< 2 Korintiyawa 1 >

1 Bulus, manzon Kiristi Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu, Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, tare da dukan tsarkaka a ko’ina a Akayya.
Paul, apostle of Jesus Christ by the will of God, and brother Timothy, to the church of God that is in Corinth, together with all the saints throughout Achaia:
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grace and peace to you from God our Father and Sovereign Jesus Christ.
3 Yabo ya tabbata ga Allah, da Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba mai tausayi, da kuma Allah na dukan ta’aziyya,
All praise to the God and Father of our Lord Jesus Christ, the Father of compassion and God of all encouragement,
4 wanda yakan yi mana ta’aziyya a cikin dukan wahalolinmu, domin mu kuma mu iya ta’azantar da waɗanda suke cikin kowace irin wahala, da ta’aziyyar da mu kanmu muka samu daga Allah.
who encourages us in all our affliction, so that we may be able to encourage those who are in whatever affliction, by means of the encouragement with which we ourselves are encouraged by God.
5 Gama kamar yadda wahalar Kiristi ta cika har tana zuba a cikin rayuwarmu, haka nan kuma ta wurin Kiristi ta’aziyyarmu ta cika har tana zuba.
Because just as the sufferings of the Christ flow over into us, so also our encouraging overflows, through Christ.
6 In muna shan wahala, ai, muna shanta domin ta’aziyyarku, da cetonku ne, in mun sami ta’aziyya, ai, mun same ta domin ta’aziyyarku ce, wadda take sa ku jure wa irin wahalan nan, da muke sha.
Now then, if we are afflicted, it is for the sake of your encouragement and deliverance, that are effective for enduring the same sufferings that we also are suffering
7 Begen da muke da shi dominku kuwa, tabbatacce ne, domin mun san cewa kamar yadda kuke tarayya da mu a cikin wahalolinmu, haka kuma kuke tarayya da mu a cikin ta’aziyyarmu.
(yes, our hope concerning you is steadfast); if we are encouraged, it also is for the sake of your encouragement and deliverance, since we know that you will share in the encouragement just as you do in the sufferings.
8 ’Yan’uwa, ba ma so ku zama da rashin sani, a kan wahalolin da muka sha a lardin Asiya. Mun sha wahaloli sosai, har abin ya fi ƙarfinmu, ya sa muka fid da tsammanin rayuwa.
And so, brothers, we do not want you to be in ignorance concerning the affliction that came upon us in Asia: we were under extreme pressure, beyond our strength, so that we despaired even of life.
9 Ba shakka, a zuciyarmu mun ji kamar hukuncin kisa ne aka yi mana. Wannan kuwa ya faru ne domin kada mu dogara da kanmu, sai dai ga Allah, wanda yake tā da matattu.
Yes, we ourselves have had the sentence of death within ourselves, so that we not place confidence in ourselves, but in the God who raises the dead;
10 Shi ya cece mu daga irin wannan hatsari na mutuwa, zai kuwa cece mu. A kansa muka kafa bege cewa zai ci gaba da cetonmu,
He did deliver us from that deadly peril, and still delivers; in whom we trust that He will keep on delivering,
11 yayinda kuke taimakonmu ta wurin addu’o’inku. Mutane da yawa kuwa za su yi godiya ta dalilinmu, saboda albarkar da aka yi mana, ta amsa addu’o’i masu yawa.
you also adding your cooperation in prayer, on our behalf; that thanks may be given by many persons for the gift bestowed on us by means of many, on your behalf.
12 Wannan shi ne taƙamarmu. Lamirinmu yana ba da shaida cewa mun yi zamanmu a duniya, musamman a dangantakarmu da ku cikin tsarki, tsakani da Allah. Mun yi haka ta wurin bishewar alherin Allah, ba bisa ga hikimar duniya ba.
Now this is our boast: the testimony of our conscience that we have conducted ourselves in the world with openness and godly sincerity, not by fleshly wisdom but by the grace of God, and especially toward you.
13 Gama ba mu rubuta muku abin da ba za ku iya karatu ko ku kāsa fahimta ba. Ina kuma fata cewa,
For we do not write you any other things than what you can read and understand; and I do hope that you will keep on understanding to the end
14 kamar yadda kuka ɗan fahimce mu, za ku kai ga cikakkiyar fahimta cewa za ku iya yin taƙama da mu, kamar yadda mu ma za mu yi taƙama da ku a ranar da Ubangiji Yesu zai dawo.
(as indeed some of you have acknowledged) that we are your boast, just as you are ours, in the day of the Lord Jesus.
15 Saboda na amince da haka, shi ya sa na so zuwa wurinku da fari, domin ku sami albarka riɓi biyu.
It was in this confidence that I was planning to come by you first,
16 Na yi shiri in ziyarce ku a kan hanyata zuwa Makidoniya, in kuma sāke dawo wurinku a kan hanyata daga Makidoniya, sa’an nan ku yi mini rakiya a hanyata zuwa Yahudiya.
and by you to proceed into Macedonia, and to come back to you from Macedonia (that you might benefit twice), and then to be sent by you on my way to Judea.
17 Kuna gani na yi wannan shirin ba da sanin abin da nake yi ba ne? Ko kuwa, kuna gani na yi shirin nan da halin mutuntaka ne, don in ce, “I” in koma in ce, “A’a”?
Now then, when I was deciding this, I was not acting frivolously, was I? Or the things I decide, do I decide according to the flesh, so that with me there would be both “Yes, yes” and “No, no”?
18 Kamar dai yadda ba shakka Allah yake mai aminci, haka ma maganar da muka yi muku, ba “I” da kuma “A’a” ba ce.
As God is faithful, our word to you was not “Yes” and “No”,
19 Gama Ɗan Allah, Yesu Kiristi, wanda ni da Sila da Timoti muka yi muku wa’azinsa, ai, ba “I” da “A’a” ba ne, amma a cikin Kiristi, “I” ne kullum.
because the Son of God, Jesus Christ, who was proclaimed among you by us—by me and Silvanus and Timothy—was not “Yes” and “No”. In fact, with Him it has always been “Yes”,
20 Domin dukan alkawaran Allah cikarsu a gare shi suke, ta wurinsa ne kuma muke faɗar “Amin”, domin a ɗaukaka Allah.
because all the promises of God in Him are “Yes”; indeed, in Him they are “Amen”, that there be glory to God through us.
21 Allah ne fa yake sa mu da ku mu tsaya daram cikin Kiristi. Shi ne ya shafe mu,
Now He who establishes us together with you into Christ, and who anointed us, is God,
22 ya buga mana hatiminsa a kan mu nasa ne, ya kuma sa mana Ruhunsa a cikin zukatanmu, domin yă tabbatar da abin da yake zuwa nan gaba.
who also sealed us and gave us the down payment of the Spirit in our hearts.
23 Labudda, Allah shi ne shaidata cewa don kada in ƙara muku wahala ne ya sa ban koma Korint ba.
For my part, I call on God as witness, upon my soul, that it was to spare you that I have not yet returned to Corinth.
24 Ba nuna muku iko a kan bangaskiyarku muke yi ba, sai dai muna aiki tare da ku ne saboda farin cikinku, domin bisa ga bangaskiya ce kuke tsaye da ƙarfi.
(Not that we have control over your faith, but we work with you for your joy, for it is by faith that you stand firm.)

< 2 Korintiyawa 1 >