোজনম্ আস্তে?
2 Ai, ku kanku ku ne wasiƙarmu, wadda aka rubuta a zukatanku, domin kowa yă santa, yă kuma karanta ta.
২যূযমেৱাস্মাকং প্ৰশংসাপত্ৰং তচ্চাস্মাকম্ অন্তঃকৰণেষু লিখিতং সৰ্ৱ্ৱমানৱৈশ্চ জ্ঞেযং পঠনীযঞ্চ|
3 Kun nuna cewa ku wasiƙa ce daga Kiristi, sakamakon hidimarmu, ba wadda aka rubuta da inki ba, sai dai da Ruhun Allah mai rai. Ba kuma a kan allunan dutse ba, sai dai a kan allunan zukatan mutane.
৩যতো ঽস্মাভিঃ সেৱিতং খ্ৰীষ্টস্য পত্ৰং যূযপেৱ, তচ্চ ন মস্যা কিন্ত্ৱমৰস্যেশ্ৱৰস্যাত্মনা লিখিতং পাষাণপত্ৰেষু তন্নহি কিন্তু ক্ৰৱ্যমযেষু হৃৎপত্ৰেষু লিখিতমিতি সুস্পষ্টং|
4 Amincewa kamar wannan shi ne namu ta wurin Kiristi a gaban Allah.
৪খ্ৰীষ্টেনেশ্ৱৰং প্ৰত্যস্মাকম্ ঈদৃশো দৃঢৱিশ্ৱাসো ৱিদ্যতে;
5 Ba mu da wani abin da za mu nuna cewa da iyawarmu ne muke aikin nan. Iyawarmu daga wurin Allah ne.
৫ৱযং নিজগুণেন কিমপি কল্পযিতুং সমৰ্থা ইতি নহি কিন্ত্ৱীশ্ৱৰাদস্মাকং সামৰ্থ্যং জাযতে|
6 Shi ya sa muka gwaninta a matsayinmu na masu hidimar sabon alkawari ba ta rubutacciyar Dokar ba, amma ta Ruhu; don Dokar, kisa take yi, Ruhu kuwa yana ba da rai.
৬তেন ৱযং নূতননিযমস্যাৰ্থতো ঽক্ষৰসংস্থানস্য তন্নহি কিন্ত্ৱাত্মন এৱ সেৱনসামৰ্থ্যং প্ৰাপ্তাঃ| অক্ষৰসংস্থানং মৃত্যুজনকং কিন্ত্ৱাত্মা জীৱনদাযকঃ|
7 To, in hidimar da ta kawo mutuwa, wadda an rubuta a kan allon dutse, ta zo da ɗaukaka har Isra’ilawa suka kāsa duban fuskar Musa saboda tsananin haskenta, ko da yake mai shuɗewa ce,
৭অক্ষৰৈ ৰ্ৱিলিখিতপাষাণৰূপিণী যা মৃত্যোঃ সেৱা সা যদীদৃক্ তেজস্ৱিনী জাতা যত্তস্যাচিৰস্থাযিনস্তেজসঃ কাৰণাৎ মূসসো মুখম্ ইস্ৰাযেলীযলোকৈঃ সংদ্ৰষ্টুং নাশক্যত,
8 ashe, hidimar Ruhu ba za tă fi wannan ɗaukaka ba?
৮তৰ্হ্যাত্মনঃ সেৱা কিং ততোঽপি বহুতেজস্ৱিনী ন ভৱেৎ?
9 In hidimar da take jawo wa mutane hukunci tana da ɗaukaka haka, to, lalle, hidimar da take kawo adalci za tă fi ta ɗaukaka nesa!
৯দণ্ডজনিকা সেৱা যদি তেজোযুক্তা ভৱেৎ তৰ্হি পুণ্যজনিকা সেৱা ততোঽধিকং বহুতেজোযুক্তা ভৱিষ্যতি|
10 Gama abin da dā take da ɗaukaka, ba ta da ɗaukaka a yanzu, in aka kwatantata da mafificiyar ɗaukaka ta yanzu.
১০উভযোস্তুলনাযাং কৃতাযাম্ একস্যাস্তেজো দ্ৱিতীযাযাঃ প্ৰখৰতৰেণ তেজসা হীনতেজো ভৱতি|
11 In kuma aba mai shuɗewa ta zo da ɗaukaka, ashe, abin da yake dawwammame, lalle ne yă kasance da ɗaukakar da ta fi haka nesa!
১১যস্মাদ্ যৎ লোপনীযং তদ্ যদি তেজোযুক্তং ভৱেৎ তৰ্হি যৎ চিৰস্থাযি তদ্ বহুতৰতেজোযুক্তমেৱ ভৱিষ্যতি|
12 Da yake muna da bege irin wannan, to, muna da ƙarfin zuciya sosai ke nan.
১২ঈদৃশীং প্ৰত্যাশাং লব্ধ্ৱা ৱযং মহতীং প্ৰগল্ভতাং প্ৰকাশযামঃ|
13 Mu ba kamar Musa ba ne, wanda ya rufe fuskarsa da lulluɓi, don kada Isra’ilawa su ga ƙarewar ɗaukakan nan mai shuɗewa.
১৩ইস্ৰাযেলীযলোকা যৎ তস্য লোপনীযস্য তেজসঃ শেষং ন ৱিলোকযেযুস্তদৰ্থং মূসা যাদৃগ্ আৱৰণেন স্ৱমুখম্ আচ্ছাদযৎ ৱযং তাদৃক্ ন কুৰ্ম্মঃ|
14 Amma aka sa hankulansu suka dushe, gama har yă zuwa yau akwai lulluɓin nan a duk sa’ad da ake karatun tsohon alkawari. Ba a kawar da shi ba, sai a cikin Kiristi ne kaɗai ake kawar da shi.
১৪তেষাং মনাংসি কঠিনীভূতানি যতস্তেষাং পঠনসমযে স পুৰাতনো নিযমস্তেনাৱৰণেনাদ্যাপি প্ৰচ্ছন্নস্তিষ্ঠতি|
15 Har yă zuwa yau, duk sa’ad da ake karatun littattafan Musa, lulluɓin nan yakan rufe zukatansu.
১৫তচ্চ ন দূৰীভৱতি যতঃ খ্ৰীষ্টেনৈৱ তৎ লুপ্যতে| মূসসঃ শাস্ত্ৰস্য পাঠসমযেঽদ্যাপি তেষাং মনাংসি তেনাৱৰণেন প্ৰচ্ছাদ্যন্তে|
16 Amma duk sa’ad da wani ya juyo ga Ubangiji, akan kawar da lulluɓin.
১৬কিন্তু প্ৰভুং প্ৰতি মনসি পৰাৱৃত্তে তদ্ আৱৰণং দূৰীকাৰিষ্যতে|
17 Ubangiji fa, shi ne Ruhu, kuma duk inda Ruhun Ubangiji yake, a nan’yanci yake.
১৭যঃ প্ৰভুঃ স এৱ স আত্মা যত্ৰ চ প্ৰভোৰাত্মা তত্ৰৈৱ মুক্তিঃ|
18 Mu da ba mu da lulluɓi a fuskokinmu duk muna nuna ɗaukakar Ubangiji, ana sauya mu mu ɗauki kamanninsa cikin ɗaukaka mai hauhawa. Ubangiji wanda yake ruhu kuwa shi ne mai zartar da haka.
১৮ৱযঞ্চ সৰ্ৱ্ৱেঽনাচ্ছাদিতেনাস্যেন প্ৰভোস্তেজসঃ প্ৰতিবিম্বং গৃহ্লন্ত আত্মস্ৱৰূপেণ প্ৰভুনা ৰূপান্তৰীকৃতা ৱৰ্দ্ধমানতেজোযুক্তাং তামেৱ প্ৰতিমূৰ্ত্তিং প্ৰাপ্নুমঃ|